Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

wannan fa."

Tab'e baki tayi tace "Dan ka rabu dani? To autan maza ne kai da zanyi bak'in cikin rabuwa da kai, kaga malam ka tambayi mahaifiyarka ta fad'a maka yanda komai ya faru, karka tsaya kana zare min ido."

Malam ta kalla tace "Malam mu tafi, zasuji da matsalarsu."

Tashi yayi yana waiwayen Husseina da shi dai yake son neman yafiyarta, suna fita colonel da lieutenant suka shigo tare da Alhaji cikin farin ciki, suna ganin yanayin mutanen wurin kowa yayi sororo ga Junaid yasa Zeinabu gaba yana magana k'asa k'asa yasa lieutenant k'arasawa da sauri wurin Hajia yace "Hajia lafiya? Meya faru duk na ganku haka?"

Colonel ma matsawa yayi kusanta yana karantar tsantsan tashin hankali daka fuskarta yace "Hajia lafiya?"

Dab'as ta zauna kan kujerar da kullum take jin dad'in zama kanta cikin isa da izza, duk yanda numfashinta ya fara barin gangar jikinta saida tayi k'arfin halin kallonshi cikin fitar da numfashi sama sama tace "Husseini..da gaske...ne.Ju...Junaid baaaa..."

Kasa k'arasawa tayi wanda hakan yasa colonel sunkuyar da kai, *wal'iyazu billah* shine abinda ya fad'a ร  ransa, kamar an jonata da kuran sai kawai ta tashi tsaye da k'arfinta, hannu ta d'aga sama da niyyar palla masa mari, sai kawai jikinta ya d'auki b'ari hannunta ya fara rawa da k'arfi kamar ta kama wayar lantarki, lieutenant da colonel d'in ne sukayi azamar rumgumata a jikinsu cikin tashin hankali lieutenant "Mu kaita mota."

Da gudu Zeituna ta k'araso tana k'ok'arin rik'eta tace "Ku saketa zamu kamata."

Soueiba ce ta taso da sauri suka kamata su kuma suka nufi mota, ana fita da ita sai asibiti wajen su Ammar, ganinsu ya d'aga musu hankali suma ba kad'an ba, Ammar da Ummy da kuma wata malamar asibiti ne suka rufa kan Hajia aka fara k'ok'arin ceto ranta.


*Awa biyu* suka d'auka kafin su fito fad'a musu halin da take ciki, Hajia kam dai...


*Alhamdulillah*
14/10/2020 ร  00:58 - Ummulkhairi: ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ
*BADAK'ALA*
๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ

*Labarin Gaske*

*NA*

_SAMIRA HAROUNA_

*Litattafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._

*SADAUKARWA GA*

๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ _*AHALI NA*_๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

๐Ÿ’ซโœจ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*๐ŸŒŸ
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_๐Ÿค

โ˜† *[ T.M.N.A]* โ˜† ๐Ÿ“–๐Ÿ–Š๏ธ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_

_49_

Ammar ne yace "Cikin sarautar Allah komai ya daidaita, jininta ne ya hau sosai, amma yanzu mun samu mun shawo kan lamarin, ba wata bazarana a yanzu zaku iya komawa da ita gida, akwai magunan da za'a bata ta samu bacci."

Alhaji ne yace "Ammar kana ganin zamu iya tafiya da ita gida tun yanzu? Me zai hana ba zaku barta nan ba ta samu ta huta."

Dafa shi yayi yace "Ba komai Alhaji zaku iya tafiya da ita, kuma ko da wani abu ya faru ma ba gani ba duk da bama fatan haka."

Sallamarta sukayi tare da Jamila ita ma amma sun rigasu tafiya, ko da aka je gida d'akinta suka kaita aka bata magani tasha, ba jimawa bacci ya d'auketa idonta na kan colonel da take matuk'ar son marin fuskarshi, suna ganin bacci ya d'auketa kowa ya sauke ajiyar zuciya, a tsanake Alhaji ya kalleshi yace "Husseini shin gaskiya ne abinda aka fad'a d'in?"

A hankali ya sulale ya durk'usa gabanshi duk da babu hawaye a idonshi amma muryarshi na rawa yace "Alhaji kuyi hak'uri ku gafarceni, kuskure na wallahi, hakan ya faru tun kafin a d'aura aurenmu, ta so na fad'a asan halin da ake ciki amma, Alhaji ina jin tsoron Hajia sosai, tsoron abinda zatayi yasa muke b'oye wannan sirrin har wannan lokacin, amma wallahi kullum da fargaban hakan muke kwana kuma muke tashi."

Ajiyar zuciya Alhaji ya sauke ya kamo shi ya tashi, kallon idonshi yayi yace "Husseini, ba'a gyara kuskure da kuskure, shiru ba shine mafita ba illa ma ya k'ara haifar da wata matsala, na so ace a lokacin ko ni ka tuntub'a da lamarin dan asan abunyi, abinda kukayi kuskure ne, kuskurenku ma akan kuskure kukayi shi, yanzu kaga me hakan ya haifar? Shi yaron da wane ido zai kalleku?"

A hankali ya d'aga kai ya kalli Junaid dake gefenshi, Zeinabu dama bata tafi asibiti ba saboda tafi Hajia ma shiga tashin hankali, kawai ita nata ya fito fili ne aka gani, k'yar kam idonshi cikin na shi, kallon babu wanda yasan na miye ma kawai suna kallon juna ne, cike da dattako Alhaji ya kallesu dukansu yace "Yanzu dai tunda haka ta faru kawai komai ya wuce, Junaid hak'uri zakayi wannan ita ce jarabawarka, kai kuma kai da ita sai kuyita istigfari wajen ubangiji, abun kuma a bud'e yake cewa yanzu shi ma magajinka bane."

Saida ya sunkuyar da kai yace "Allah ya kyauta ya kuma kiyaye gaba."

Saida ya goya hannayenshi baya ya fara tafiya ya fita daga d'akin, da sauri Junaid ya bi bayanshi da alama kuka ya fashe dashi, ajiyar zuciya lieutenant ya sake saukewa mai k'arfi, shima fita yayi tare da Ummy data baro asibitin suka taho tare.

Ko da aka dawo Jamila tace a mata shinfid'a a d'akinsu na yan mata, a lokacin babu wanda ya kula saboda duk jikin kowa yayi sanyi *gwamnatin* gidan babu lafiya, ga kuma zulumin abinda ya faru da mamakin al'amarin, can aka gyara mata ta zauna ita da jinjirinta, basu kula ba saida Jibril ya zo yana tambayar inda take kad'ai aka gano, Soueiba da Husseina ne sukayi ta bata baki amma ta rufe ido ta botsare tace ita fa ta gama zaman gidan shi, k'yaleta sukayi da tunanin idan ta huce sai a mata magana ta koma. Tunda Zeinabu ta shiga d'aki ta kasa fitowa sai dai colonel ya shiga kawai ya fito, sai kuma Zeituna dake kai mata abinci ta aje ta fito. Haka kuma ita ke kula da Hajia tunda ta farka da la'asar, da taimakonta tayi alwala tayi sallah, da hannunta ta bata abinci tasha magani.

Bayan sallah magriba lieutenant ya shirya cikin kakin shi ya fita, oda ya bayar tare da rahoto akan motar cewa a dakatar da ita, kafin a sanar dashi ganin motar wasu abubuwan ya shiga yi, sai misalin *11:40* aka kirashi aka fad'a mishi ga motara hannu d'auke da kaya, nan yayi umarni aka taho da ita har ofishinsu inda ya fito da kanshi bayan anshiga da ita ciki, saida ya gama kallonta ya ga sak kwatancen da Ammar ne ya masa, nan yasa yaransa suka bud'e motar aka fara fito da kayan ciki, dreban na gani ya fara fad'in "Ba fa komai bane yallab'ai, indomie indomie ce sai madara."

Wani kallo lieutenant ya masa yace "Ka bari to mu gani da kanmu."

Pilla pilla lieutenant yasa aka ma kayan nan, sai gashi karton d'in da ake tunanin indomie ce ciki da kwalayan madara an samu tramol a ciki, haba ai sai hankalin dreba ya tashi dan baisan abinda ya d'auko ba, mai kayan aka sa shi ya kira sai ga Jano ya zo ya d'auka kamar yanda aka saba ne, idan aka rik'e kayan ko kuma aka musu awo a caji kud'i masu yawa, sam basu sarara masa ba hannun jami'an tsaro suka mik'ashi tare da dreban, sai dai shi daya rantse baisan menene ba kuma ya fad'i yanda akayi ma har ya d'auko kayan sai suka gamsu, musamman da shi kanshi Jano d'in ya tabbatar musu da babu ruwan dreban, shi ma kuma cewa yayi ba kayan sa bane, abu dai yaja daga an sake dreba Jano kuma yau gashi da kwanan magark'ama.

Da dare tana zaune ita kad'ai a d'akin ta had'e fuska, tunani take irin matakin ma da zata d'auka na wannan cin zarafi da Husseini ya mata, ita zai kunyarta ya wulak'anta a idon duniya, tana kalkad'a k'afa alamar masifa Zeituna ta bud'a k'ofar ta shigo da sallama, saida ta zo har ta aje kwanukan abincin zata fara zuba mata tace "Dakata malama bana so, fice min a d'aki."

Da ladabi ta kalleta tace "Hajia lokacin shan maganinki yayi fa."

"Nace bana so ki fitar min a d'aki." Sake k'asa tayi da muryarta tace "Dan Allah Hajia ki daure..."

Tsaye ta mik'e ta nuna mata k'ofa tana fad'in "Nace ki fita ko, ko saina sa an fitar min dake ne?"

Juyawa tayi cikin sauri sauri ta fita, da harara ta bita duk sai take jin haushin matan ma, kawai ita bata yarda dasu ba, dan haka sai kowace ta fito mata da d'an da ba jininta ba, inba haka ba duk saita kaisu asibiti an gwada uban kowa dan tasan yaran da suka ciyar a banza. Tana cikin safa da marwa Ammar ya shigo da siririyar sallama, tana juyowa ta ganshi ranta ya sake b'acewa tace "Fitar min a d'aki kaji, bana son kowa ya sake shigo min d'aki ina buk'atar zama ni kad'ai."

Rufe k'ofar yayi ya tako da sauri yana fad'in "Hajia ta nayi kewarki fa."

Cakumota yayi ya rumgume da k'arfi yace "Kin tsoratani fa sosai, ban tab'a yarda cewa ana jin k'amshin lahira ba sai yau dana kusa rasaki."

Tureshi tayi daga jikinta cikin tsawa tace "Kana hauka ne? Ammar fice min a d'aki kafin ranka ya b'ace."

Hannunta ya kamo ya zaunar da ita bakin gadon ya fara zuba abincin yana fad'in "Ba zan yarda ki sake min wasa da lafiyarki ba, Hajia dole sai kinci abinci kafin kisha magani, inba haka ba zansa Alhaji ya rik'e min ke mu miki d'ure."

Zaune yayi bayan ya gama zubawa ya d'ebo a cokali ya kai bakinta, k'ank'ance idonta tayi tace "Baka da hankali ne Ammar?"

Kai ya d'aga mata yace "Eh Hajia ta, akan ki mahaukaci ne ni."

"Shin baka fahimtar abinda nake fad'a maka ne?"

Saida ya turo baki yace "Ai ba zan fahimta ba har abada."

Cike da k'aguwa tace "Akan me to zaka nuna ka damu dani bayan nasan ba so na kake ba kamar yanda bana sonka?"

Murmushi ya mata yace "Saboda bana so na rasaki."

Kallon idonshi tayi tace "K'arya kake Ammar, nasan zaka fi kowa murna idan na mutu."

"A'a Hajia, zanfi kowa bak'in ciki." Ya fad'a shima yana kallon k'wayar idonta, cikin taushin murya tace "Me yasa?"

Ba tare daya d'auke idonshi ba yace "Saboda zanyi kewar masifarki, zanfi kowa damuwa na rasa babbar mai yi min fad'a da zagina da kuma yanke hukunci akaina ba tare da shakku ko shawartata ba."

Me Hajia zatayi ba dariya ba, ita kanta ji tayi ta taho mata, bata san me yaron nan yake ji dashi ba da har yake iya tunkararta ya fad'a mata abinda ke ranshi ba tare da shakku ba, ita yake kallon idonta yake fad'a mata wai zaiyi kewar *masifarta*, ba tare data tsagaita da dariyar ba tace "Ammar kai mahaukaci ne."

Yana kallonta yace "Na sani Hajia, haka kuke fad'a kullum."

Lomar ya mik'o mata sai kawai ta harareshi tace "Ban ci nace ko."

Langab'e kai yayi yace "Hajia jan ajin ya isa haka mana."

Wata dariyar ta sakeyi ta kamo hannunshi ta zura lomar bakinta, kallon bakinta yake yanda take tauna abincin yasa yake hango k'uruciyarta, abun mamaki shine karb'an abincin da Hajia ta dinga yi daga hannun Ammar kai kace dama can haka suke, shi kanshi sai yake jin abun na daban bai saba ba, duk da bata ci sosai ba haka ya aje ya bata magani tasha, tana sauke kofin daga bakinta ta kalleshi, haka kawai taji kamar kunyarshi na son lullub'eta ba gaira a dalili, aje kofin tayi a hankali ta d'ora goshinta kan gwiwarshi ta sauke ajiyar zuciya tace "Ammar kaga abinda kawunka ya min ko? Kaga irin k'ask'ancin daya ja min? Kana ganin irin tozarci da zubar da mutumcin daya min? Wane irin mataki ne zai d'auka akan shi? Akan me zasuyi min haka saboda kawai ina son kare iyalina."

Cikin murmushi ya k'ara jawo kanta saman cinyarshi yana wasa da yatsun hannunta yace "Hajia na fahimci duk k'ok'arinki na son karemu ne daga aikata abinda bai dace ba, amma kuma tsananin da kikayi ne yasa iyalinki ke matuk'ar tsoronki, Hajia idan kana son yaro ya saba da kai ya dinga jin maganarka ba tsanani ke sa haka ba, jawo shi a jiki da wasa da shi da kuma durmiya cikin al'amuranshi, shi ke sa ba mace ba har namiji ya saki jiki da kai yana fad'a maka sirrinsa, Hajia ni baki gani ba har yanzu bana iya wani sirri da mahaifiyata ba, Abba ma yanzu ne kad'ai na fara fad'a masa damuwata, ke ma hakane Hajia ya faru da ke, da ace tun farko kinsa iyayenmu a jikinki kin nuna musu so da k'auna wallahi da sanda abin nan ya faru kawu zai sanar dake ko da yasan ranki zai b'ace, kiyi hak'uri Hajia idan abinda na fad'a ya b'ata miki rai."

D'agowa tayi ta kalleshi ido cikin ido tace "Ammar me kake nufi? Wace irin soyayya ce zai nuna musu da ban nuna musu ita ba?"

Murmushi yayi yace "Hajia kina son 'ya'yanki sosai mana, saboda kin haifesu haihuwa kuma ba wasa bace, matsalar d'aya ita ce ba kya nuna musu soyayyar a zahiri."

Wani dogon tsaki taja ta gyara zamanta tace "Ban gane me kake nufi ba, kawai ka fitar min a d'aki."

Murmushin gefen labb'a ya mata ya mik'e tsaye yana kallonta yace "Zan fita Hajia, amma kiyi tunani akan abinda na fad'a miki, domin kuwa na fi kowa son ganin kan gidan nan ya had'u."

Har ya juya sai kuma ya tsaya ya juyo yace "Ban san ko zaki iya tuna ranar k'arshe da kika tab'a bin iyayenmu da addu'a ba ta alkairi, misali idan sun miki alkairi ko zasu fita aikinsu ko kuma zasuyi balaguro, Hajia ke a ganinki duk abinda suka miki abune dama da yake wajibi akansu dan haka babu buk'atar kiyi musu godiya ko addu'a, Hajia kina ganin kin haifesu kin gama musu komai a rayuwa, dan haka ya zama dole akansu suyi duk abinda kike so, amma kina mantawa da ubangijin daya hallicesu kuma ya halliceki, to Hajia ko ubangiji yana bawa bayinsa wata dama, wannan damar kuwa ita ce talala da yake mana dan mu tuba ga laifikanmu, amma ke..."

Girgiza kai kawai yayi ya fita daga d'akin, da kallo ta bishi da mamaki, to wai akan me yake magana? Soyayya? Addu'a? Jansu a jiki? Tsanani? Tab'e baki kawai tayi ta jinjina kai tace "Dan na saki jiki da kai shine har zaka fad'a min magana."

Zaune suke a falon sama suna hirar da babu nishad'i a ciki sakamakon abinda ya faru, Zeinabu ma ko fitowa ba tayi ba bare ta gansu taji kunya, Hamna na gefe d'aya k'asan carpet ta mik'e k'afafu, Shureim ma na nesa dasu saboda k'arfin pankar da suka kunna saboda guje mishi kamuwa da mura, motsawa yayi tare da fashewa da kukan daya shiga duka kunnuwan iyayen nashi biyu, autar Soueiba *Basira* ce tayi karanbanin rugansu d'aukoshi, yanda ta d'auko shi ba daidai ba yasa Hamna zabura daga zaman da take da gudu har tana take rigarta ta nufeta, tana zuwa ta rumgoshi jikinta ta karb'eshi tana kallon Basira tace "Uban wa yace ki d'aukeshi, sai kin ji masa ciwo hankalinki zai kwanta, baki ga jikinsa baiyi k'wari bane da zai juri wannan wahalar."

Tsaki tayi cike da jin haushi har zuciyarta ta juyo da niyyar zaunawa, saida ta zabura ganin Ummy ita ma ta taso a bayanta tsaye tana kallonta, wani kallo ta mata mai cike da gargad'i sannan ta karb'eshi ta koma ta zauna, gabanta fad'uwa kawai yake tana satar kallon su Soueiba da Zeituna, su dai abun ya basu mamaki na saurin zaburar da tayi kamar daga cikinta d'an ya fito, amma bayan haka basuyi tunanin komai ba, Hamna na zaunawa wayarta tayi k'ara, dubawa tayi taga Amna ce, d'auka tayi sai kawai tace "Dan Allah yer uwa ki zo."

Wani iska ta furzar dan ita fa bata so tana kusantar da kanta gare shi, bata so tana ganinshi akai akai wani abu take ji, tabbas kuma ba tsana bace sai dai tana jin haushinshi, kashe wayar kawai tayi ta gyara zaman kallabin doguwar rigarta ta fita.

Tana saukowa ta zo tsakiyar falon shima ya fito daga d'akin Hajia, a tare suka kalli juna da sauri ta d'auke na ta idon ta k'ara sauri dan ta fita, shima kuma cikin takon sauri yake dama shiyasa suna ka kai daf da k'ofar a tare, zata fita ba tare data bari ya wuce ba shine abinda ya bashi haushi, tsayawa yayi ya mata wani irin kallo yace "Wuce uwata."

Wani kallon sama da k'asa ta masa ta fice kam abinta, a baya ya binta yana kallo kuma ita ma can ta nufa, kawai baya jin masifa ne amma da saiya gabza mata mari ko ta koyi girmama shi, tana shiga ta sameta zaune k'asa kamar kullum, jin takonshi a bayanta yasa ta d'aure fuska tace "Me zan miki da kika kirani?"

Turo baki Amna tayi tace "Shikenan fa tunda muka dawo daga asibiti baki zo kika dubani ko ina lafiya ba."

"Akan haka kika kirani?" Gira ta d'aga mata kawai, juyawa tayi tace "Saida safe."

Da kallo kawai ta bita haka shima, zaune yayi kusan Amna yace "Yarinyar can k'uruciya na damunta."

Kallonshi tayi tace "Tana damunta ko tana damun mu?"

Saida ya rumgumota jikinshi yace "Ai ke kin kusa girma da zaran kin fara aje min yara."

*Da safe* Alhaji na zaune ya zo dubata colonel ma ya shigo dan yana son yin sammakon komawa, sallama yayi Alhaji ya amsa, saida ya kai har k'asa cikin tsananin ladabi ya gaishesu, Alhaji dai ne ya amsa banda Hajia dake kallonshi, yana d'agowa suka had'a ido yayi saurin sauke kanshi k'asa, shiru ne ya d'an ratsa d'akin kamar anyi sabuwar mutuwa, ganin dai ba zatayi magana ba yasa ya kalli Alhaji yace "Alhaji zan koma ne dama."

Cikin dattako yace "To Husseini, Allah ya tsare ya kiyaye."

"Ameen nagode." Ya fad'a yana kallon Hajia yace "Hajia zan..."

Saida ta d'ago daga jinhinar da tayi cikin katse hanzari tace "Wallahi ranka zai mugun b'aci idan ka ambaci suna na."

Marairaicewa yayi kamar yaro yace "Hajia dan Allah kiyi hak'uri ki yafe mana."

Saukowa tayi daga gadon tace "Akan me zan yafe maka? Husseini kasan me ka aikata kuwa? Ni zaka wulak'anta."

Alhaji ne ya mik'e tsaye ya kalleshi yace "Kaga tashi, tashi ka tafi inda zaka Allah ya kiyaye hanya."

D'aga kai yayi ya kallesu duka saiya kasa tashi, cikin d'aga murya Alhaji ya sake cewa "Ka tashi ka tafi nace."

Mik'ewa yayi yace "Na tafi." Yana fita Hajia ta kalleshi cike da jin haushi tace "Wai me yasa kake min hakane? Ya zanyi magana dashi kawai ka wani ce ya tafi? Ina ruwanka to da abinda zamu tattauna? Meya hana kai ka fita idan ba zaka sauraremu ba."

"Dakata Zeeya'atu." Ya fad'a yana d'aga mata hannu, d'orawa yayi da "Da alama har yanzu baki san annabi ya faku ba, to ki bud'a kunnenki da kyau ki saurareni, babu wani hukunci ko matakin da zaki d'auka kan lamarin nan, dukanmu zamu duk'ufa ne mu nemi gafarar ubangiji kan zunubanmu, dan idan da wanda yayi sanadiyar faruwan hakan to ke ce."

Nuna kanta tayi tace "Ni? Ni fa kace! To me nayi ni d'in? Ce musu nayi su aikata? Ko kuma ina wurin sanda suka aikata bare ya zama laifina ne dana barsu suka aikata."

Saida ya tsaya daf da ita yace "Ke kin manta abinda ake fad'a ne cewa duk abinda kayi shi za ayi maka?Ai indai zakayi d'in to fa ka kwana da shirin sai an maka."

Rarraba ido ta fara yi alamar rashin gaskiya, sai kuma ta nad'e tabarmar kunyarta da hauka tace "Ban gane ba? Kana nufin nima nayi ne ko?"

Dariyar kin raina min hankali ma ya mata yace "Ni bance ba, amma dai ki sake kula ki kuma nemi yafiyar ubangijinki, idan ba haka ba wallahi yanzu irin abunuwan nan suka fara faruwa, kuma ki sani su ne zasuyi ajalinki, dan haka zaifi kyau ki koma ga Allah ta yanda in mutuwar ma ta zo ki cika da imani cikin kyakyawan yanayi."

K'wank'wasa k'ofar suka ji anyi wanda yasa su kallon k'ofar, Alhaji ne yace "Shigo."

Ammar ne tare da Amar da Amna da kuma Jibril, da sallama suka shigo dukansu, gaishesu sukayi sosai kafin su kalli Hajia su ce "Ya jiki?"

Saida ta wani d'aure fuska tace "Da sauk'i."

Ammar ne yace "Hajia kin karya kuwa?"

Girgiza kai tayi alamar a'a, juyawa yayi yana fad'in "Ya kamata ki daina jinkirin nan fa."

Amna ce tayi saurin cewa "Yah Ammar bari na karb'o."

Tsayawa yayi ita kuma ta fita, Alhaji ne yace "Ina Junaid yake?"

Amar ne yace "Anya Junaid ya kwana gidan nan kuwa? Dan ni dai jiya sai dare sosai na shigo amma banga motar shi ba, yanzu ma kuma babu motarshi a wajen ajiyewa."

Kai Alhaji ya girgiza, Amar ne ya fara mik'ewa yace "Zan wuce ni lokaci na tafiya, Hajia Allah k'ara sauk'i."

Saida ya mik'e tace "Shalele ka zauna tare dani mana, kai kad'ai nake son gani a kusa dani, wasu banda b'ata min rai babu abinda suke yi."

Ta k'arashe maganar tana kallon Alhaji da kuma Ammar, murmushi dukansu sukayi sai Amar da yace "Kiyi hak'uri Hajia, wallahi akwai aiki sosai a ofishi, amma na miki alk'awarin zan dawo da wuri sai na zo mu zauna."

Murmushi ta masa tace "To karka manta fa, saika dawo."

Ficewa yayi Amna kuma ta shigo, Jibril ma tashi yayi ya fita haka ma Alhaji, yau ma kamar jiya da kanshi ya zuba abincin ya zauna kusa da ita ya fara d'ebowa a cokalin ya nufi bakinta, kawar da kai tayi tace "Bani zan ci da kai na."

Girgiza kai yayi yace "Idan da kanki ne ba zaki ci dayawa."

Sake tura mata cokalin yayi ta bud'a baki ta karb'a, yana cikin bata Ummy da lieutenant suka shigo tare, su ma gaishe ta sukayi da tambayar jikinta ta amsa ba yabo ba fallasa, kallonta Ammar yayi ya d'an sunkuya yace "Baki tambaye su Shureim ba."

Kallonshi tayi amma yanda yake kallonta yasa taji ta kasa masa gardama, kallon lieutenant yayi dake rik'e dashi kamar zata bud'a baki sai kuma ta ga ai ba girmanta bane sai kawai ta sake kawar da kanta, Ummy da lieutenant mamaki suke sosai har da Amna ganin wai Hajia ce ke karb'an abinci daga hannunshi, da wannan mamakin Ummy tace "Hajia Allah k'ara sauk'i, zan tafi gurin aiki amma ba zan jima ba saboda na dawo kusa dake."

Ko kallonta ba tayi ba harta fita, lieutenant ma sallama ya mata suka fita, Amna ce ta kalleshi tace "Yah Ammar zan duba Hamna na dawo."

Kai ya jinjina mata ta fita, saida ya gama bata ya bata maganin tasha ya mayar da komai ya aje sannan ya kalleta, cikin dakakkiyar murya yace "Hajia gaskiya Alhaji ya fad'a miki, akwai buk'atar mu tuba ga Allah."

Ya fad'i hakane saboda sanda ya riga kowa isowa bakin k'ofa yaji kalamanshi na k'arshe cewa *"Dan haka zaifi kyau ki koma ga Allah ta yanda in mutuwar ma ta zo ki cika da imani cikin kyakyawan k'arshe."*

Ido ta zaro tana kallonshi, duk tsoro ya bayyana tare da ita tace "Me? Ammar lab'e kake mana dama?"

Murmushi ya mata yana girgiza kai yace "Banda wannan lokacin Hajia, watak'ila Allah yasa na jini saboda akwai abinda zan iya yi akai."

"Me kaji d'in?" Ta fad'a idonta a waje, saida ya had'e dariyarshi ya kalli idonta sosai yace *"K'uruciyarki, rayuwarki ta baya Hajia, wacce babbu wanda yasan da ita sai Alhaji sai kuma ni da naji yana fad'a a cikin addu'o'inshi."*

Cikin rawar hannu ta d'oki hannunta na dama ta rufe baki da taji numfashinta na neman gagararta, a hankali a hankali ta fara lumshe idonta da taji kanta na juyawa tare da sara mata, mik'ewa yayi ya kwantar da ita kan matashi, yatsu biyu yasa ya dafa kanta inda yaga tana dafewa da hannu, bud'a jakarshi yayi ya fara dube dube, da k'arfi ya d'aga daga sunkuyawar da yayi yace "Shiit."

Da gudun bala'i ya juya ya fita, kamar wanda kura ta biyo haka yake gudu har wanda suka ganshi suka tsaya kallonshi, b'angarensu na samartaka ya shiga cikin sauri yake bud'a kowane d'aki ya shiga, d'akin magungunanshi ya shiga cikin sauri sosai ya
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment