Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

yara biyu ne dake wanda kika samu a gidan nan, sannan abinda ke faruwa yanzun yana da alak'a da d'aya daga cikin ya'yan naki, ki zauna dan Allah sai muyi magana."

Komawa tayi ta zauna gabanta na fad'uwa kan abinda Hajiar tace, kallon lieutenant tayi tace "Kira min Sa'ada ka ce inji ni duk inda take yanzu ta zo ina nemanta."

Wallahi wannan Hajiarsu ce ta baya mai magana d'ayan nan, in yayi wasa zai sha ashar yanzu dan haka da sauri yace "To."

Wayar shi ya fiddo ya shiga neman lambarta, Gambo ta kalla tace "Ka kira min Ammar ka ce ya zo."

"To." Ya fad'a yana ciro wayarshi a aljijun balaluwarshi, yana gama magana dashi a lokacin har ya fita da yaran, sake umartarshi tayi daya kira Hamna sannan ta kalli Hadiza tace "Husseina na ciki, ki ce ta fito zamuyi magana."

"To Hajia." Ita ma ta fad'a ta nufi d'akin jikinta har rawa rawa yake na tunanin abinda ya faru tsakanin Ammar da Hamna daya har yasa Ummy suke k'ok'arin rabuwa da lieutenant.

Hamna ma ko da kiranshi ya shigo wayarta tana k'ofar gidan, saida hancin motar ta ya shigo sannan ta d'auki wayar, shi kuma yana hangenta ma saiya kashe kawai.


_Kuyi hak'uri da wannan, yau ne sai a slow._


*Alhamdulillah*
04/11/2020 Γ  14:38 - Ummulkhairi: πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨
*BADAK'ALA*
πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨

*Labarin Gaske*

*NA*

_SAMIRA HAROUNA_

*Litattafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._

*SADAUKARWA GA*

πŸ‘¨β€πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘¦ _*AHALI NA*_πŸ‘¨β€πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘¦

πŸ’«βœ¨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🀝

β˜† *[ T.M.N.A]* β˜† πŸ“–πŸ–ŠοΈ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_

_66_


Husseina ta fito ta samu wuri ta zauna, tunda sauran matan suka fahimci zaman ba dasu bane kowace tayi d'akinta, sai lieutenant dake kiran Ummy, k'in d'aukar kiranshi tayi tunaninta hak'uri zai bata, Hajia ya kalla yace "Hajia ta k'i d'auka fa."

Wayarta ta lalubo a bayanta tana fad'in "Ban ga laifinta ba mana."

Kallon Hajiar yayi da mamaki, wai duk abinda tayi bata ganin laifinta? Kiran Hajia kad'ai ta d'auka cikin ladabi tace "Hajia."

Kai tsaye tace "Kina ina Sa'ada? Maza ki zo gida ina son ganinki."

Cikin rarrabawa tace "Hajia..ina..kan hanyar...zuwa gida ne."

"Wane gida? Sa'ada kina da gidan daya wuce nan ne? Kina da hankali kuwa? Ke yanzu dan Allah idan kika je ki ce me? Yaji kikayi? Kiyi sauri ina jiranki yanzu."

Cikin ladabi tace "Wallahi Hajia da gaske na ke, ina cikin bus d'in da zata tafi *Arlit*, yanzu haka mun wuce *Tessaoua*."

Shiru Hajia tayi tana kallon lieutenant da shima yake kallonta yana sauraren abinda take fad'a, sunkuyar da kanshi yayi k'asa ita kuma ta harare shi, wata shawarar ta yanke kawai bari ta barta yaje har can ya dawo da ita, kashe wayar tayi cikin fad'a tace masa "Ka shirya tafiya yin bikonta gobe goben nan, babu ruwa na da iskanci kaji na fad'a maka, kai in ba'a hak'uri da ko haihuwarku nayi a gidan ubanku ma."

K'wafa tayi mai k'arfin gaske dake nuna ranta ya b'ace sosai, kafin wani yayi magana Hamna ta shigo tare da Ahmad, da mamakin ganin mahaifinta taje gabanshi ta zauna tana fad'in "Abba? Yaushe ka zo?"

Kallonta yayi yace "Banjour."

Lab'e baki tayi tace "Pardon Abba, bonjour."

Gaisawa sukayi sosai inda take kallon mahaifiyarta da mahaifinta tana jin kamar ace babu aure kan mamanta ta sake had'a aurensu, ba wai sai iyayenka sun mutu ba wani lokacin kake zama maraya, su kansu akwai abubuwa dayawa wanda sukayi musu manquΓ© musamman daga mahaifi, lallai Ummy ta kai su kirata uwa dan ta musu abinda ta cancanci hakan, amma duk da haka uwa uwa ce, ko hakk'in rayuwa a cikinta kad'ai ya ishi d'awainiya dasu.

Sallamarshi tasa ta gyara zamanta ta tank'washe k'afafu ta matsa daf da k'afafun mahaifinta, yaran duk wurin Gambo suka nufa ya sumbaci kowane kafin yace suje sama suyi wasa zai zo ya ba kowa tsarabarsa, saida suka haye sannan Hajia ta kalli kowa tace "Abinda yasa na tara mu anan dama akan maganar yaran nan ne."

Yanda ta k'arashe maganar da nuna Ammar da Hamna da hannu yasa su k'ura mata ido, dukansu kallo ne suke mata suna tunanin hannun da zasu iya begeta dashi daga lokacin data tona musu asiri, ba tare data damu da kallon da suke mata ba tace "A gani na tunda Hamna har yanzu bata da wani tsayayye me zai hana mu had'asu aure da Ammar?"

Kallon kallo aka shiga yi sai dai wasu na su kallon farin ciki da al'ajabain maganar ne, Ammar Hamna kuma a d'an birkice suka fahimci abun, Gambo ne yace "Masha Allah, gaskiya Hajia wannan tunani ne mai kyau."

Hadiza ma murmushi tayi tace "Gaskiya ne, Allah ya tabbatar mana da alkairi."

Lieutenant da fuskarsa ke had'e yana kallon Ammar ne yace "Amma Hajia ina ga da an ji ta bakinsu, tunda shi yayi rayuwar auren nan yasan komai dake cikinta, ita kuma bata tab'a ba dan haka da an tambaye su aji idan hakan ya musu."

Husseina ce tace "Hakane kuma, tunda babu yaro a cikinsu da za'a ma tilas."

Hajia ce ta kalli Hamna tace "Hamna kinji abinda aka ce, Me ye ra'ayinki? Ki fad'a mana abinda ke ranki dan ba za'a miki tilas ba."

Daram! Gabansu ya fad'i a tare, kallon juna sukayi kowa da abinda yake sak'awa a ranshi, Hamna a ganinta ba zata iya zama da tsohon mijin yer uwarta ba, taya ma zata iya auren yar uwarta saboda ta mutu? Mijin ma kuma Ammar wanda zata iya rantsewa da Allah ba zasu tab'a zama lafiya ba kamar yanda suka zauna da yer uwarta, gaskiya ba zata iya ba sai dai suyi hak'uri. Kallon da yake mata kallon son gane abinda ke ranta ne, bakinta yake kallo yana mai matuk'ar zak'uwa da son jin kalamanta, sanda kanta tayi k'asa tana wasa da yatsunta na hannu, Hadiza ce ta kalli fuskarta tace "Hamna kiyi magana mana, duka anan babu bak'onki."

Husseina ce tayi murmushi tace "Ai mace kunya ne da ita, shirun kuma shi ya bamu amsar tambayarmu."

Da sauri Hamna ta d'ago ta kalleta tace "A'a Hajia, gaskiya ni ina da saurayi, yanzu ma ni yake jira na bashi dama ya gabatar da kanshi."

Tana fad'a ta d'an kalle shi, da sauri ta d'auke idonta, ba zata iya yarda ta k'ara kallonshi ba, wannan kallon babu alamar arzik'i a ciki. Hajia da bata ji dad'in abinda ta fad'a bane tace "Amma Hamn..."

Ammar bai jira me zata ce ba yayi saurin cewa "Nima haka, ina da wacce nake so."

Ko da ya fad'a ya mik'e tsaye ya juya zai fita Gambo yace "Ammar dawo ka zauna."

Juyowa yayi cike da girmamawa yace "Dan Allah tonton, zan gabatar muku da ita nan da lokaci k'ank'ani."

Juyawa yayi ya fice ita ma a hankali ta mik'e zata shiga d'akinta, duk sai taji jikinta yayi sanyi da yace wai yana da wacce yake so, lallai ma mutumin nan! Kenan har ya manta da yer uwarta a wata shida kacal ya fara son wata? Tsaki tayi a zuciyarta tana fad'in "Allah ya tsine mata ma."

πŸ€” *Wacece?*

Gambo ne ya katse mata tunaninta da tafiyarta ta hanyar fad'in "Ke."

Juyowa tayi ta dawo ta durk'usa gabanshi, cikin kakkausar murya da gargad'i yace "Tunda kince baki son d'an uwanki to ki turo mana wanda kika ce d'in, yau d'in nan ba zan bar garin nan ba sai nayi magana dashi."

A mugun tsorace ta kalleshi, me kenan ta jawo ma kanta? Ita fa ta fad'a ne dan abar maganar shi, amma bata da wani tsayayye yanzu ita in banda 'yan abi yarima asha kid'a, yanda ta kakkafeshi da idonta babu ko k'yabtawa yasa shi daka mata tsawa cikin jin haushi yace "Tashi ki bani wuri, kina girma kina cin k'asa har yanzu kin kasa sanin ciwon kanki."

Saida ta juya zata tafi taji wasu hawaye sun taho mata, bata san abunyi ba a yanzun gaskiya, Hadiza ma da bata ji dad'in k'in amincewarta ba tashi tayi tana fad'in "Kuyi hak'uri dan Allah zanyi magana da ita."

"Dawo zauna Hadiza." Cewar Hajia, komawa tayi ta zauna tana kallon Hajiar da tace "Watak'ila tana da dalilinta na k'in amincewa, karku matsa mata dan Allah ku barta ta zab'arwa kanta abinda take so."

Gambo ne yace "Amma Hajia ko ma menene dalilinta ai bata k'i d'an uwanta ba, ko dan marayunshi ai zata amince."

A hankali Hajia ta kalli lieutenant ta kuma kalli Husseina, kallon Gambo da Hadiza tayi tace "Magana ta gaskiya bai kamata mu ci gaba da b'oye muku ba, ku kuka haifi abarku ya kamata kusan komai dake faruwa kan 'yarku."

Gaban Hadiza ne ya sake fad'uwa dan ita tun farko tayi tsammanin jin wani mummunan abu, kallonta suke sosai kafin ta gyara zama tana fuskantarsu da kyau tace "Kuyi hak'uri dan Allah ku yafe mana dukanmu, sannan zan so ku nutsuwa kuyi duba na tsanake akan lamarin, karku yanke hukunci cikin hushi, hakan zai iya janwo mana dana sani."

Shiru tayo sai Hadiza da tace "Hajia ko me ya faru bai kamata ace kina neman afuwarmu ba, mu 'ya'yanki ne baki buk'atar wannan."

Gambo ne yace "Hakane, koma menene Hajia ai ba sai kin rok'e mu ba."

Numfasawa tayi cike da muryar rarrashi da nuna nadama tace "Shekara biyar da rabi kenan da wata mummunar k'addara ta fad'a kan Hamna, idan kaji ance tsautsayi to akwai ganganci a ciki, shi yasa na ce muku k'addara dan ku fahimta da kyau, k'addarar data tashi fad'a mata ma sai ta fito daga ruhin d'an uwanta Ammar, bayan abinda ya faru ya faru ciki ya shiga jikinta, hakan kuma ya tabbatar mana da lallai wannan abun daya faru rabon wannan yaron ne, dan da wani yayi k'ok'arin shiga tsakanin faruwar wannan al'amari, ko shakka babu wannan rabon zai iya ajalinshi, *Shureim*, shine yaron wanda Sa'ada a matsayinta na uwar yarinyar da kuma yaron tayi k'ok'arin b'oye wannan laifin dan kar mutumcin yaranta ya zube a idon duniya, bata so 'yarta ta rasa kimarta ta 'ya mace, ta d'auki zunubin da hannu bibbiyu ta d'ora akanta, tayi mana k'arya duk dan ta kare mutuncinsu, ta yaudari mijinta dan ta tseratar dasu a matsayinta na uwa, ta nuna mana zata iya yin komai akan 'ya'yanta, tabbas laifi ta aikata amma fa a dalilin soyayyar da take wa yaranta, muyi k'ok'ari mu fahimceta dan Allah, uwa takan iya yin komai ta kan iya tarar kowane bala'i saboda yaranta."

Ajiyar zuciya tayi tace "Da wannan nake nema mata alfarma a wajenku dan Allah ku yafe mata, kuma iyayen yaran nan ne, ku kamalta da idan kune abun ya faru a idonku me zakuyi? Nasan ko baki abinda tayi ba zakuyi makamancin shi."

Tirk'ashi! Yanzu abinda ya faru kenan da 'yarsu da kuma d'an su? Tambayar da suka ma kansu kenan? Sai dai Hajia ta gama sage musu gwiwa, ta gama dasu tunda tace k'addara, babu wanda ke kauce mata inda ta tashi fad'a masa, sannan ta k'ara d'auresu da tace tana nema mata alfarmarsu, uwa ce ita gare su sannan Ummy ta rik'e yaran kamar ita ta haifesu a cikinta, sun gamsu ba tayi haka bane dan ba ita ta haifeta ba, sai dai su ce kawai k'addarar da kuma sharrin shaid'an, bugu da k'ari ma abun ba yanzu ne ya faru ba, shekaru har biyar to wane fad'a zasuyi kuma da dama ya wuce suyi hak'urin? Cikin jinjina al'amarin Gambo ya kalli Hadiza ya kuma kalli lieutenant yace "Abinda ya shiga tsakaninku kenan har kuka samu sab'ani da matar da baku tab'a sab'awa ba?"

Ajiyar zuciya lieutenant ya sauke yace "Gaskiya raina ya b'ace sosai, matata uwar yarana ta ha'ince ni har haka? Mtsss."

Hadiza ma data gama sawa zuciyarta ruwan sanyi ta yanke hukunci taushe komai ta had'iye ya zama sakayyar da zata musu na kula da yaranta da sukayi ta kalle shi tace "Abban Ammar, dan Allah muna nema mata alfarma kayi hak'uri ka dawo da ita, tayi hakane saboda 'ya'yanka, idan zaka nutsu kayi tunani zaka fahimci da a lokacin kowa yasan abinda ya faru, kayi tunanin irin abinda zai faru marar kyau, sannan kayi duba da shekarun da kuka d'auka ba tare da kun samu sab'ani irin haka ba, kayi hak'uri dan Allah, mu ma wallahi mun yafe babu komai, Allah ya yafe mana baki d'aya."

Gambo ne ya kalle shi yace "Ku daina bashi hak'uri ma dan Allah, yanzu zai tura dreba ya d'aukota ya dawo da ita."

Wani kallon ban son iskanci lieutenant ya mishi, shi ma hararanshi yayi yace "Allah sai kayi ko baka so, ba dan ma raini ba matar taka ta shekaru zaka yarda ta bar gidanta a wannan lokacin, to ina kake so taje? Ko kunya abun ba zai baka ba ace ta tafi gidansu, da yaranku da jikoki ku tsaya kuna abu kamar yara."

Had'e fuska yayi yace "Gambo, kayi shiru da bakinka kafin ranka ya b'ace."

Shi ma ba alamar wasa yace "Ya b'ace d'in mana, an fad'a maka ina jin tsoro ne."

Tasowa lieutenant yana fad'in "Zan tosheka kuwa yaro."

Da sauri Gambo ya tashi yayi baya yana dariya yana cewa "Ni ne yaron? Ni kake kalla ka kira ni yaro? Haba."

Hajia ce tace "Karka tab'a min auta wallahi, inba haka ba ranka zai b'ace."

Dawowa Lieutenant yayi ya zauna yana murmushi, Hadiza kam banda k'yalk'yata dariya ba abinda take, komawa yayi shi ma ya zauna yana dariya, Hajia ce tace "Dole zaka tura a d'aukota, kuma ba dreba kad'ai nake so ba, har da kai ma zaka tafi."

Kallonta yayi yace "Haj..." Bata barshi ya k'arasa ba tace "Bana son jin wata magana, abinda ka mata zaisa taji kamar ba a bakin komai take a wurinka ba, ba zan lamunci haka ba gaskiya, matar data k'arar da shekarun rayuwarta a tare damu, ta maka biyayya ni kuma ta min bauta, haka kawai yau ka wulak'anta ta."

Cikin marairaicewa yace "Shikenan Hajia zan tafi, amma ki min uzuri dan Allah har zuwa gobe, wallahi yau ina da muhimmin aiki a gaba sosai."

Fuska a d'aure tace "Shikenan, kaje Allah ya bada sa'a."

Da farin ciki ya amsa da "Ameen nagode."

Tashi yayi ya kallesu yace "Sai anjima."

Husseina ve tace "Allah ya tsare."

Sada ya fita Gambo ma yace zai fita ya dawo kafin Hadiza ta shiga d'aki ta samu Hamna, kwance ta same ta gefenta farantin kankana amma da alama bata sha ba, zaune tayi tana kallonta tace "Tashi zaune zamuyi magana."

Cikin muryar kuka tace "Dan Allah Mama in akan maganar nan ne kawai ki barta, ba zan iya ba wallahi."

Ajiyar zuciya ta sauke tace "Tashi Hamna, c'est très important."

Tashi tayi ta zauna tana ci gaba da share hawaye kuma wasu na bin wasu, kallon basira ta mata kallon fahimta tace "Hamna, me yasa kika ce ba zaki iya auren Ammar ba?"

Da sauri tace "Mama je ne peut pas, ba zan iya auren mijin yer uwata ba, kuma ni bana son shi ko kad'an."

Saida ta karanci yanayinta kafin tace "Corrections, mijin yer uwarki data rasu zaki ce, sannan Hamna zaki iya aurenshi ko da baki son shi, kinsan me yasa?"

Da ido ta kalleta hakan yasa tace "Saboda shine uban d'anki Shureim."

Da fari zaro ido tayi tana kallonta a firgice, sai kuma ta fad'a kan k'afafunta tana kuka tace "Mama kiyi hak'uri ki yafe min dan Allah, wallahi ba laifi na bane shine ya tirsasa ni, Mama bana manta tunatarwarki a kanmu kullum, dan Allah kiyi hak'uri."

D'agota tana share mata hawaye tana ji kamar tayi kukan ita ma tace "Karki sani kuka Hamna, na riga dana yafe miki har da shi ma, bana so ki karyar min da zuciya kuma."

Sassautan kukan tayi sai ita data d'ora da cewa "Hamna a gani na ki amince da auren shi, sai nake gani kamar ba zaki samu wanda zai dace dake ba kamar shi, sannan Hamna duk wanda zai fito neman aurenki yanzu ya zama dole a sanar dashi kina da yaro, kina ganin zai amince ya aureki duk yanda yake son ki? Ba lallai bane gaskiya a wannan yanayin da ake ciki, amma kinga shi ba zai k'yamace ki ba, zai rik'e ki kuma ya rik'e d'anku hankali kwance."

Girgiza kai tayi tace "Mama zan samu amma ba dai Ammar ba, mutumin daya rabani da mutumci ne yaushe zan iya rayuwar aure dashi? Kuma shi ma fa kinji abinda yace yana da wacce yake so, to me zaisa na tusa kaina gare shi."

Murmushi Mama tayi tace "Wallahi baya da wata wacce yake so Hamna, kawai ya fad'a ne saboda kinsan shi ba rainin wayo yake so ba, nasan yanzu yana can yana bala'i kin kalle shi kince baki son shi."

Kallonta Hamna tayi tace "Mama kawai ko bar maganarshi, ni idan ma ban samu mijin aure ba zan zauna na ci gaba da kulawa da yara na."

Da sauri tace "To ba gashi ba, Hamna kina son yaran nan sosai kuma kin k'i yarda kowa ya kama miki kula dasu, indai kina son ki ci gaba da rayuwa da su dole ki auri mahaifinsu, amma ba zan takura miki ba ki zauna kiyi tunani sosai, duk abinda kika yanke ki kira ni ki fad'a min."

Tashi tayi zata fita tace "Mama ina zaki je."

Juyowa tayi tace "Zan je gida na dawo na d'auki Ahmad."

Fkta tayi inda Hamna ta shiga d'aukar kankanarta da d'aya d'aya tana sha tana kuma tunanin abinda Mama ta fad'a, lallai indai zata rayu da yaran da ko kukansu bata so dole ta bi shawarar Mama, amma kuma Ammar? Kai! Tana cikin wannan tunani wayarta ta shiga k'ara, d'auka tayi ta ga ko suna babu a lambar, d'auka tayi suka gaisa kafin ta tambaya wake magana, nan ya fad'a mata sunanshi tace bata gane ba, dan haka yace ta bashi izini ya zo zai ta ganshi ido da ido, burinta na son samun wanda ya dace yasa ta amince da ya zo anjima.

*Tsautsayi*

Bayan sallah isha'i ta gama shirinta cikin doguwar rigar shadda, duk da ba tayi kwalliya ba amma tayi kyau, wayarta ya kira ya shida mata ya zo, ko da ta aje wayar Imam ya shigo yana kuka wai Shureim ya dake shi, jawo shi tayi tana lallab'a shi ta bashi wayarta tace "Ka je kayi kallon abinda ka fi so karka bawa kowa, kuma zan ga Shureim d'in saiya gane kurensa."

Cikin jin dad'i ya karb'a ya fita, ita kuma saida ta shafa turare sannan ta d'auki gyale ta yafa tasa takalmi ta fito, su Zeinabu ta samu a falo ta fad'a musu tayi bak'o a waje zata shigo dashi ciki, fatan alkairi suka mata ta fice.

Tana fita ta shiga mamakin wanda ta gani, kusa da salon d'inta yake nan take ganinshi zaune a wata fada, da mamaki tace "Kai ne?"

Murmushi yayi "Kin gane ni ashe? Na d'auka yanzu ma saina kwatanta miki."

D'an murmushi tayi tace "Na gane ka mana."

Gyara tsayuwa yayi yace "To ya kike?"

"Lafiya lau, mu shiga ciki ko, ba'a barinmu tsayawa kan hanya."

Gabanshi ne yaji ya fad'i sosai, tambaya ya wa kanshi to me ya kai na shiga ciki? Shi fa ba wata babbar magana bace ta kawo shi wajenta. Murmushin yak'e ya mata yace "Amma kafin nan mu gaisa ki san suna na, in ya so sai mu shiga ko."

"Amma ai duk zamu iya yi a ciki." Ta fad'a fuskarta a d'an had'e, kallonta yayi yace "Hakane, amma in d'an jin tsoro."

Wani irin kallo ta masa tace "Tsoron me kuma?"

Cikin rashin gaskiya yace "Eh to, kin gane? Kawai dai, gidan na ku ne, nasan mutanen cikinshi, akwai abokaina dayawa."

Wani kallo ta masa zatayi magana Imam ya fito daga cikin gidan da gudu yana kuka, tana ganinshi ta durk'usa ta rik'eshi tana fad'in "Imam me ye? Waya tab'a ka?"

Kafin yayi magana Shureim ya fito da wayarta a hannu ya zo ya tsaya yana fad'in "Aunty wai dan na ce ya bani nayi jeux (game) shine ya k'i."

Ranta a b'ace ta kalle shi tace "Shine ka fizga da k'arfi?"

Mik'ewa tayi tsaye ta kamo kunnenshi ta kwad'a masa mari tana fad'in "Shine zaka saka min yaro kuka? Dan ubanka ban hana ka tab'a min su? Wallahi ka sake karb'ar min a waya a hannun sai na ci ubanka a garin nan."

πŸ˜‚ *Hamna kin taro match fa, da kin duba bayanki kafin ki fad'i haka.*

*Ammar* da saida ya kusa kawowa gida motarsa ta tsaya, makanikenshi ya kira shi kuma ya k'araso k'asa saboda tafiyar ma na da anfani ga lafiya, tunda ya hangeta ya ganeta, k'ara hassala yayi dama a tafashe ya fita daga gidan, har yanzu yana nanata kalmar data fad'a ta *ina da saurayi*, ya rasa dalilin da yasa Hamna ta soka mishi wannan iskancin, a gaban iyayensu tace tana da saurayi kuma bata son auren shi. Sannan yazu ya dawo ya tarar da ita da saurayi a k'ofar gida tana hukunta masa yaro, wannan wace irin uk'uba ce? Bayan ta gaura masa mari kuma ta bishi da zagi, zagin ma ubanshi kawai take zaga, wato dan ta ga wani d'an iska a gabanta shine zata tsaya tana zaginshi, tunda dai ta zagi yaronshi ai da shi take.

Amma ba damuwa zaiyi maganin saurayin kafin ita, shi daya zauna yana kallo yana jin dad'i tana zagar masa yaro amma bai hanata ba, dan baisan darajar 'ya'ya ba saboda bai da su shi, da azama ya k'araso wajen ta bayansu ba tare da sun san da zuwanshi ba, saida ya tsaya da kyau ya toge sosai yasa k'afarsa ta dama a gaban k'afafun saurayin nan da ko sunanshi Hamna bata sani ba bare ta fad'a mana ya kwashi k'afafunsa.

Sai ji tayi kawai abu ya fad'i k'asa pamm, da sauri ta saki Shureim ta juya ta kalli ikon Rabb, bawan Allah bai san me ya faru ba, baisan wane shaid'anin bane a cikin shaid'anun, abinda ya sani kawai shine a cikin aljannun ma wannan gagararre ne, duk yanda akayi ko dai a gidansa ne suke tsaye ko kuma sun taka masa yara basu sani ba, amma wannan kwasa da aka masa ko jirgin sama yana shaida maka zai tashi ya d'aga ka daga kan k'afafunka bare kuma bil'adama.

Yana shirin bud'e idonshi daga k'asar da fuskarshi ta daduma yaji an tokara masa gwiwar k'afa a baya an hana shi tashi, bai yarda yayi gamo ba saida yaji an figi hannunshi ta baya anyi ciri dashi, yana jin sautin k'arar gotawar k'ashin shi sanda aka karya hannunshi, azaba ce tasa shi sakin k'arfinshi ya daka uwar ihu.

Yana jin k'ararshi ya sake cije leb'e yana fad'in "Au! Zaka iya ihu ashe."

Tsakiyar kanshi ya dafe ya rik'e hab'arshi da d'aya hannu da niyyar kawai ya juyar masa da wuya, an jima uban kowa bai mutu ba, Hamna data shiga firgici na abinda zai aikata bata san sanda ta rumgume shi ta baya ba ta rik'e hannayenshi gam ta fashe da kuka tana fad'in "Dan Allah Ammar sake shi baiyi komai ba, dan Allah karka kashe shi ka rufa mana asiri."

K'arfin tartsatsin da yaji kamar k'arfin dake cikin wutar lantarki ne, ba wai tsayawa ba daga masifa, hatta numfashin shi ma ta kusa sawa ya bar jikinsa, har jikinshi ma ya shida ita ta musamman ce, sannan dokinshi ma ya tabbatar da yana kewar mace, dan a take sak'on yaje ya kuma haifar da sakamako mai kyau. Sakinshi yayi tare da mik'ewa tsaye yana kallon mutumin, shi fa ko fuskarshi ba bai gani ba, tsabar fitina ce kawai da neman wanda za'a mutu tare, sai lokacin ta sake shi tana k'ok'arin su kalli juna sai kawai ya taka da sauri yaja hannun Imam da Shureim wanda dukansu sukayi shiru da kukansu suna kallon babbar harka, cikin gida ya shige dasu.

Cikin jin kunya ta kalleshi ya tashi zaune yana karkad'e k'asa a fuskarshi yana furzar data bakinshi, a hankali cikin taushin murya tace "Dan Allah kayi hak'uri kaji, kayi hak'uri da abinda ya maka, yayana ne."

Shi dai da har yanzu bai gama gane komai ba ga hannunshi dake zugin bala'i na karaya ko kallonta baiyi
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment