Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

Ya fad'a yana nuna mishi biyu da yatsunshi ya ci gaba da cewa "A lokaci d'aya, kuma kuma ku kuna baccin iya shege."

Juyawa yayi cikin takon k'arfi kamar zai shiga filin daga ya shiga falon Hajia, saida ya tsaya tsakiyar falon ya fara bubbuga bokitin yana ihu yana fad'in "Kowa ya fito, kowa ya tashi."

Har sama ya haura k'ofar kowane d'aki ya bubbuga yana shelar kowa ya fito, har yara masu nauyin bacci saida suka fito haka Zeinabu da Hamna take hangenshi daga sama, Kamal ne ya iya jarumtar cewa "Yah Ammar lafiya ka tashemu a bacci?"

Kallon duka yaran yayi yace "Kowa ya sauko k'asa."

Cikin turo baki da girmama jarabarshi kowa ya sauko rai a b'ace, kamar zai basu horan yak'i haka suke jera suna kallonshi, kallonsu shima yake yace "So nake ku fita farfajiyar gida kuyi murna kuyi tsalle kuyi ihu da hauka saboda murnar samun 'yan biyu da nayi, yan biyun ma ni duka jinsin aka had'a aka ban, dan haka ina so duk unguwar nan ta shaida anyi sabon *Ammar* da kuma k'anwarsa *Amna*."

Yanda ya fad'a haka suka fita duk sukayi inda suka ga su Hajia, d'aga kai yayi suka had'a ido, girgiza kai tayi a ranta tace "Allah ya shiryaka Ammar."

A zahiri kuma ce masa tayi "Saboda wannan ne ka d'aga mana hankali? Allah ya baka lafiya to."

Sake d'aga kai yayi yace "Ki sauko kema ko kuma na sauko dake yar bak'in ciki, hassada kike min na samu 'ya'ya biyu a lokaci d'aya."

Wani murmushi ta masa tace "Biyu ko uku?"

Dara daran idonshi ya sake kafewa kanta da mamaki yace "...

*Alhamdulillah*

*Wallahi rashin comment yasa duk rubutun ya fice min a rain, ba zan dakatar da rubutun ba amma zan iya daina turawa ko ina, idan kun canza na samu gamsuwa zaku ga wata page gobe insha Allah ba ma sai kun tambaya ba.*

_A kafta, yawan sharhi yawan rubutu._
14/10/2020 ร  00:58 - Ummulkhairi: ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ
*BADAK'ALA*
๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ

*Labarin Gaske*

*NA*

_SAMIRA HAROUNA_

*Litattafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._

*SADAUKARWA GA*

๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ _*AHALI NA*_๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

๐Ÿ’ซโœจ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*๐ŸŒŸ
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_๐Ÿค

โ˜† *[ T.M.N.A]* โ˜† ๐Ÿ“–๐Ÿ–Š๏ธ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_

_52_


"Yan uku kankana?"

Yawu ta had'e duk tayi alamar rashin gaskiya, ganin bai daina kallonta ba yasa ta juya zata koma d'akinta taji yace "Har d'akin zan sameki wallahi idan baki sauko ba."

Juyowa tayi ta kalleshi, yamutsa fuska tayi ita kam ba zata iya wannan tozarcin ba, hararanshi tayi tace "Hijabi zan d'auko to, saboda gidan nan ba tsaro gareshi ba, ta ko ina kuraye ke akwai ko ganye suka gani kallon nama suke mishi."

Da kallo kawai ya bita har ta fito, kallon saukowarta yake da dogon wando sai hijab daya rufe iya cinyarta, saita ta kawo daf da shi suka jera zasu fita yace "Duk kurar da take ma ganye kallon nama lallai lafiyayya ce, shiyasa fa har yanzu nake mamakin yanda akayi baki karb'i sak'on dana tura miki ba bayan kuma ina da tabbaci akan d'an aike na."

Hararanshi tayi ta murgud'a baki tace "Ta Allah ba taka ba, burinka kenan a kaina kuma ba zai cika ba."

Suna zuwa Ummy ta fito ta kalleshi tace "Malam muje dan Allah ka kaimu asibiti idan ka gama shiriritar."

Turo baki yayi gaba ya kalli mutanen dake wurin yace "Yanzu jama'a ba zan iya samun wanda zai kira ni ya danganta yaran nan dani ba?"

Alhaji ne yace "To uban..." Kallon yaran yayi yace "Da fari fad'a mana sunansu? Ko kuma ka bamu zab'i ne?" Da k'arfi tace "A'a Alhaji, haba dai kura da shan bugu gardi da kwashe kud'i, ai yanda nake ubansu haka zan saka musu suna."

Hamna ce ta kalli Ummy tace "Ummy ina Amna?"

Nuna mata d'akin tayi tace "Tana ciki." D'akin ta shiga dan ganin yar uwarta, shi kum saida ya gyara tsayuwa sannan yace "Namijin sunan *Ammar*, macen kuma domin nuna farin cikina ga uwarsu na mata takwara, dan haka ita ta ci *Amna*."

Kallon kallo aka shiga yi harda yaran, lieutenant ne yace "Meye na mayar musu da sunanku to kamar suna ya k'are?"

Murmushi yayi yace "Abba ai duka sunaye ne masu kyau, ina so jarumi na ya zama namiji marar tsoro da fargaba, ya zama babu shakka babu d'aga k'afa kuma zai iya fad'a ko a gaban waye, sannan ya zama wanda baya d'aukar raini, jarumata kuma zan so ta zamar ruwa masu aiki sannu kamar mahaifiyarta, hakan zaisa kowa ya so ta."

Lieutenant ne yace "Idan na fahimce ka kana so ka saka mishi sunanka saboda kana so yayi komai naka ko?"

"Eh Abba." Ya fad'a cike da kuri, jinjina kai yayi yace "Har da fitsarar da rashin ta idon ma?"

Kwab'e fuska yayi alamar shagwab'a yace "Abba ni ne marar kunyar?"

Murmushi lieutenant ya masa yace "A'a d'an albarka."

Husseina ce tace "To wai akan me sai sunayenku za'a mayar ma da yaren kamar wad'anda suka mutu?"

Alhaji ne yace "Dan Allah ku barshi tunda haka yake so ai ya hallata, kawai mu dai ya fad'a mana wani sunan ko da alkunya ce da zamu dinga kiransu dashi, d'an ba zamu kiraku da sunanku ba kuma suma mu kirasu da sunanku."

Girgiza kai Hajia tayi ta kalleshi tace " *Shalele* na, fad'a mana alkunyarsu ko kuma na saka musu da kaina."

Kallon kallo aka shiga yi Hajia ta kirashi shalelenta, basarwa kawai tayi shi kuma saida yayi tsayuwar tata rashin mutumci yace "Eh to shi jarumin Ammar d'in zaku iya mishi lak'abi da *Abu Ahmad*, sunan da zai sawa d'anshi kenan insha Allah, jatumar tawa kuma saiku mata lak'abi da *Ummu Aysha*, idan kuma alkunyarsu kuke so saiku kirasu da *Ameer* *Ameera*, idan kuma a sauk'ak'e kuke so saiku ce *A.A*, ita ma kuma saiku ce mata *A.A*."

.Cike da k'aguwa Ummy tace "Ba zan iya sauraren wannan shirmen ba, yarinyar can asibiti take buk'ata a bata kulawar data dace, amma kun tsaya kuna maganar sunan yara tun yanzu."

Juyawa tayi cikin jin haushi ta shiga ciki, Hamna ta samu rik'e da hannun Amna cikin sanyin murya take fad'in "Yer uwa wallahi ban tab'a tsammanin haka haihuwa take ba, ta zo min da sauk'i fiye da tunaninki, sannan yah Ammar ya tsaya kaina har na haihu, gaskiya naji dad'in kulawarsa a kaina."

Murmushi Hamna ta mata tace "Yanzu ma gashi can sai hauka yake mana a gida wai shi yayi yara, ya hana kowa bacci fa."

Murmushi tayi tace "Ba hauka bane yer uwa, farin ciki yake ya d'ora idonshi akan 'ya'yansa."

Kamata Ummy tayi tana fad'in "A ganinki haka murna ce? Wannan ai hauka ne da shirme, kanshi aka fara haihuwa?"

"Ummy a gareshi shine na farko." Cewar Amna, da sauri Ummy ta kalli Hamna ita ma kuma ita ta kalla, kamata sukayi ta tashi Ummy ta mata durwa (k'unzugu) sannan suka fito, sun same su tsaye sai zuba musu haukan ko yake ta bakinsu, sunaye kawai yake zana musu idan basu iya fad'in wannan su fad'i waccen, rankaya sukayi zasu fita ya kalli Hamna ya cilla mata makulin mota yace " Ke b'ukekiya tuk'asu ina zuwa."

Hajia ce tace "Ina zaka je kuma?" Kallonta yayi yace "Ku dai ku tafi gani nan."

Hamna da bak'in ciki ke neman kasheta tsabar haushi kawai taji hawaye sun taho mata, lieutenant ne yayi sauri matsowa kusanta yace "Ke lafiya? Meya miki?"

Saida ta nuna Ammar tace "Abba na fad'a mishi bana so yana shammatar min jiki amma ya k'i dainawa, haka kawai kamar maye ya sa min ido."

Kallonta yayi da mamaki yace "Ke ni banda lokacinki, girma ya zo min yanzu na wuce ajinki wallahi."

Yana fad'a ya wuce b'angarensu, k'ofar Amar yaje kamar Allah ne ya aikoshi ya shiga jijjiga mishi k'ofa, cikin kasala ya taso ko baccin ma baiyi ba su gama tijara shi da Umaimah kan shinfid'ar gado da bata gyara masa ba, yana bud'ewa Ammar yace "Shege, wato ina can ina bud'ar baki dan murna ku kuna can kuna nanik'e tsakani k'ugu da k'irjin matanku, to fito kaje ka d'ora mana shayi a k'ofar gida zanje na tado sauran matsiyatan."

Da mamaki Amar yace "Ammar Amna ta haihu ne?"

Cike da isa yace "Biyu, biyu yaro ta haifa min, a halin da ake ciki yanzu zan iya bada 'ya kuma nima za'a iya bani 'ya."

Wani mamakin ne ya sake lullub'e shi yace "Ban gane ba, kar dai yan biyu ta haifa maka mace da namiji?"

Sororo ya kalleshi yace "Ban gane kar dai ba? Bai kamata bane ko me kake nufi?"

Cike da damuwa yace "Kai sarkin masifa, ni ba haka nake nufi ba."

Hanyar b'angaren Junaid ya nufa yana fad'in "To maza kaje ka d'ora mana shayi."

Niyyar komawa ciki yayi yana fad'in "Ba uban da zan d'ora ma shayi yanzu ehe."

Shi dai baisan ya akayi ba saiji kawai yayi har ya shak'o wuyan rigarshi yana fad'in "Sai ni Ammar, ni zaka d'ora ma inba haka ba ubanka zaka ci Allah a cikin daren nan."

Cikin son k'wak'ule hannunshi yace "Naji to zan d'ora sake ni."

Sakinshi yayi da sauri ya shige ciki yana fad'in "Sai naga tsiya yanzu in zaka biyo ni ciki ne."

Saida ya rik'e k'ugu yace "Kai dai kafi kowa sanin waye d'an uwanka, kaine zaka bayar da labari na ba wai wani ya baka ba, k'arami ne a cikin k'ananun aikina na shiga ciki, to miye a ciki? Daga kai har Umaimah a gabana kuka girma, dukanku k'annai na ne to sai me."

Juyowa Amar yayi ya mayar da k'ofar ya rufe ya tunkari inda yake jin k'arar motoci yana fad'in "Naji dan Allah zan d'ora, je taso sauran."

A wurin Junaid ma haka abun yake bayan ya gama kiranshi gwauro sannan ya iza k'eyarshi gaba, Jibril ma haka taso shi gaba yayi har da Jamil ma bai bari a baya ba, yana dawowa k'ofar gida ya same su mai gadi na kunna musu wuta a mangal, Jibril ne yayi wata doguwar hamma yana fad'in "Allah gamu gareka, wannan lamari sai kace a mulkin mallaka."

Junaid ne yace "Muyi fata kawai d'ora shayin nan ba kullum zai ce sai mun d'ora ba, dan in kullum ne akwai matsala wallahi."

"Shawara mai kyau." Ammar ya fad'a daga bayansu, saida ya k'araso yace "Yanzu ku haihuwar da aka min ita ce ba zaku iya tayani farin ciki ba duk kuke k'ananan maganganu, sai yaran sun girma kuma kuce zaku dakesu wai sunyi ba daidai ba, to duk uban da bai tayani murna yanzu ba yace zai dakar min yara Allah shari'a ni dashi daga nan har tahatas-sara."

Junaid ne yace "Allah ya baka hak'uri duniyar Amna, farin ciki mu ai mun fika dan mu aka ma haihuwa."

Kallon jamil yayi yace "Jamalun (rak'umi๐Ÿ˜‚, amma ya cuceka) shiga ciki ka samo k'atuwar tukunya da wake da shinkafa ka d'ora mana, zanje yanzu a samo mai yanda zai ishi kowa har ayi wanka dashi."

Jamil take ya b'ata rai kamar zaiyi kuka, shi kuma meya had'ashi da dafa wake da babbar tukunya? A ransa yayi tsaki ya shige cikin gidan kamar ya kwamtsa ihu, kallonsu yayi su kuma yace "Kuyi da jiki mana kuna abu kamar yan mata."

Amar ne ya kallesa a ransa yace "Yau ni naga ikon Allah, kuma ba damar magana wannan jaraba."

Hannu ya tara musu yace "Mai makullin mota ya ban."

Junaid da makullinshi ke tare dana d'aki ne ya mik'a mishi yace "Dan Allah yanda na baka motar nan lafiya ka dawo min da ita lafiya, kar kaje ka ja min jarfa ka sani zuwa ofishin yan sanda ko gendarmerie."

Hararanshi yayi yace "Wato ga Ammar masifaffe jarababbe d'an masifa d'an bala'i wanda aka haifa ana tsaka da yak'in duniya na farko."

K'wafa yayi ya shiga gidan Amar yace "To me ya rabaka da abinda ka fad'a d'in."

Yana d'aukar motar ya fito da gudu da gangan yayi kansu hakan yasa su watsewa daga wurin a tsiyace, yana wucewa ya zuro kai ta k'ofa ya musu gwalo, kai dukansu suka girgiza, bai d'auki lokaci ba ya isa asibitin, ya samu Ummy da ma'aikaciyar dake aikin kwana a asibitin sun gama kimtsa Amna duk abinda take buk'ata sun mata tare da yaran, har an shiga da ita d'akin hutu ta kwanta tare da duka yaranta, su Hajia ne suka musu sallama suka tafi sai Husseina aka bari da Ummy su kwana anan, har Hamna zata shiga mota yace "Ki bari zamu tafi tare dake."

A lokacin babu wanda ya iya tanka masa dan ba k'aramin shan kunu yayi ba, hatta Ummy sai taji tsoron ko da hararansa bare tace a'a, ita kanta Hamna ta tsorata sosai sai kawai ya shige ya barsu, ko da suka koma ciki Ummy ya tambaya abinda suke buk'ata, magunguna ta rubuta wanda zasu taimaka mata ya siyo ya dawo, lokacin sukayi saida safe suka fito shi da ita.

Tunda suka d'auki hanya babu mai magana sai Hamna dake addua'r Allah ya kaisu lafiya, saida suka kusa kaiwa gida ya taka birki ya jingina bayanshi a kujera, kanshi na kallon sama kamar ba zaiyi magana, tunda taga haka ta fara sallalami da duk addua'r da ta zo bakinta, tana tsaka da addua'rta taji muryarshi irin babu wasa a ciki yace "D'azu kinyi maganar yara uku, me kike nufi da abinda kika fad'a?"

Saida ta zaro ido tsabar tsoro kafin ta k'ank'ancesu a ranta tace "Yayin da wasu ke zuwa duniya lokacin wasu ke barinta, Hamna kuma ta wannan hanyar k'arshenki zai zo."

Ba tare data kalleshi ba cikin b'ari da rawar murya tace "Ba..ba abinda na...ke nufi, ina tambayarka ne kawai."

D'agowa yayi ya daki sitiyarin motar da k'arfi ya kalleta yace "Hamna na miki kama da sakarai ne?"

Haba wane mutum, ai sai ta fashe da kukan da babu hawaye tana girgiza kai tace "A'a, a'a yah Ammar, dan Allah kayi hak'uri ka kaini gida."

Cikin tsawa yace "Idona zaki kalla ki min magana."

Da sauri ta kalli fuskarshi sai kuma tayi k'asa da kanta tace "Dan Allah kayi hak'uri karka cutar dani."

Bayan wuyanta ya shak'o ya matso da fuskarta gaf dashi yace "Ni zaki rainawa wayo Hamna, tun a waccen lokacin naga alamun ciki a tare dake, kwanciyar hankalin Ummy kawai yasa nayi shiru, amma yau ba zan barki ba sai kin fad'a min gidan uban da kika kai min ciki na."

Yanzu kam kuka ta fara na k'warai sosai har hawayen na shiga bakinta sun jik'e leb'enta sharkaf, ganin bata da niyyar magana yasa shi sakinta ya kuma dukan sitiyarin motar da k'arfi har wata razananniyar oda ta fito, k'amewa ta sakeyi ya kalleta cikin jin haushi yace " Hamna bana son dukanki, ke kad'ai ce bana jurar ganin cutuwarki, ki taimaka ki fad'a min ya kikayi da cikin nan Hamna, idan kuma kin zubar dashi ne kamar yanda nake tunani ki fad'a min."

Kallonshi tayi cikin kuka jin ya fad'a mata mafitarta, sunkuyar da kai tayi tace "Kayi hak'uri yah Ammar."

Lumshe ido yayi a k'alla tsawon minti biyar yana saita nutsuwarsa, saida ya daidaita kansa ya kalleta yace "Nayi hak'uri da me? Da cikin nawa da kika zubar?"

Da sauri ta d'aga masa kai alamar eh, rintse ido yayi ya yamutse fuska kamar zaiyi kuka, ya d'an jima a haka kafin ya bud'e ido yana sauke ajiyar zuciya ya kalleta yace "Hamna kinsan me zai hana ni sake miki wani cikin a yanzun nan?"

Fik'i-fik'i ta masa da ido ta kuma kallon titi ba tace komai ba, d'orawa yayi da cewa "Saboda yer uwarki ne, wallahi ba dan Amna ba da saina miki wani cikin naga abinda zai faru, ke ko da zaki zubar dashi ne saina k'ara miki wani sai dai mu tabbata a haka, amma..."

Kallon titin shima yayi cikin nutsuwa ya ci gaba da cewa "Ina ganin mutumcinta sosai, ina girmama al'amarin Amna har zuciyata, ina ganin k'imarta da darajarta a idona, ta kasance wacce tafi kowa kusanci dani, ta zauna dani sanda kowa ke kirana mahaukaci da ganin rashin tarbiyata, ta zauna dani ta fahimce ni ta shanye komai daga gareni, ta juri dukana ta shanye bak'ar maganata tayi dariya ga fitsarata, duk sanda na zalinceta bata tab'a fitar da k'walla a idonta ba sai dai tayi kukan da babu hawaye, duk sanda nayi niyyar dukanta bata guduwa sai dai ta tsaya wurin ta shiga bani hak'uri, wannan haukan nata na birge matuk'a. Ki sani yau kinci albarkacin yer uwarki, ba dan haka ba da sai kin gane kurenki na zubar min da ciki da kikayi, amma ko yanzu ma zaki gane kuren naki."

K'wafa yayi mai k'arfin gaske tare da tayar da motar ya fara ja, suna tafiya ya juya ya kalleta, ganin har yanzu bata saki jikinta ba sai share hawaye take, wani uban rank'washi ya gaura mata akai yana fad'in "Shegiya 'yar bak'in cikin tsiya, wai yaron ne da zaki haifo min kike jin haushi da hassada, a ganinki da ki haifo min shi gwara kin min asararshi, to Allah ya isa Allah saiya saka min wallahi dan ba yafe miki zanyi ba, mai bak'ar zuciya kawai."

Tunda ya rank'washeta ta baje baki tana kuka, cikin jin haushi ya sake shirga mata k'ulli a baya yana fad'in "Dan ubanki rufe min baki, Allah kinci sa'a bana son dukanki da saina karya k'asusuwanki yau a garin nan."

Hamna dai da yake muguwa ce k'ala ba tace masa saida suka isa gida tana wannan kuka kamar an mata mutuwa, a k'ofar gida ya tsayar da motar ya bud'a zai fito ita mata fito fuska rufe da hijabi, nufa yayi wajensu Junaid dake zaune suna hira suna aikin daya sa su, saida ta bud'e k'aramar k'ofa zata shiga dama wandon bacci ne gareta ta kalleshi tace "Ammar mugu Ammar azzalumi mai bak'ar zuciya, Allah ya isa Allah ya saka min duk cut..."

Da gudun bala'i ta k'arasa shiga ciki kamar zaki ya biyota ta haye sama, Ammar daya bita da kallo su Amar ne suka kwashe da dariya, kallonsu yayi a k'ufule yace "In ban muku wanka da tafasashen shayin nan ba ku ce ba namiji bane ni."

Kowa kama bakinshi yayi kamar sun cika iska, ture Jibril yayi daga kan kujerarshi ya fad'i k'asa ya zauna yana fad'in "Zan kama ki ne yarinya, Allah zaki san ni kika tab'o yar banza mai zubin gwiwar daji."

Amar dake ta rik'e dariya ne ya kasa ya mik'e tsaye ya mik'o mishi d'an k'aramin bol d'in shayi na glas yace "Babban yaya ga shayinka, premier ( na farko) ne."

Lokacin kowa ya samu damar sakin dariyarsa har da masu rik'e ciki, kallonsu yayi da niyyar masifa sai kuma ya fashe da dariya shima yasa hannu ya karb'a ya kurb'a, saida ya kallesu ya sumbaci yatsunshi biyu ya jefa musu sumbar yace "Ina sonku k'annai na, kune rayuwata fa."

Jamil ne ya fito duk yayi gumi yana ganinshi yace "Yawwa Jamalun ya ake ciki? Waken ya dahu ne?"

Cikin jin haushi Jamil yace "Da k'yar na tashi Nana daga bacci ta bud'e min madafa, da k'yar na samu na d'ora ruwan, yana can zata k'arasa dafawa."

Girgiza kai kawai yayi suka ci gaba da zuk'ar shayinsu suna hira, wani abun daya fad'a kowa sai yaji abun wani iri, wani suyi dariya kamar cikinsu zai fashe wani kuma su girmama al'amarinshi, kamar yanda ya fad'a kam saida akayi sallah asuba kad'ai ya barsu suka koma cikin gida shima ya shiga ciki, wanka yayi ya canza kaya farare tas wanda rigar t-shirt ce sai wando 3 quater kafin yasha magani saboda k'afarsa da har ya manta akwai ciwo, kiran Ummy yayi ya tambayesu yanda suka tashi tare da neman a bashi Amna, sosai suka jima suna hira cikin nishad'i kafin suyi sallama yace sai ya zo d'aukarsu.

Misalin *06:30* na safe Hamna ma ta kirasu suka gaisa ta tambayi yara, saida suka gama waya har ta kashe Amna mijinta ya zo tunaninta, tunawa tayi da fa ciwo a k'afarsa, sannan mutum ne dake wasa da cikinsa, idan ya ga abinci ne zai ci idan kuma bai gani ba babu ruwansa, ita kanta wani lokacin sai tayi rarrashi yake ci kafin ya fita da safe, sake kiran Hamna tasa Ummy tayi ta bata wayar, tana d'auka tace "Na'am Ummy."

"Ni ce yer uwa." Ta fad'a murya k'asa k'asa, d'orawa tayi da "Dan Allah yer uwa wani taimako zaki min."

Daga b'angarenta ta amsa da "Wane irin taimako kuma Amna? Kin fara manta yanda muke ne?"

"A'a, amma nasan abu ne mai wuya a wajenki, ki min alk'awarin zaki min kafin na fad'a miki dan Allah."

Cikin rashin son wasa tace "Fad'a min ina jinki, nayi alk'awarin."

Cikin muryar rarrashi tace "Yer uwa taimaka min zakiyi dan Allah idan an kammala abin kari ki kaiwa yah Ammar, sannan idan kinje ki d'ora masa ruwan zafi ki ce masa ya gasa k'afarsa sosai sannan yasha magani, dan Allah." Ta k'arashe da sake kashe murya.

Wani mamaki ne ya kashe Hamna tare da tunanin taya zata je su had'u bayan abinda ya faru jiya? Gashi kuma tayi alk'awari, bayan alk'awarin kuma tasan halin Amna da rik'o zata iya yin hushi da ita akan haka, a hankali ta bud'a baki tace "Shikenan naji zanyi, tunda so kike ki mayar dashi kamar wani jariri."

Murmushi Amna tayi tace "Jariri ne mana, har yanzu baya iya kula da kanshi, Hamna yana buk'atar kulawa."

Tsaki Hamna tayi tace "Ki kular min da yarana ni, banda lokacin haukanki ke da mijin na ki."

Kashe wayar tayi ta aje ta sauko k'asa, madafa ta shiga su Zeituna na aiki ta kalleta tace "Aunty Zeituna idan kun kammala Amna tace a fitarwa mijinta da abincin saina kai mishi."

Cike da sakin fuska Zeituna tace "Kin ganshi nan zan fidda mishi kuwa, dan bana mantawa da babban d'an gidan nan, tunda yau babu mai girka masa."

Kallonta tayi tace "Amma kun gama da wuri yau aunty."

"Eh saboda za'a kaiwa yan asibiti ne." Saida ta d'auki wanda Zeituna ta nuna mata tace "Wa zai kai musu?"

"Ni nake son tafiya tare da Abban Fatima." Cewar Zeituna, kallonta Hamna tayi da mamakin sunan data kirashi dashi, wato tunda ita ma yanzu ta haihu dashi ba buk'atar ta ci gaba da kiranshi da Abban Ammar? Abun ya birgeta sosai har taji ina ma tana da 'yancin kiran d'anta da sunan ubansa data kirashi da *Shureim Ammar* da babbar murya kowa yaji, karb'ar abincin tayi ta fito ta nufi b'angaren nasu, ta manta bata saka ko da mayafi ba bare hijab, wannan siket d'in na atamfa da rigarsa wanda suka kama jikinta suka zauna daram dam, ga k'ibar data k'ara yasa k'ugun ta ya sake sama ya zauna da kyau, d'aurin kallabin mai sauk'i ne wanda zamu iya kiransa da ture kaga tsiya, dan ya turo sosai gaban goshinta, ko kwalli babu a idonta haka ta bud'a k'ofar d'akin ba tare da tunanin zata same shi a bud'e ba, amma sai ji tayi ya bud'e a hankali ta shiga tana kallon yanayin d'akin shiru kuma babu wuta sai hasken safiya kawai, saida ta je gaban teburin nan ta aje kwanukan ta nufi hanyar madafa dan d'ora ruwan d'umin kawai tayi tafiyarta, ta taka d'aya biyu na uku taji wata tattausar murya a bayanta yace "Ba sallama, ba neman izinin shigowa bare ki gaishe da mutane?"

Tsayawa tayi sai jikinta da taji ya fara rawa rawa kamar zata kifa k'asa, had'e fuska tayi alamar bata son wargi sannu sannu ta juyo, inda taji maganar ta kalla sai taga ashe ya kishingid'a ne kan kujera yayi luf, turo baki tayi cikin shagwab'a tayi k'asa da kanta tace "Ina kwana."

Wani narkakken kallo ne yake mata inda yake jin abubuwa da dama na b'abb'akowa daga k'asa suna yin sama, ganinta a haka ba k'aramin gigita nutsuwarsa tayi ba, a hakan daya ganta ta tuna masa da duniyarsa, dan atamfar ma kala d'aya ce haka d'inkin, kuma ita ma haka suka amsheta a ranar daya fara ganinta dasu, lumshe ido yayi tare da buk'atuwar son ganin hak'oranta ko da ba ta sigar dariya bane, hakan zaisa ya yarda cewa ta daina hushi dashi, amma ganin fuskarta a had'e a haka zai rikita lissafinsa
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment