Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

murmushi yace "Kamar ya?"

Saida ya kalli k'ofar gidan yace "Da alama akwai wani abu da kake ji, ko ba haka ba?"

Matse bakinshi yayi cikin sanyin jiki yace "Kuskure ne, amma bai kamata na bari haka ta faru ba tun farko."

Gyara tsayuwa Ammar yayi yace "Kuskure kamar ya? Soyayyar taka ce kuskure ko kuma wacce kake so ce bai kamata ka so ta ba?"

Shima gyara tsayuwa yayi yace "Wacce nake so mana, kai fa kasan komai."

Girgiza kai yayi yace "A'a ban sani ba, fad'a min miye matsalar?"

Cikin nutsuwa Amar yace "Ammar kasan fa Hajia ba son doguwar mu'amula take tsakaninmu da Hajiarsu Jibril ba, sannan ina auren Umaimah wanda dukansu yan uwa ne, kaga abune da ba zai yiwu ba ai."

Wani kallo ya masa kamar na wanda baisan ciwon kansa ba kafin yace "Yanzu Amar wannan har dalili ne da zai iya sawa ka hak'ura da wacce kake so? Hajia ba tana nusar damu dasu bane saboda Allah, tana so muyi nesa dasu ne saboda izzarta da wani buri na zuciyarta, hakan haka saika haramtawa kanka abinda Allah ya hallata maka."

K'ara matsawa yayi kusanshi ya sake dafa shi yace "D'an uwa, daga ni har kai mun sani ba wai kowa ya auri wacce zuciyarsa ke so bane, umarninta ne muka bi mukayi biyayya, kada ka tauye kanka ta b'angaren abinda kake so in har ba sab'on Allah bane, idan kace zakayi haka kuma wallahi zaka wahalar da kanka ne sannan ka wujijjiga zuciyarka, idan bar Hajia tace bata yarda ba ka tambayeta dalili? Sannan ta fad'a maka hujjar k'in amincewarta."

Nunfasawa yayi ya ci gaba da cewa "Kar kayi wasa da damarka yaro, inhar kana sonta to kawai ka fad'a a gida asan abunyi."

Murmushi Amar yayi yace "Daga yanda kake magana d'an uwa kamar kai ma ka fad'a soyayyar nan ko?"

Murmushi yayi shima yace "Sosai ma, amma ni dalili na da yasa na hak'ura da soyayyata yafi naka k'arfi gaskiya."

Da mamaki yace "Kamar ya? Me yasa ka hak'ura da soyayyarka? Bansan da sarewa ba haka ma tsoro, na d'auka idan ka samu wacce kake so zaka tsaya ne wajen ganin ka same ta ko da hakan zai iya janyo yak'i."

Cikin fad'ad'a murmushi yace "Amar wasu abubuwa basa buk'atar jarumta ko rashin tsoro, kai halal d'in bata haramta maka halal d'inka ba, karin maganar hausa ne da ake cewa wai *ana barin halak ko dan kunya*, ni tawa halal d'in ta haramta mani wata halal d'in ne."

Wani kallo ya bishi dashi na son gano abinda yake nufi, shi kanshi saida ya ji bugun zuciyarshi ya k'aru da sauri sauri, cike da mamaki da tsoron abinda zai fad'a yace "Ammar, kar dai kace min kankana kake so?"

Rintse ido yayi tare da buga tagumin rashin jin dad'i, ya jima haka kafin ya bud'e ido ya kalleshi, wata iska ya furzar mai zafi tare da d'aga kafad'u yace "Amna duniyata ce, uwar 'ya'yana ce, kwanciyar hankali na ce da farin ciki na, k'aramin abu idan ya gilma ta gaban rayuwata marar dad'i gurinta nake zuwa na samu nutsuwa, ba zan iya mata butulci ba har na bari tasan abinda ke zuciyata ba, Hamna kuma ita ce burin zuciya ta, abincin ruhina sannan mafarkina, su biyun sun sani tsakiya bansan ya zanyi ba, *sune k'addarata*, na d'auka da hannu biyu har naga yanda ubangiji zaiyi dani."

Yana gama fad'a ya bar wurin, da kallo ya bishi sai yaji kamar ya zubar masa da hawaye, shima cikin k'warin gwiwa ya shiga wajen Hajia dan fad'a mata abinda ke ranshi babu b'ata lokaci, bayan sun gaisa yake sanar da ita shi fa yana son k'ara aure, cike da mamaki tace "Shalele aure kuma? Yaushe akayi auren naku da har zaka k'ara wani? Umaimar bata kwantar maka da hankali ne?"

Cikin turo baki yace "Hajia kawai ina so na k'ara auren ne, dan Allah kada ki hanani."

Girgiza kai tayi tace "Ba zan hana ka ba, amma fad'a min wace yarinya ka samu?"

"Farisa." Ya fad'a ko kallonta baiyi ba, k'ank'ance ido tayi tace "Wai me yasa ba kwa ganewa ne yaran nan? Shalele ya zaka min haka? Wace Farisa kuma yarinyar da ko jinin al'ada yanzu ne ta fara shi."

Kallonta yayi yace "Eh ita Hajia, a hakan ta min wallahi ina so."

"Kayi hak'uri shalele ka nemi wata, ba zan yarda a sanadiyarku ba na rasa ji da kaina da d'aukakata ba."

Kallonta yayi da matuk'ar mamaki, amma daya tuna abinda Ammar ya fad'a masa sai yace "Hajia d'aukakarki? Yanzu akan hakane zaki hana mu abinda zuciyarmu ke so?"

Shiru ta masa sai kawai yace "To Hajia me yasa ba kya son aure na da ita?"

"Saboda kakarta tsohuwar karuwa ce, ita kuma wannan rayuwa tana bin ahalina kamar yanda yan biyu ke bin mahaifa, a dalilin auren Farisa kana iya haihuwar yaran da zasu addabeka."

Cikin jinjina kai yace "Hakane, na gani kam, to amma Hajia taya su tanti Zeinabu suka samu Junaid ta wannan hanyar bayan kuma hakan ba d'ab'iar zuri'arki bace? Ko dai zama da Hajiar..."

Cak ya tsaya da maganarsa saboda hannun data d'aga da niyyar marinsa sai kuma ta tsaya, kallonshi tayi ido jawur kamar zatayi kuka ta nuna masa k'ofa tace "Fita, fitar min a d'aki."

Mik'ewa yayi ya kalleta yace "Kiyi hak'uri Hajia, Umaimah ba irin matar da nake so bace, ba zan iya hak'urin zama da ita ba gaskiya har bak'in cikinta ya kashe ni, ki taimaka ki yarda da aure na da Farisa."

Fita yayi ya rufe mata d'akin, zaune tayi kan gado ta fara wa kanta karatun tanutsu, wata rana fa komai zai iya fitowa in tayi wasa, to miye mafita daya wuce ta amince da buk'atarsu, take ta sawa zuciyarta ruwan sanyi ta d'auki niyyar gyarawa ko dan kar a mata dariya ma.

*Da dare* ma kowa na harkar gabanshi ya wuce d'akin Ummy data kira shi a waya tace ya zo, da sallama ya shiga ya zauna yace "Ummy gani kince na zo."

A hankalce ta kalleshi tace "Ammar, da izinin ka aje Baba Inussa a asibiti?"

Kallonta yayi yace "Ummy kafin nayi taimako saina nemi izinin wani? Kawai naga yana buk'atar kulawar asibiti ne shiyasa na d'aukeshi."

"Amma kasan hakan me zai iya janyowa kuwa? Me yasa baka tsoron abin fad'a ne?"

Nisawa yayi yace "Ummy ba haka bane, kamar yanda zamu iya bayar da komai namu ga Alhaji matsayinsa na kakanmu haka shima Alhajin, wani k'aramin abune daya faru tsakaninsu shekaru da dama, mu bamu san komai ba bai kamata mu tayasu hura wutar ba."

Cikin d'aga murya tace "Ammar, ina so ka sallameshi daga asibitin nan ka kaishi wata ko kuma ka mayar dashi gida ka ci gaba da bashi kulawar, amma zamanshi a asibiti zai janyo maka matsala da ma ni kaina, ni kuma wallahi ba zan yarda ka k'ara ja min banzayen matsaloli ba ina zamana lafiya."

Kallonta yayi fuskarsa a had'e yace "Kiyi hak'uri Ummy, a gaskiya ba zan iya d'aukeshi daga nan ba, bugun k'irji nayi na nuna na isa dashi shiyasa na kawo shi nan, saboda tsoron Hajia kawai ba zan lalata aikin alkairin da nayi niyya ba, Ummy ke ma ya kamata ace kin rage tsoron nan da kike mata, tsoron Hajia yana saki kina aikata kuskure a kowane numfashi na rayuwarki."

Tsuru ta masa da ido, gaskiya ne abinda ya fad'a fa, amma da yake abun ya gyauraya da jininta saita rufe ido tace "Naji ina tsoronta, kawai ina so ka d'aukeshi daga asibitin nan."

Kallon mamaki ya mata yace "Hajia Alhaji ne fa d'an uwan Alhaji na Abbanmu, ya zaki ce a masa haka?"

Cike da k'aguwa tace "To naji, idan ba zaka fitar dashi ba ka fad'awa Hajia tasan da zamanshi, kaga idan ta amince shikenan saiya zauna."

Tashi yayi tsaye ya juya mata baya yana fad'in "Hajia dai, Hajia dai, wai abun alkairi ma saika nemi umarnin Hajia, to wai ita ta busa mana rayuwar nan ne ko me?"

Mik'ewa Ummy tayi ita ma tace "Na sani dama ba zaka yi ba, ban isa na saka kayi ba saboda baka d'auke ni bakin komai ba, kaje kayi duk abinda kaga dama, amma ka sani shirme ko haukanka ba zai k'ara sani a damuwa ba, yanzu b'ace min a gani."

Kallonta yayi yace "Ummy me yasa kullum sai ki kore ni daga wajenki? Kina yawan fad'a min b'ace min da gani, me yasa?"

Cikin b'acin rai ta juya mishi baya tace "Saboda ban son ganin na ka."

K'uri ya mata da ido yana kallonta ta juya masa baya, rintse ido yayi yana sauke numfashi yana son zuciyarsa ta kwanta, bud'a ido yayi har sunyi ja sosai jijiyar kanshi duk ta fito, dunk'ule hannunshi yayi ya daki bangon wurin, juya baya yayi shima a lokacin ta juyo da sauri, yana juyowa suka had'a ido yace "Ba kya son gani na? Ni d'an halak ne Ummy kuma mai biyayya, tunda har kika fad'a da bakinki ba kya son ganina zan miki nesa da kaina ta hanyar samar miki da farin ciki, amma duk da haka duk ranar da kika buk'aci na zo gareki zan zo da saurina, saboda ke mahaifiyata ce kuma ina son ki, *ina sonki sosai* Ummy."

Fita yayi daga d'akin sai kawai Ummy ta durk'ushe ta fashe da kukan da bata san ma na miye ba. Shima yana fita bai kula kowa ba ya nufi b'angarensu, Amna na zaune cikin k'ananan kaya riga da wando sai yara dake wasarsu, cikin dakakkiyar murya yace "Ki shirya kayan yaran nan da safe zamu tafi Niamey."

Zaro ido tayi ta bishi da kallon mamaki shi kuma kai tsaye d'akin shi ya shiga, kamar hauka haka ya shiga had'a kayanshi yana turawa a akwati, jin Amna ta shigo shi kuma baya so ya zubar da hawaye gabanta ko ya sauke hushinshi akanta yasa shi saurin shigewa ban d'aki, da kallo ta bishi cikin sanyin jiki ta kalli kayan da yake ta bankawa a akwati, a hankali ta shiga gyara zaman kayan tana saitasu, tsawon lokaci kafin ya fito yana ganinta ya sunkuyar da kai yace "Bana no ki aje min kaya, kije ki had'a naki dana yaran nan, idan kuma ba zaki tafi ba ke kika sani zan d'auki yarana."

Da sauri tace "Amma yah..." Da k'arfi kamar zai tsaga d'akin yace "Amna bana son tambayar banza, kiyi abinda na fad'a miki kawai."

Shagwab'e fuska tayi ta sake takowa zata matso ya sake daka mata tsawa "Amna ki fita ki bani wuri, bansan ganin kowa a kusa dani, bana so na sauke b'acin rai na akan ki."

Da sauri ta sake takowa gabanshi tana fad'in "Na yarda ka huc..."

Wani bazawarin mari ne ya d'auke fuskarta dashi da yasa ta fad'awa kan gado da k'arfi ta kifa gaba d'aya, rintse ido yayi dan har cikin ranshi yaji marin, cikin hushi da fad'a yace "Na fad'a miki kiyi nesa dani, wai ke ba kya fahimta ne? Ki dinga yin nesa dani kamar yanda kowa keyi mana, yanzu gashi kinsa na mareki a banza."

Juya baya yayi da k'arfi yana dafe kanshi, cikin rawar jiki na bala'in marin data sha tana karkarwa ta mik'e, cike da k'arfin hali ta rik'o hannunshi ta juyo dashi gabanta, suna had'a ido ta fashe da kuka tana shafa kanshi ta ko ina tana fad'in "Dan Allah yah Ammar ka daina, tsorata ni kake idan kayi irin hushin, bana so ka daina kaji, na yarda ka huce a kaina amma karka cutar da kanka ko wani, dan Allah kaji."

Tsakiyar idonta yake kallo sai yaji hawaye na fitowa a idonshi, cakumarta yayi da k'arfi ya matse yace "Me yasa Amna? Me yasa Amna?"

Kuka kawai take har da ajiyar zuciya, jawota yayi jikinshi sosai ya rumgumeta, tun yana yi a hankali har ya fara saka k'arfi yana matseta sosai kamar zai mayar da ita ciki, duk da tana jin zafi amma haka ta daure, sun jima haka kafin ya d'ago ba alamar annuri ya saketa ya juya zai bar d'akin, da sauri ta rik'o hannunshi tace "Ina kuma zaka je?"

A hassale yace "Yaro ne ni Amna da sai kin tambaye ni inda zanje?"

Girgiza masa kai tayi tace "A'a, amma ba zan barka ka fita a halin nan ba yah Ammar, idan ka fita ranka a b'ace zaka iya yin komai."

Tsabar neman fitina saiya rufe ido yace "Amna ni? Mahaukaci dama kike kallona ban sani ba, eh lallai yau ta tabbata kowa mahaukaci yake d'aukata."

Cikin zubo da hawaye ta girgiza masa kai alamar a'a, k'wafa yayi ya juya zai fita ta sake rik'e hannunshi, fizgewa yayi da k'arfi zai bar d'akin ta tare gabansa da gudu, rufe k'ofar tayi cikin kuka tace "Wallahi babu inda zaka je, nasan halinka yah Ammar in dai har ka fita yanzu saika nemi wani da masifa, ka bigeshi ko ya bigeka shine burinka, dan haka na zab'i ka zauna tare dani in ya so ni ka kashe ni, amma hankali ba zai kwanta ba dan bansan da wa zakayi rigima ba."

Belt d'inshi ya fara zagewa yana fad'in "Shikenan, bari na fara miki laga-laga sai na bi ta kanki na wuce."

Matsowar da yayi kusanta da sauri yasa tayi saurin duk'ewa tayi k'asa tana jingina a jikin k'ofar, yana ganin ya saki d'amarar cike da tausayinta ya sunkuya ya kamota, bud'a ido tayi ta kalleshi saiya rumgumeta yace "Amna baki da hankali ko kad'an."

Saida ta rumgume shi sosai tace "Na sani yah Ammar, shiyasa nake so ka dinga saita ni."

Tallabo kanta yayi ya had'e bakinshi da nata ya shiga tsutsa, shiru komai ya kwanta aka shiga wata duniya, ta d'auka an bar maganar tafiya ashe ko kad'an, cikin muryar bayar da umarni ya nuna ta yace "Ki tabbatar kin had'a kayanki dana yaran nan."

Kallonshi tayi, ba zata iya magana ba yanzu kam dan zasu sake samun matsala, sai kawai ta bishi da to da niyyar yin sun tafi ta lallab'a shi tasan meya faru haka.

*Washe gari* da sanyin safiya suka fito a shirye, ko falon Hajia bai shiga ba yace Amna dai taje ta fad'a musu zasuyi tafiya dan kar aga basu nan, haka ta shiga jiki a sanyaye bayan ta gaishesu ta fad'a musu, kowa yayi mamaki amma tunda tace tare dashi ne sai aka bisu da addu'a kawai, tare da Hamna suka fito suka tsaya farfajiyar gida inda suke iya hangenshi tare da yaran a mota yana jiranta, tsaye suke suna sallama inda Hamna ke d'agawa yaran hannu, idonshi na kanta ya fito da wayarshi, sak'o ya rubuta ya turo mata yana ci gaba da kallon fuskarta.

Tana jin wayarta tayi k'ara ta fito da ita ta duba, kallonshi tayi ta kuma kallon wayar, sak'o ne ba mai tsayi ba, amma ma'anarshi da abinda yake nufi da kuma yanda ita ta fahimci sak'on yayi kusa ya tsayar da tafiyar jinin jikinta, kad'an ne ya rage bata iya nuna abinda ke ranta ba, kafe wayar tayi da ido tana sake maimaita karanta sak'on mai d'auke da wasu tsirarun kalmomin kamar haka _"Bansan me yasa ke da Ummy kuka tsane ni ba, amma zan tafi nayi nesa daku dan na hutar da zukatank'u."_

Suka tsaneshi fa yace, shin yasan me take ji a zuciyarshishi a game da shi kuwa? Bai sani ba, Amna dake kallonta ne tace "Yer uwa ko zamu tafi tare ne dan kar kiyi kewata?"

Cikin gigita, cikin rashin sanin madafa, cikin hargagi da son fitar da abinda ke ranta, cikin yanayin da bata san tayi magana dashi ba, yanayin da bata tab'a ma yer uwarta magana ba sai gashi yau dalilin *namiji* ta mata, tsawa ce mai ban tsoro ta mata ta hanyar fad'in "Ba zanje ba malama ki rabu dani, kiyi rayuwarki nayi tawa, duk ke ce silar komai."

Tana gama fad'a ta taka da sauri ta nufi motar, ta tafi da niyyar yin wani abu daban, amma Ameer na lek'o kanshi ta mota ta sauke ido akan yaron sai taji ta rasa kuzari da k'arfin halin, sai kawai ta juya ta nufi inda motar ta take da sauri. Amna da tayi mutuwar tsaye odar daya mata ce ta farfad'o da ita daga doguwar sumar, da k'yar ta iya d'aga k'afarta ta shiga motar suka fita daga gidan, saida ta ga fitarsu da wasu mintuna kafin ta fita ita ma tana kuka.


*Alhamdulillah*
14/10/2020 ร  00:58 - Ummulkhairi: ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ
*BADAK'ALA*
๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ

*Labarin Gaske*

*NA*

_SAMIRA HAROUNA_

*Litattafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._

*SADAUKARWA GA*

๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ _*AHALI NA*_๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

๐Ÿ’ซโœจ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*๐ŸŒŸ
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_๐Ÿค

โ˜† *[ T.M.N.A]* โ˜† ๐Ÿ“–๐Ÿ–Š๏ธ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_

_56_


Ammar dai ya tafi tare da iyalinshi, inda suka kwana biyu a garin Niamey a masaukin da mahaifin Amna ya tanadar musu, a kwana na uku ya gama musu shirin komai har da allura saida aka musu na shiga wajen k'asarsu, ticket ya cirar musu ya aje motarshi anan gidan suka tafi *cotonou*, a kwanakin da sukayi saida yayi magana da abokinshi likita wanda ya yarda da k'warewarshi kan ya ci gaba da duba mishi Inussa, sannan duk abinda ake buk'ata a mishi magana zai bayar, sun isa lafiya kuma da yake harka ce ta dala ya samu masaukin daya dace da tsarinshi da kuma iyalinshi, sun fara rayuwarsu kamar yanda suke yi a gidan, amma anan kullum zai fita waje sai Amna tace ya kula kar ya ja musu rigimar da za'a k'onasu da ransu, shi kuma abinda yake fad'a mata shine "Amna ke ma mahaukaci kike d'aukata, amma ba komai zan kiyaye ko saboda ke."

*A gida* fa abubuwa sun shiga juyin waina inda komai ya fara tafiya a hargitse, Hajia da kanta tace ta amince da auren Junaid da Salma, sannan ta bawa Amar dama ya nemi auren Farisa, ta b'angaren Junaid anyi matuk'ar farin ciki ganin zumunci zai had'u tanan wajen, amma a b'angaren Amar tashin hankali ne ya kunno kai daga wajen Umaimah, dan kuwa ranar da taji labarin saida ta mata dukan tsiya har cikin falon uwarta, hakan ya b'ata ran Amar yace ta je gida kawai saiya neme ta, Alhaji ne ya bashi hak'uri yace ya lallab'ata kishi ne, Zeinabu ma hak'uri take bata dan ita yanzu ta nutsu tun abinda ya faru, amma Umaimah sai botsarewa take wai akan me zai mata kishiya kuma k'anwarta data yarda da ita har take shiga d'akin baccinshi. Saboda gudun matsala yasa Soueiba da Labaran cewa in akwai matsala kawai a bari, Hajia tace ai bata isa ba Umaimahr banza ko uwarta bata isa ta hana auren ba, Farisa aka tambaya idan tana so to babu fashi, abinda ta fad'a kawai shine "Ni karatu nake so nayi."

Hakan yasa Amar d'aukar alk'awarin barinta tayi karatunta har aiki ma udan tana so, magana ta kankama sosai har anyi komai an gama an saka rana.

Duk da akwai mutane a gidan kuma ana hayaniya, amma kowa ya tabbatarwa da kanshi akwai mutum d'aya da babu a gidan, babu nishad'i ko wata raha, Hajia Alhaji da Ummy abun yafi damunsu fiye da kowa, ko kiransu a waya bai cika yi ba saiya kwana biyu, yanzu Hajia saita wuni ta kwana a kujerar nan zaune bayan gaisuwa babu wanda zai tsokaneta ko ya sakata dariya ko nishad'i, idan abinci ake ci haka kowa zai gama ya tashi, inba tashin hankali ba na auren Amar ko kuma sab'ani na zaman tare baka jin komai a gidan, dan haka yanzu kowa ya zama shiru zaman d'aki yafi yawa, kowa saiya had'a kan yaranshi k'ananan ya shige d'aki ya zauna abinshi, har Zeituna ma dake da yarinya d'aya, sai dai ita suna waya da Ammar kullum dan yana girmamata sosai.

Hamna ma gaba d'aya ta canza kamar ba ita ba, jikin nan nata duk ya rage yanzu sai lalacewa take, tafi son zama wajen aikinta fiye da ko ina, idan ka ganta gidan nan da dare ne, kuma gari na wayewa zatayi sammako ta fita, hatta Shureim yanzu ta rage kusanci dashi kamar da, sai dai tana waya da Amna akai akai suna gaisawa, wani lokaci haka zata tashi tayi ta b'ata rai a banza, a haka ita ma rayuwar ta godewa Allah kawai zata ce.

*A kwana a tashi* ba wuya a wurin Allah, sai gashi an sake d'aura auren Junaid da Salma da kuma Amar da Farisa sai Jamil da amaryarsa *Zeinab* shima, amare sun tare sun fara rayuwarsu mai cike da jarabawa, tunda akayi bikin aka gama Umaimah ke hushi da Amar bata kula shi, har ranar girkinta ya zagayo da safe ina abin kari tace ai bata dafa dasu ba, banza ya mata ya fita da rana ma bai dawo gidan ba, da dare ma daya tambayi abinci tace yaje amaryarshi ta bashi, murmushi ya mata ya fita daga d'akin, yana zuwa ya samu amaryarshi kam ta mishi dubaru ya cika cikinshi, ko da ya dawo bai kulata ba ya kwanta shima. Washe gari ya bata kud'i haka ma Farisa yace tayi girki, lokacin da take aiki a madafa Umaimah ta dinga masifa akan me zata karb'e mata ranar girki, ita dai bata ce komai ba saboda tana tsoronta.

_Yan uwa rayuwa wata aba ce dake tattare da k'alubale da shubuha, wani lokacin zata iya zuwa maka yanda kake so, wani lokacin kuma ta zo da sab'anin haka, ka yarda ka karb'a ko kuma ka kafirce mata ya rage naka, so da dama mukan so abinda ba alkairi bane a gare mu, haka ma sau tari mukan fifita tsana ga wanda yake alkairi gare mu, shiyasa a kullum ya kamata kayi fatan zab'in Allah._

*Daren yau* duk suna zaune ana cin abinci Jamila ta shigo da gudu wai Umaimah suna fad'a da Farisa sai dukanta take, da gudu kowa yayi b'angaren nasu suka same su, tsaf tayi zaune kan yarinyar mutane tana mai k'aramin ciki tana bugu, ba tsayawa komai colonel ya d'auketa da mari, da k'arfi yasa k'afa ya turata tayi baya yana fad'in "Jaka kawai, yaushe haukan naki yayi tsanani har haka?"

Lieutenant ne ya rik'e shi yana fad'in "Ya isa dan Allah karka ji mata ciwo."

Tana mik'ewa Hajia ma ta kwad'a mata mari tana fad'in "Mahaukaciyar ina ce? Baki san halin da take ciki bane da zaki mata wannan dukan? Jaka ce aka kawo miki?"

Tsayuwar rashin mutumci tayi tana ta wani girgiza da gunguni, Ummy ce ta kama Farisa ta shiga d'aki da ita tana dubata, Hajia kuma kallon Umaimah tayi tace "Bari Amar d'in ya dawo kiga yanda zanyi dake, wallahi sai kin shiga taitayinki."

Wani par-par tayi da ido tana motsa baki tana fad'in "Ya dawo d'in a sa ya yanka ni sai me?"

Wani mari colenel ya sake datsa mata a kumatu wanda yayi sanadiyar gabcewar jini daga hancinta da bakinta, duk'ewa tayi rufe da bakinta ta fashe da kukan da ko sauti babu tsabar azabar marin, cikin bala'i yayi kanta zai sa mata k'afa yana fad'in "Dan ubanki uwar tawa kike fad'awa magana? Sa'arki ce Hajia ko nine kika raina?"

Da sauri lieutenant ya rik'eshi, jinjina kai Hajia tayi kawai ta fita a d'akin, bayanta suka bi sai ita da aka bari tana kuka, suna shiga falon akayi cirko cirko ana kallon Hajia data sunkuyar da kai, Alhaji dake zaune anan bai tafi ba dama ya tambaye su lafiya, kafin wani yace wani abu Hajia ta d'ago cikin dattako tace "Ba komai, zanyi maganinta."

Tana fad'a ta mik'e ta nufi kan teburin cin abinci ta zauna, kowa cikin nutsuwa ya je ya samu kujera ya zauna, Zeituna da Zeinabu ne suka zuba abincin suka aje ma kowa gabansa, amma abun shiru babu armashi kamar anyi mutuwa, Hajia ce ta d'ago kai ta kalli kowa sai kawai tayi murmushi ta tangale hab'arta da bayan hannunta tace "Hausawa sunyi gaskiya da suka ce *duk wanda ya tuna bara baiji dad'in bana ba*, tabbas mutum baya sanin abinda yake so sai ya rasa wanda yake hannunshi, *Ammar* yana raye amma yau ranar yabon ta zo, duk da wani mawak'i yace wai *kar Allah ya
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment