Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

saita tsorata ta dawo baya gidan Iklima, a gurguje dai nan suka had'e suka fara wannan rayuwa ta k'ask'anci, kamar yanda Mari tace ita k'aramar karuwa ce, domin kuwa duk kud'in da zata samu basa wuce na yan buk'atu abin ci abin sha yar sutura marar tsada, ciki kuma na girma tana rainonshi tare da tunanin irin tarbiyar da zata bawa wannan cikin idan ya fito, saida cikinta ya tsufa ta daina fita sai Iklima kad'ai, a wannan lokacin sai take jin Iklima kamar yer uwa da suka fito ciki d'aya, tana haihuwa ma Iklima ce tsaye kan komai kamar ita akawa haihuwar, har akayi suna sai dai *Nurul Huda* bata samun gatan da aka yanka mata rago ba har yau maganar da ake tana shekara shida da haihuwa, bayan haihuwarta tayi arba'in suka ci gaba daga inda suka tsaya, bata sake waiwayar gida ba bare tasan meke faruwa, sai dai tana had'uwa da yayan Khadi a cikin gari har ma su gaisa, lokacin da suka samu kud'i ne sai suka kama gidan hanya wanda duk matan aure ne a gidan, mace d'aya suke abin arzik'i da ita maman Husna, ita ma bata nuna musu tsana ko kyara shiyasa, ana haka Junaid ya ganta wajen bikin wani abokinshi sunje d'aukar abinci gidansu k'awar amaryar wacce ita ta asassa taron suna tsakiyar fili suna rawa, ita ba abokiyar ango bace bare kuma amarya, kawai mawak'in ne mutuminsu shine ya gayyace su kuma suka je, dama kuma in zasuje irin wannan shiri ake na musamman, dan ko rigar nono basa sakawa bare wando saboda ana so komai yasan an motsa shi, haka kawai yarinyar ta mishi yaji ta birge shi, ya kasa gajiya da kallonta, daga ranar ne fa yake bibiyar rayuwarta kuma har yanzu bai daina ba duk da yasan wacece ita, tak'aitaccen labarin Maryama kenan.

*Ci gaban labari*

Ya jinjina sosai da jin labarin, shirun da yayi yana tunani barkatai yasa Iklima mik'ewa tace "Na tafi ni saida safe."
Bai iya kallonta ba har ta wuce, da k'yar shima ya tashi ya shiga motarshi sai dai babu kuzari a tare da shi, gida ya nufa cike da k'warin gwiwar jin wani hukunci daya yanke yana daf da isa gidan.

➡️➡️➡️➡️➡️➡️➡️

Tun yamma Hamna ke son amsar wayarta a hannun Ammar amma ta rasa yanda zatayi, har saida akayi sallah isha'i sannan ta shirya cikin shiga irin ta Amna sak ta nufi b'angaren na samari, tana isa bakin k'ofar ta tsaya tana k'wank'wasawa tare da yin sallama, Ammar da ke zaune falo shi kad'ai yana latsa wayarshi sai wayar Hamna aje gefenshi, a hankali ya d'ago kai ya sauke kan k'ofar, take kuma ya mayar da kallonshi kan wayarshi duk da dai muryar da Hamna keyi tayi sak data Amna, saida ya d'auki kusan minti biyar bai sake d'agowa ba kafin yace "Shigo." A hakan ma ba tare daya kalli k'ofar ba.

Cikin nutsuwa kamar yanda tasan yer uwarta nayi ta shigo tana sake wata sallamar, bai amsa ba bai kuma kalleta ba har ta tsaya tsakiyar falon, a sanin data mishi yasa bata tsaya b'ata lokaci ba ta fara bayani kamar haka "Yaya Ammar, dama zan kira Mamanmu ne a wayar Hamna saboda tawa babu kati a ciki, sai tace wayar tana hannunka kuma kaga idan akayi sallah isha'i ba'a barinmu fita ko yara bare..."

Wannan bayani da take jin shi yake kamar saukan ruwan sama da k'ank'ara a tsakiyar kanshi, k'aguwa tasa ya d'auko wayar dan dama ta ishe shi saboda wayan kiran da ake ya mik'o mata, hannu ta zuro ta karb'a tace "Nagode."

Sai lokacin kad'ai idonshi suka kalli na ta idon, gabanshi ne yaji ya fad'i da sauri ya d'auke idonshi daga kanta, juyawa tayi zata fita a lokacin kuma Jibril ya shigo falon da kular abinci a hannunshi, saida ta kusa kaiwa k'ofa ta juyo ta kece da dariya tace "Allah sarki boss, a hakane kake cewa kana son zama soja bayan baka iya gane waye wannan waye wannan, to kai fa ina ganin ko namiji ya zo maka a shigar mace saika yarda."

Tunda ta fara magana yake hasosho irin muguntar da zai mata, hakan yasa shi kallon Jibril da suka fi kusa cikin kaushin murya yace "Wallahi kai zai ci wa uwa idan har baka rik'e min ita ba."

Tsuru Jibril yayi ya juya ya kalli Hamna data tattare zanin atamfarta, to shi taya ma zai fara rik'e ta ne? Juyowa yayi ya kalli Ammar daya had'e fuskar nan kamar hadarin gabas, sai kawai ya juya da sauri ya nufi k'ofa, Hamna na ganin haka ta rufa a guje da tunanin ita zai kama, shi kuma yasan sai Ammar ya cuce shi, tunda kuma ba zai iya kamota ba gwara ya bar masa gidan, da kallo duka ya bisu kafin yayi k'wafa yace " *Kankana* kenan, zaki shigo hannu na ne, zaki gane shayi ruwa ne."Jibril kam k'ofar gidan ya zauna a teburin mai gadi yana cin abincin suna 'yar hira.

Iyayen na zaune a falo suna hira k'asa kasa saboda Hajia na d'aki kar a dameta, wayar Zeinabu ce tayi k'ara tana neman agaji, d'auka tayi ta duba mai kiran hakan yasa gabanta tsinkewa ya fad'i, datse kiran tayi kafin ta mik'e tace tana zuwa ta shiga d'akin ta, maida kiran tayi da sauri kuwa aka d'auka ana fad'in "Eh lallai Zeinabu kin cika 'yar halak, yanzu har ni zan dinga kiranki amma kina kashewa? To yayi kyau, ni dama ba wani abu yasa na kiraki ba na kira ne inji ya ake ciki? Wata kusan biyu kenan ba sak'onki bana mijinki, shine nake so naji ina aka kwana?"

Har yanzu gabanta bai bar fad'uwa ba a haka ta amsa mata murya k'asa k'asa da " *Inna* Dan Allah kiyi hak'uri, wallahi bana shareki bane, abubuwa ne suka min yawa, colonel kuma nasan ba wai bai nemeki bane aiki ne dai yasha kanshi, amma kiyi hak'uri insha Allahu gobe zan aika miki da kud'in wata d'aya kafin colonel ya dawo."

Da k'arfi tsohuwar tace "Duba Zeinabu, kinfi kowa sanin bana son ana min wasa da maganar kud'i, ki tabbatar gobe kin aiko min kud'in da zanyi cefanai dasu dan kayan abinci na sun k'are, sannan ba zan iya tsayawa jiran mijinki ba, ki kirashi a waya ki fad'a masa ya aiko min da sak'on kamar yanda mukayi yarjejeniya da ku, idan kuma ba haka ba wallahi wallahi *asiri zai tonu*, ehe!"

Da sauri tace "A'a Inna ba sai anyi haka ba, insha Allahu zan tura miki nawa sak'on gobe nan, yanzu ma dan dare yayi ne, colonel kuma zan kirashi yanzu na tuna mishi dan nasan sha'afa yayi."

Cike da gadara tsohuwar tace "To, kashe waya."

Cikin sanyin jiki Zeinabu ta datse kiran ta sake kiran lambar colonel, yana ganin lambar ta yayi murmushin da ba kowa zai iya gane murmushi yayi ba ya d'auka, cikin wani irin amon murya da ba zaka fahimci yanayin da mai ita ke ciki ba yace "Ai na d'auka ba zaki kirani ba, ashe dai ina da rana ta."

"Ni ba abinda yasa na kiraka kenan ba, na kira ne na fad'a maka Inna ta kirani yanzu, bansan dalilin daya hanaka cika alk'awarin daka d'auka ba a wannan watan da har ta kira ni take k'ok'arin tayar min da hankali."

Daga b'angaren shi ya amsa da "Kin kira ne kenan dan ki min fad'a ko me? Saboda ke ce uwata zaki tsareni kina fad'a min maganar nan."

Ita ma a hassale tace "Amma ai kasan kai ka d'auki alk'awari ko? Dan haka dole ka cika."

"Idan na k'i fa? Dukana zakiyi? Wai ko dan kinga bana kusanki ne zaki nemi ki min iskanci?"

Murmushi tayi kamar a gabanshi tace "Ba ma zaka yarda ba wallahi, tunda ka fara dole ka kai k'arshe tunda laifinka ne koma menene."

Wai, colonel Hussein da yake ji kamar ya ganta gabanshi ne ya harzuk'o yace "Laifi na? Laifi na ma kike cewa? A waccen ranar ni nace kiyi abinda zai tayar min da hankali? Ko kuma tursasaki nayi? Ba da amincewarki komai ya faru ba?"

K'asa tayi da ta ta muryar tace "Duk da ba tursasani kayi ba ai ba kana nemana na amince maka ba, sannan bani na ce ka kirani inda kake ba, da kuma na zo kaga zan tayar maka da hankali me ya sa ba kayi gaggawar korata daga wajenka ba?"

D'orawa tayi da "Duk kai ka ja mana wallahi, ba dan kasa tsoron Hajia a ranka ba da yanzu muna rayuwa cikin salama, amma tsoron wanda baida wutar da zai samu ya saka mu sai aikata laifi muke akan wani laifin."

Rintse ido tayi saboda jin k'arar ya bugi wani abu da yake nuna mata da ita ce a kusa da ita ya kaiwa wannan haura, datse hak'oran shi yayi ya rasa bakin magana, ina ma zai ji an kawo masa hari ta baya ko ya samu damar huce wannan haushin, jin baiyi magana yasa tace "Ni duk ba wannan ba, kayi azamar turawa Inna kud'in ta kamar yanda kukayi da ita, dan ni dai ba zan so asiri na dana yarona ya tonu ba a wannan lokacin, gaskiyar magana kenan."

"Kutumar bala'i." Inji colonel a cikin zuciyarshi dan har yanzu ya kasa sakin hak'oran shi, "Wannan ma ai raini ne, Zeinabu umarni ne take bani ko me? Ni? Ni? Ina!" Buga wayar yayi a bango ta baje tare da kai wa bangon naushi, Zeinabu dai ta fad'i abinda ke ranta ta kashe waya ta dawo falo.

Jibril ne a d'akin kakarshi bayan ya gama cin abinci suna hira, kallonta yayi da fara'a a fuskarshi yace "Yar tsohuwa, insha Allahu idan aure na da Amna ya tashi da kaina zan tuk'aki ki kaini wajen dangi Baba, dan wallahi ina so na gansu sosai."

Tunda yayi maganar nan ta had'e fuska tayi shiru, jin shirun yasa yace "Hajia, wai a wane gari dangin mahaifin Baba suke? Na gaji da tambayar Umma akan wannan."

Ba alamar wasa ta kalleshi tace "Kenan ni ce yanzu zaka dama? Malam tashi ka fitar min daga d'aki."

Da mamaki ya kalleta yace "Hajia, kema damuwar ce kamar yanda Umma ke damuwa a duk sanda na mata magana makamanciyar wannan?"

Cikin d'aga murya tace "Ban sani ba Jibril, kuma in har baka son gayyato fushina to kayi gaggawar janye wannan k'udirin naka na son ganin dangin mahaifin mahaifinka."

Mik'ewa yayi da tsantsar mamaki yace "Saboda me? Meyasa Hajia baku so ana..."

"Na ce ka fita." Ta fad'a da k'arfin gaske, juyawa yayi jiki a sanyaye ya fita yana tunanin meke faruwa, fitowa yayi k'ofar gidan da tunanin shiga motarshi daya bari anan, Junaid ya had'u da shi zai shigo hakan yasa ya tsaya ya fito suka gaisa, Jibril ne yace "Na ga yau sai wani farin ciki kake mutumina, ko dai Maryama ta amince ne?"

Wani murmushin ya sake yi yace "Bata amince ba, amma dai na gano hanyar da zanbi nasa ta amince."

"Wace hanya kenan?" Ya tambaya da zumud'i, da murmushin gefen labb'a yace " *Zan je garinsu, sannan na shirya tsakaninta da mahaifiyarta da sauran danginta."*

Da fara'a Jibril yace "Eh to kuma fa ka zo da dubara, kana shirya tsakaninsu zaka ga ta amince kosu su amince da kai."

Kallonshi yayi yace "Amma dai zaku rakani ko?"

Zaro ido yayi yace " Ni da wa?"

Hararanshi yayi yace "Kai da zaratan 'yan uwa na mana."

"Har da Ammar?" Cewar Jibril, ba wasa yace "Har da shi mana, ai watak'ila ma ya mana anfani fiye da kai, dan in mukayi sa'a muka had'u da wani tsagera a cikin dangin mai taurin kai shi zai mana maganinshi."

Juyawa Jibril yayi zai nufi motarshi yana fad'in "Shikenan to sai kuje babu ni."

Da sauri ya rik'o shi yana dariya yace "Kai haba daga wasa, kai fa zaka nuna mana hanyar ma tunda ai kasan hanyar *Gouré*."

Cak ya tsaya ya juyo yana kallon Junaid, Goure, wannan yarinyar? Tana nan har yanzu? A ina take? Ina zanje na sameta? Rik'e hannun Junaid yayi yace "Da gaske kake? Yaushe zamu tafi?"

"Eh to, ni ko gobe ma zan iya tafiya, amma ka bari mu fara jin ta bakin su Ammar da Amar."

Hannunshi ya kama zuwa cikin gidan yana fad'in "Muje ciki muyi magana da Ammar yana nan, Amar idan ya shigo zamu fad'a mishi kuma kasan ba matsala zai bamu ba."

Wucewa sukayi ciki Junaid na fad'in "Wai duk wannan saurin na miye haka? Kamar wanda zaije ganin tashi budurwar."

Wani murmushi Jibril yayi, dan haka kawai ya ji kamar ana fizgarshi da yaje garin, yana so ya Allah ya sake had'a shi da yarinyar nan, suna zuwa suka saka Ammar tsakiyarsu Junaid ne yace "Babban yayanmu, dama wata alfarma muka zo nema, dama yarinyar nan da nake so ce ta fad'a min garinsu, to akwai yar matsala tsakaninta da iyayenta, shine nayi shirin tafiya neman aurenta wajensu tare da shirya tsakaninsu, to bana so ne naje ni kad'ai gaskiya, nafi so muje tare da ku dan su san ni d'an dangi ne."

Ammar da hankalinshi ke kan waya saida yaji ya kai aya kamar mai ciwon haure yace "Ina da abinyi."

Yana fad'a kuma ya mik'e ya shiga d'akin shi, Junaid ma ya mik'e yana tab'e baki sai ga Amar ya shigo, nan suka fad'a mishi kuma kamar yanda suka sani dama ba zai basu matsala ba, shirya yanda tafiyar zata kasance sukayi kafin kowa ya nufi d'akin shi.

*Zanyi magana, amma ba yanzu ba.*
03/06/2020 à 23:33 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨
*SANIN MASOYI*
_(sai Allah)_
*BAYA DA K'URA*
👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨

*NA*

_SAMIRA HAROUNA_

*Litattafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._

*SADAUKARWA GA*

💞 _*MASOYA NA*_💕


_Bismillahir rahamanir rahim_

🇳🇪 *TAURARIN NIGER*
```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)```

_6_


Ma'arufa ce da Ma'aruf a d'aki kowa da wayarshi yana dannawa, kwance take akan katifa mai tufun gaske shi kuma tashi katifar bata da maraba da bargo, kallonta yayi yace "Ke wai kin fara shirin tafiyar ne gobe ko kuma kina nan kina jan jikin?"

Ba tare data kalleshi ba tace "Ba gobe zan tafi ba."

Ba tare daya daina kallonta ba yace "Saboda me?"

Kai tsaye tace "Saboda akwai wasu kud'i da Labo zai bani gobe idan ya zo, kuma ina so na shiga kasuwa na siyo sabbin yadin da za'a min sabbin riguna dogaye, tunda waccen gurguwar tace mutumin ba wai harkar matan banza yake ba."

Tsaki yayi yace "Ke dan Allah kiyi duk iskancin da zakiyi zuwa jibi ki bar garin nan, na k'osa kud'in nan si shigo wallahi harka ta bud'e, dubi shegiyar katifar da nake kwana akai."

Sai lokacin ta kalleshi tace "Wai kai yanzu ko kunya baka ji? Kana kwance gida ni ce zanje na nemo maka kud'in da zaka ji dad'in rayuwarka da su."

Ba tare da damuwa ba yace "To meye a ciki? Ke ma sau nawa ina miki anfani? Yanzu lokacinki ne yayi."

Tsaki taja ta mayar da kallonta kan wayarta tace "K'aton banza kawai."

Kallonta yayi amma bai biye mata ba saboda yana wata hira data d'auke mishi hankali, wata budurwarshi ce mai sunan *Meena* ke ikrarin daina harka dashi tunda baya sonta baya kashe mata kud'i, maida mata sak'on yayi da "Rabuwa dani a daidai wannan gab'ar na nufin ke asararriya ce."

Maido masa tayi da "Sai dai in kaine asararren, shege d'an iska wace tsiyar kake tsinana min?"

Shima mayar mata yayi da "Ke haba matsalata dake banza ce, kanki baya kawo wuta ko kad'an, ina nufin idan kika barni a wannan lokacin to zakiyi asarar wata opportunity da muka samu."

"Ban gane ba d'an rainin hankali, fahimtar dani?"

Nan ya fad'a mata wai sun samu wani Alhaji gara zasu wanke shi, kuma k'ashin bayan tafiyar abokiyarshi ce Ma'arufa, dan haka karta bari damar nan ta wuce ta, nan dai suka sulhunta komai ya wuce.

♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡

Yanda Abbas yayi tunanin aikin zai kaishi kwana uku sai ya zo da sauk'i, dan haka ya shirya ya taho ba tare daya fad'awa madame ba, su a lokacinsu dare ne dan har sun shiga bacci, saida ya fara shiga wajensu Ammie da suma har sun kwanta ya gaishe su, daga nan kuma part d'in shi ya wuce ya aje jakarshi yayi wanka, kayan bacci ya saka ya feshe jikinshi da turare mai sanyin gaske kafin ya d'auki makullin k'ofar da zata sada shi da falon Sameera ba sai ya fito ta farfajiyar gidan ba, yana shiga ya tabbatar sun jima da kwantawa, d'akin Raihan ya fara bud'a k'ofar a hankali ya lek'a, saida ya sauke ajiyar zuciya sabida ganin tana bacci hankali kwance, duk da har yanzu bai siya mata waya ba amma dai yana tsoron sharrin zamani da dubarar 'ya'yan yanzu, rufewa yayi ya lek'a d'akin Rauda, Khalifa da sauran yaran, amma yana ganin Abdul raheem shi kad'ai kwance a gadonshi babu Ameer ya tabbatar yana wurin mamanshi, a hankali ya shiga can cak ya tsaya, rarraba ido yakeyi tare da shafar kai, a hankali ya fara takowa har ya zo kusa da ita ya tsaya, jefar da makullayen yayi kan gado ya bud'e mata hannayenshi yace "Come on my angel, i miss u."

Sameera da tunda mota ta shigo gidan ta farka a hankali cikin turo baki ta bud'e hannayenta ta kwanta luf a k'irjin shi, lumshe ido yayi ya sauke wata ajiyar zuciya mai d'an k'arfi wacce iska da gumin bakinshi har suka sauka kan fuskarta, k'ara shiga jikinshi tayi tana sake matseshi sosai saboda k'aunar mijin nata, ido rufe take sauke ajiyar zuciya tana shak'ar turarenshi dake son mayar da ita bacci, cikin muryar shagwab'a tace "Me yasa baka fad'a min zaka zo ba?"

Saida ya fara yawo da hannayenshi a gadon bayanta yana latsawa saboda taushi da laushi ba tare daya bud'a ido ba yace "I'm sorry, nima bansan aikin zai sakeni yau ba, ina k'arasawa kuma naji ba zan iya kwana nesa da ke ba, shiyasa na garzayo na zo gareki."

K'ara daidaita zamanta tayi cikin k'irjinshi shi kuma yana sake matseta yana shafata, cikin wata murya mai kama data bacci yace "Meerata."

"Uhmmm." Ta fad'a ba tare data kalleshi ba, d'orawa yayi da "Zan samu kulawarki a wannan daren kuwa? Naga baba na yayi kane-kane a kan gadon."

D'agowa tayi ta kalleshi ta juya ta kalli Ameer dake ta baccinshi, sake kallonshi tayi tace "Ka d'auke shi mana saika kaishi d'akin su."

Kallon Ameer yayi shi ma ya zagaya zai d'auke shi yace "Allah kasa kar yaron nan ya hanani sakewa."

Murmushi tayi wanda harya fitar da sauti, kallonta yayi yace "Wallahi yaron nan rigimarki ce ya koya, ko da yana jariri bai hanani yin rayuwa da ke ba kamar yanda yanzun yake hana ni."

Zaune tayi bakin gadon tace "Watak'ila yana tsanani buk'atar a kasance auta ne shiyasa, yasan idan ya baka fili saika masa k'ane."

Harara ya cillo mata yace "Idan na tashi yi a hanani na gani, kinsan dai ko gabanshi na so zanyi yanda nake so ko?"

Dariya tayi tace "To ka barshi yanzu saimu jaraba mu gani."

A lokacin daya d'auki Ameer ne yace "Bana so na jefo shi k'asa ai."

K'arar bud'a k'ofa yasa Ameer bud'a ido tare da zabura ya kalli wanda ya d'auke shi dan ya hango mamanshi zaune, rintse ido Abbas yayi wanda yasa Ameer cikin muryar bacci cewa "Yeee! Dady na ganka bud'e idon."

Kafin ya bud'e idon ido ya sake cewa "Dady yaushe ka dawo? Ka kawo min computer ta?"

D'ago shi yayi suka kalli juna yace "Muje na kaika d'akinka ka kwanta da safe zan nuna maka wacce na siyo maka, ko Khalifa baya da irinta."

Ai sai Ameer ya dirko daga kafad'ar Abbas yace "Um um Dady, ni tare da Ammie na zan kwana, abinda ma tunda ka tafi tare muke kwana, kai kaje d'akin ka."

Da gudu ya yo kan Sameera ya kwanta kan cinyoyinta yana kallon Abbas, ganin yana nufoshi yana fad'in "In dai kana son na baka computer sai ka zo mun tafi, idan ba haka ba kuma sai dai na bawa *Amjad* (d'an Naseer) ita."

Zagaya hannayenshi yayi ta kunkumin Sameera ya mak'aleta sosai yace "Um um, bana so ni dai."

Dariya Sameera tayi rumgume shi tace "Babana kenan, yaro kwana a gado d'aya tare da mahaifiyarshi yafi mishi komai na duniya ko?"

"Eh Ammie." Kwance Abbas yayi kan gadon dan ko yace ya zare mishi ido kuka ne zai saka musu a daren nan, kallonshi yayi yace "Zo nan baba na nayi kewarka sosai."

Rarrafawa yayi ya kwanta kan k'irjin shi ya rumgume shi, Sameera ma kwance tayi ta d'ora kanta a kafad'ar shi tace "Ka ci abinci kuwa?"

Ido lumshe yace "Um." Tsautsayi yasa Sameera cewa "Auta na kayi abinci kaji, kasan..."

Wata k'ara ta saki saboda mintsinin da Abbas ya mata a mazaunai, zaune ta tashi idonta har sun fara ja saboda zafi, kallonshi tayi shi kuma ba tare daya kalleta ba yace "Gobe ma na sake jin kin kira shi auta kiga yanda zanyi da ke."

Kamar zata fashe da kuka tace "To meye a ciki dan na kira shi da auta dan Allah?"

Ido rufe kamar wanda zaiyi bacci yana ci gaba da shafa bayan Ameer yace "Saboda yawon kiran na shi da auta zaisa wata rana ki fad'a lokacin amsar addu'a, ni kuma so nake sai kin dire min sha biyu insha Allahu." Shiru ta mishi ta kwanta, gashinta yake shafawa da d'aya hannun a haka har bacci ya d'auke su.

*BASRABA*

Tunda garin Allah ya waye Takawa yake jin kamar ba shi ba, a haka har akayi sallah la'asar ya dawo b'angaren shi kan kilisarshi ya kishigid'a, haka kawai yaji yana buk'atar ganin liman, dan haka yasa d'aya daga cikin masu tsaron k'ofar shi ya nemo mishi liman, kusan dama unguwar duk duk fadawan fada ne a ciki, dan haka ba jimawa sai gashi ya dawo tare da liman, jakadiyar uwar d'aki na ganin haka ta garzaya ta fad'awa uwar d'aki, cikin tashin hankali tace "Kin tabbatar liman ne ya shiga wajenshi?"

Cikin girmamawa tace "Ko zanyi k'arya uwar d'aki harshena yayi kad'an daya furta miki k'arya, yanda na ga liman tare da bafaden nan ina fatan ganin annabi haka."

Wata ajiyar zuciya ta sauke marar dad'in sauti tace "Tashi kije, amma kar kiyi nisa dan zan buk'ace ki."

Tashi tayi ta fita ita kuma ta d'auki waya ta kira waziri, yana danna ok ya sake danna wurin nad'ar duk maganar da zasuyi kafin yayi magana, cikin tashin hankali tace "Waziri ka ce na bar komai a hannunka, amma gashi kana neman ka mana kwance da aiki, ko kasan cewa takawa ya nemi ganin liman? Yanzu haka suka turakarshi."

"What!" Cewar waziri, sausauta murya yayi yace "Ki gafarce ni uwar d'aki, yau ba sai gobe ba zan miki maganin matsalar nan."

"Ka tabbatar?"

"Na baki tabbacin haka." D'if ta kashe wayar, sai lokacin kuma ta tambayi kanta "Amma me yasa baki tambayeshi meye zaiyi ba?"

Shiru tayi tana tunani kafin daga bisani ta d'aga kafad'a irin bai dameta ba tare da cewa "Koma me zaiyi indai zaisa a fasa auren kuma naga yarinyar can Ameera cikin garari to hakan ya isheni."

A wajen takawa da liman kuma sun jima suna tattaunawa kafin ya mishi maganar neman auren Safiyya, nan liman ya nuna mishi ba komai ya kuma gamsu da bayanan takawa, amma duk da haka saida yace idan har akwai matsala to gwara abar maganar, takawa ya nuna mishi babu komai kawai suyi musu fatan alkairi, da haka takawa ya nemi alfarmar a d'aura auren nan kusa, amma liman yace a bashi lokaci dan sanar da mahaifiyar yarinyar da ita yarinyar kanta, cikin mutumta juna suka gama tattaunawarsu liman ya bar takawa lafiya.

Bayan tafiyar liman haka kawai takawa ya nemi ganin duka iyalin na shi a turakarshi, nan suka hallara uwaye da 'ya'ya maza da mata, nasiha ya dinga musu da gargad'i da jan kunne akan rayuwa, daga bisani ya musu addu'a tare da jadadda musu rik'o da zumunci, kar su yarda su bari mulki ko
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment