Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

kuma wani tarin wahala, kafin ta tashi zaune ya finciko dogon gashinta ya jawota k'asa yana shirin fita da ita daga d'akin, da gudu Sameera ta k'arasa ta durk'ushe ta rik'e ta tana rufe mata jikinta, dan dukan da taci ranar yasa bras kad'ai take iya zama da ita sai wani dogon wando wanda bai kamata jikinta ba, kallonshi tayi ido jawur cikin b'acin rai dan abun ya fara isarta tace "Abban Ameer meye haka wai? Ya zaka mayar min da yarinya kamar wata jaka? Me tayi maka?"

Sakin gashinta yayi ya nunasu da hannu yace "Ni yarinyar nan zata kunyata ta tozarta a idon al'umma? Kinsan meya faru yanzu? To auren da aka d'aura mata yanzun nan Abdul ya saketa saki uku saboda ganin hoton shaid'ancin da take aikatawa a waje, me zan mata idan ban illata ta ba?"

Kallon fuskarta Sameera tayi ta kuma kalleshi tace "Abdul d'in ne ya saketa? Wane hoto kuma?"

Cikin b'acin rai ya fito da wayarshi ya nuno hoton ya nuna mata, tana gani ta lumshe ido tace "Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un, Raihan? 'Yar dana haifa?"

Kallonta data mata yasa Raihan ganin ta sake shiga uku, da sauri ta mik'e tayi baya nesa da su cikin matsanancin kika tana fad'in "Iyayena dan Allah ku fahimce ni, wallahi ban aikata abinda kuke tunani, idan baku yarda ba zaku iya kaini duk likitar da kuke so a duba ni."

A fusace Abbas yayi kanta ganin haka Sameera da sauri ta mik'e ta shiga tsakaninsu tace "Kayi hak'uri dan Allah ka nutsu, idan muka bi ta zuciya zamu iya kasheta, a k'arshe zamu iya yin nadama."

Yatsa ya nuno mata ya bud'a baki zaiyi magana wayar shi tayi k'ara, juyawa yayi ya koma inda Sameera ta saki wayar ta taso ya duba, lambar Alhaji Khamis ne wanda suke mutumta juna, juyawa kawai yayi ya fita daga d'akin inda Sameera ta juyo kan Raihan ta wanketa da mari tace "Mamana abinda zaki saka min dashi kenan? Me na miki a rayuwa da kika zab'i hukuntani ta wannan hanyar?"

Dafe kunci tayi tana kuka zata durk'usa k'asa ta fizgota ta nufi toilet da ita, suna shiga ta mayar da k'ofar ta rufe ta kama Raihan da k'arfi ta zage mata dogon wandon had'e da pant d'in ta, kunya ce tasa Raihan ja baya tana rufe gabanta, wata harara Sameera ta wurga mata hakan yasa ta d'an kawar da kanta, ba zato ba tammani taji wani zafi ya ratsata da k'arfi sakamakon shigar da yatsa da Sameera tayi na kusa da manuniya, k'ara tayi lokaci d'aya kuma tayi shiru har wasu hawayen wahala sun zubo mata, fito da yatsan tayi ta kalleta sai kuma ta zauna dab'as a tsakiyar toilet d'in, ita gaba d'aya ma kanta ya kulle ta rasa taya zata iya fahimtar yarinyarta budurwa ce, ba zata iya kaita likita ba gaskiya saboda sanannun mutane ne su, hakan zai tab'a kima da kuma mutuncinsu, Raihan kuma d'aukar wandon tayi ta mayar ta sunkuya tace "Ammie, dan Allah ki daina kuka a kaina, Ammie zan sake samu wani mijin na aura, nayi miki alk'awari da idonki sai kin tabbatar da yarki bata watsar da tarbiyyarta da kika bata ba."

A waje kuma yana fita Alhaji Khamis ya samu k'ofar masallacin ya tsaya, cikin nutsuwa Alhaji Khamis yace "Alhaji Abbas na fahimci duk abubuwan dake faruwa, idan zaka bani dama zan so na karb'awa babban d'ana *Baban gida* aurenta? Dan bai kamata a fasa d'aura auren nan ba."

Kallonshi Abbas yayi sosai, hak'ik'a yasan Alhaji Khamis mutumin kirki ne mai sanin ya kamata da dattako, sai dai kuma baisan komai a game da d'an sa ba, duk lalacewar Raihan kuwa zai yarda yayi wannan gangancin? Ganin baice komai ba yasa Alhaji Khamis cewa "Nasan abune mai wahala, amma karka damu ka fad'a min abinda ke ranka, maganar aure tafi k'arfin wasa, Baban gidan bai tab'a aure ba, karatu ya saka a gaba, yanzu haka ma yana *Maroc* wurin karatu, amma shekara mai zuwa zai kammala ya dawo gida, sunan mahaifina ne da shi, wato takwaranka ne."

Kallonshi Abbas yayi sai kawai yace "Ba damuwa Alhaji Khamis, ai hallaci ka mana, kasan yarana ka haifesu amma baka haifi halinsu ba."

Take suka shiga masallacin yan mutanen da suka rage suka shaida d'aurin auren *Abbas Khamis Abbas* da kuma *Khadija (Raihan) Abbas Abdul rahaman* akan sadaki dubu d'ari biyu.

Suna fitowa daga masallaci ana taya juna murna suna tattauna yanda tariyar zata kasance, amma Abbas cewa yayi ai kawai tunda shi Khamis gobe ne zai tafi to kawai zai tafi tare da surukarshi, sannan a yau zai gama mata shirye shirye taje can ta samu mijinta, kuma duk yayi hakane dan ya kawar da ita daga gabanshi, dan ranshi b'acewa yake idan ya ganta kuma tana tuna mishi da abinda shi ma ya aikata, nan Alhaji Khamis ya kira gida ya sanar da iyalai, mahaifiyar Baban gida ta rasu sai kishiyoyi, hakan yasa babu wacce tayi murna da jin haka, dan su abinda suka hango ba wai dalilin auren da gaggawa ba, a'a, tarin dukiyar da mahaifin yarinyar ke da shi, mutumin daya mallaki jirage na kanshi, compagnie da masana'antu ba adadi, sannan uwarta ma jinin sarauta ce, wannan bak'in cikin yasa suka kasa farin ciki, saidai sunyi abincin sadaka kamar yanda mai gidan yace, dan in basuyi ba rai zai b'ace kasancewarshi mutum jajirtattace a gidanshi.

Baban gida ma da yaji musu yayi wa mahaifin nashi, amma dayake yana da zafi saiya balbaleshi da bala'i yace idan ya turo mishi yarinyar ya yankata idan ya cika d'an halak ne shi, haka yaja baki yayi shiru shima yana jiran isowar yarinyar.

*Ma'aruf* da kanshi ne ya shigo musu da abun kari, babu abinda Ma'arufa tayi tunani dan dama kusan kullum shi ke siyowa, ko da baya da kud'i ita zata bayar ya siyo, yana kallonta har ta gama cin indomie ta d'auki lemun daya siyo mai sanyi ta fita dashi tana sha, fatan alkairi ya mata har da cewa tayi sauri ta dawo fa, tana kan hanyar zuwa ta kira Abbas a lokacin an d'aura auren yana wa su Ammie bayani, ganin lambarta yasa shi barin waje ya d'anyi nesa da su, Harira data fito d'auke da jus jus d'in da zata kaiwa bak'in dake gidan ta ganshi yana amsa waya, tsayawa tayi ta lab'e ta kasa kunne tana sauraren shi.

Abinda taji kawai shine "Naji, mu had'u a inda muka had'u jiya, amma ki sani wannan uta ce had'uwarmu ta k'arshe dake."

Tana ganin ya nufi wajen ajiyar motoci ta d'an fito daga lab'ewarda tayi ta aje jus jus d'in ta rigashi fita, yana fitowa ya d'auki hanya ita ma cikin sa'a adaidaita ta fito daga kwana, shiga tayi tace su bi bayan motar...

πŸ‘πŸ‘πŸ‘
22/06/2020 Γ  17:26 - Ummulkhairi: πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨
*BADAK'ALA*
πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨

*Labarin Gaske*

*NA*

_SAMIRA HAROUNA_

*Litattafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._

*SADAUKARWA GA*

πŸ‘¨β€πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘¦ _*AHALI NA*_πŸ‘¨β€πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘¦

πŸ‡³πŸ‡ͺ *TAURARIN NIGER*
```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)```

_Bismillahir rahamanir rahim_

_21_


"Dan ubanka meye haka? Wallahi idan ka sake dukanta saina rama mata tunda d'an iska ne kai, Ammar meye haka? Zalincin ne ya motsa maka? Wannan wane irin haukane da iskanci? Me yarinyar nan ta maka da zaka kamata da duka haka?"

Cikin d'aga murya kamar zai fasa gidan yace "Ummy inba raini da iskanci ba ni Amna zata rainawa hankali? Na d'auke na kaita shagon Ilu amma dan iskanci a gabana zata tsaya kula wani bayan kuma tasan nine mijinta, akan me zata min haka? Laifin me nayi? Tana so ta nuna ni ba cikakken namiji bane ko me? Waccen d'in da me ya fini? Kyau? Ilimi ko kud'i? Ko kuma lafiya da girman jiki taga ya fini?"

Cikin hassala Ummy tace "Mijinta? An d'aura maka auren da ita ne? Kai bari ma na tambayeka? Ka k'addara an d'aura muku auren, kenan haka zaka mata wannan dukan tana matsayin matar taka?"

Zaro ido yayi yace "To me zan mata? D'aki zan sakata na dinga rera mata wak'a ina mata rawa dan na kwantar mata da hankali?"

Kallonshi Ummy tayi tace "In kuwa hakane lallai ba namiji bane kai, ba zaka tab'a zama jarumin namiji a gurin mace mai hankalin da tasan ciwon kanta, tun ranar da aka ce Amna ce k'addarar aurenka ta fad'a mata na fara mata kukan tausayi, dan indai har akayi kuskuren had'a ta da kai to babu makawa yarinyar nan tana daf da ajalinta."

Take yaji wasu hawaye na son taho mishi, mahaifiyarshi ce data haifeshi take fad'a masa haka? K'ok'ari yayi ya mayar da hawayen ya kalli Amna yace "Kina ji ko? A dalilinki ne take fad'a min haka, ni kuma nayi alk'awari saina tabbatar muku da namiji ne ni."

Girgiza kai Ummy tayi ta kama Amna suka mik'e tana gyara doguwar rigarta, Husseina ce da mamaki ya isheta tace "Amna kuma? Ai ba Amna bace Hamna ce, Ammar meyasa baka tsaya kayi tunani ba kawai ka hau dukanta haka?"

Dafe k'ugu yayi da hannu d'aya hannu d'aya kuma ya nuna kanshi yace "Kenan yanzu na zama mahaukaci ne da ban iya gane yaran da har goyasu nayi a bayana? Yaran da suka tashi a gaban idona ne zan kasa fahimtar wacece wannan ko wacce waccen?"

Kallonta Ummy tayi dan ta gane wacece ma a ciki, sai dai duhun dake akwai wajen bai bari ta iya ganewa ba, hakan yasa tace "Da gaske ne? Amna ce?"

Gyad'a kai tayi alamar eh, sallalami Husseina ta fara ta rik'e baki tace "Oh ni Husseina, yanzu dama Amna ce nake wa kallon Hamna? Amma meyasa dana kira Hamna kika amsa? Ita tana ina?"

Amna da har yanzu take jin marin nan daya mata da takalmi kuka kawai ta sake fashewa dashi, shi kuma k'wafa yayi ya kalleta ya nunata yace "Daga yanzu duk inda zaki je saina baki izini indai har nine wanda zai aure ki." wucewa yayi inda Ummy ta bishi da kallo ganin jikinshi biji-biji ga kayanshi sai k'yallin mai suke, kama Amna tayi suka shiga ciki bata yarda sun tsaya falon ba, sama suka haura d'akin su suka zaunar da ita, fad'a Ummy keyi sosai na haushi da takaici, har da cewa "To ubanki ne shi da har zaki tsaya ya miki wannan dukan? Ba dan kin zama sakarya ba ma akan me zakiyi tsaye yana d'irkarki haka? Amna aure fa ake shirin yi miki dashi, da hakane zaku zauna kinsa tsoronsa a ranki? Na tabbata da yer uwarki ce Hamna wallahi ko gudu ne tayi daga gurinshi, dan baya da maraba da mahaukaci idan ranshi ya b'ace."

Amna dai shiru tayi sai sharar hawaye take, hakan yasa Ummy cewa "Kiji harda wani cewa wai in zaki fita saida izininshi, to mu duk aikin banza ne kenan a gidan? To zaki fita bada izinin nashi ba sai naga in kasheki zaiyi."

D'agowa Amna tayi cikin kuka tace "A'a Ummy, tunda dai yace haka ni zan bi umarninshi, zan nemi izininshi kafin na fita, shikenan sai a zauna lafiya, ko Mama ma tana fad'a mana mu dinga jin maganarshi dan shi kad'ai ne ke tsawatar mana."

Da mamaki Ummy tace "Ke yanzu sai ki biye masa kuma?"

Jinjina kai tayi alamar eh tare da cewa "Ummy hakan shine zaman lafiya na, nasan ni ba yer uwata Hamna bace, nice mafad'aciyar kuma mai zuciyar, amma akan yah Ammar bana da ko d'aya, bansan meyasa ba."

Tab'e baki Ummy tayi tace "Lallai kina da aiki Amna."

Ko da yayi wanka shiryawa yayi cikin riga da wando bak'ak'e, makullin mota ya d'auka ya sake fita, k'aramin gurin cin abinci ne *Kebab* ya zauna ya ci abinci, daga nan kuma hanya ya d'auka saida ya samu inda babu hayaniya ya paka nan, jingina kawai yayi yana sauraron wa'azindake tashi a motar, maganganun Ummy ne kawai ke dawo masa a k'wak'walwa, awa d'aya da rabi ya d'auka a wurin nan kamar mai bacci kafin wayarshi ta fara ruri, saida kiran ya tsinke aka sake maidowa kad'ai ya taso daga kwanciyar da yayi ya d'auki wayar, a zuciyarshi yace "Abdullahi kuma? Meyasa zai kirani a wannan lokacin?"

Tsaki yayi saboda wata zuciyar data fad'a masa watak'ila zai maka k'orafine saboda baka je d'aukar amarya ba, d'auka yayi ya d'ora a kunne yayi shiru, daga can b'angaren Abdullahi yace "Ammar yane? Kana cikin gari ko kana gida?"

Can k'asan mak'oshi yace "Lafiya?"

Abdullahi ne yace "Lafiya ba lafiya, dama a cikin yan matan amarya ne aka bar wasu basu samu komawa tare da sauran mutane ba, kuma gashi duk wanda na kira wallahi wasu ma sun fad'a min kai tsaye ba zasu iya dawowa d'aukar su, ni ma kuma mota ta tun safe tana hannun k'ane na, yanzu haka nafi awa d'aya ina jiran adaidaita sahu ko taxi na samar musu amma wallahi shiru, gashi dare na k'arayi shiyasa nace bara na kiraka dan Allah ka zo ko Hamna ka d'auka, tunda kaga gidanku ba bari fitar dare ake yi ba inba da dalili mai..."

Ammar ne ya dakatar dashi cikin sanyayyar murya yace "Ya isa haka dan Allah, magana ba tsayawa ba numfasawa, yanzu kenan nufinka naje na zama drebata na d'auko ta? Bayan kuma a gida babu wanda ma yasan da fitarta, to ba zan iya ba."

Abdullahi ne yace "Dan Allah Ammar ka taimaka, bana so ne ta shiga matsala a dalilin halartar bikin nan nawa, dan Allah."

Tsaki yayi ya kashe wayar, hakan kuma yasa Abdullahi yarda d'ari bisa d'ari cewa zai zo, dan haka ya ci gaba da tsayuwa a bakin titin, ai kuwa baifi minti ashirin ba saiga motar Ammar, dan dama yasan gidan da jimawa dan anjima ana ma gidan tsare tsare tsare da tanadi, k'arasawa sukayi k'ofar gidan Abdullahiya shiga ya samu su Hamna cirko cirko su biyar a farfajiyar gidan, Hamna ya kalla yace "Hamna ki taso ga Ammar nan zai tafi dake."

"Wa!? Ta fad'a da k'arfi tana zaro ido ta d'ora da "Waya fad'a mishi ina nan? Meyasa sai yanzu ya zo bayan ban ganshi d'azu ba?"

Abdullahi ne yace "Yanzu dai ba lokacin magana bane ki taso ku tafi kafin ya mana tijara ni dake."

Mik'ewa tayi tace "Ina zuwa." Cikin d'akin ta shiga ta samu amaryar tare da babbar yayarta tana k'ara gyara mata d'aki, uwar d'aki suka shiga Hamna tace "Dan Allah k'awata taimako zaki min."

"Taimakon me kuma k'awata?" Cikin fargaba tace "Yah Ammar ne ya zo d'auka ta, kuma jiya ma a wurin kamun ku saida ya min fad'a kan fita babu hijabi, shine nake so dan Allah ki ara min ko da babban mayafi ne, insha Allahu gobe idan na taso daga Γ©cole zan biyo na kawo miki."

Murmushi tayi ta nuna mata wurin kayan tace "Besty akan wannan ne har kike cewa wani taimako? Ki duba ga kayan nan sai ki zab'a."

"Yawwa." Ta fad'a tana bud'a wurin kayan, wani babban mayafi ta d'auka wanda ya dace da kayan nata, ita kanta data kalli madubi sai taga tafi kyau da kamala, sai ta ganta kamar wata amaryar ita ma, fitowa tayi zata fita sauran k'awayen suka ce ai ba zata barsu ba, tare suka fito inda ta zagaya zata shiga motar, da kallo ya bita har ta shigo, amma take jikinshi ya bashi wannan ba mayafinta bane, cikin lallami Abdullahi ya zuro kai yace "Abokina ka taimaka ka aje wad'annan ma mana, in kayi haka zaka samu lada fa."

Kallonshi yayi fuskar nan a d'aure yace "Me zai hana ka basu makwanci a gidan naka? Ai sabgaka suka zo? Ni munyi da kai zan zo d'aukar maka mata ne?"

Murmushi Abdullahi yayi yace "Ba haka bane, amma dai ka taimaka."

Mayar da kallonshi yayi kan titi yace "Kasan zasu rage maka jin dad'i kenan? Shine ni ma zaka takura min."

Kallon yan matan yayi da suka saki baki suna kallonshi yace "Ku muje."

Da sauri wuka bud'a suka shiga suka zauna, ko kallon Abdullahi baiyi ba ya ja suka wuce, saida sukayi tafiya mai nisa babu mai magana kafin ya daidaita madubin gabanshi yana k'arewa yan matan kallo, a ranshi yake k'yamar irin shigarsu kamar ba yaran musulmi ba, babu wacce babu k'arin gashi a kanta da muguwar kwalliya ta d'aukar hankali, girgiza kai yayi ya juya ya kalli Hamna, sai kace wata malama k'wafa yayi ya ci gaba da tuk'i, sunyi nisa muryar d'aya daga cikin yan matan tace "K'awa Hamna da kina da yaya kyakyawa haka shine bamu sani ba?"

Wani buhun haushi ne ya tasowa Hamna, tasan halin k'awarta dan haka ta d'aure fuska ta kalli Ammar da yake tunanin kalar iskancin da zai tatawa yarinyar, tab'e baki tayi a zuciyarta tace "Wai kyakyakwa, humm."

Ammar kuma juyawa yayi zai kalli k'awarta ta sai kuma ya ga ita sai wani had'e fuska take, kallon gabanshi yayi hakan yasa k'awar cewa " Yayanmu mun gode fa daka d'auko mu, dan har mun fara tunanin k'aryar da zamu fad'a a gida zuwa gobe."

Cike da shak'iyanci yace "Karki damu, ai mace irinki tafi k'arfin ta rasa mai sa'ar da zai d'auko ta, ni ne da godiya."

Fasa mata kai yayi da wannan maganar tashi, sai kawai tace "Nagode, amma nima sa'ata ce ace na shiga motarka har muna musayar yawu da kai."

Tsaki sukaji wanda yasa shi kallon Hamna da tayi tsakin, to na meye? Haka kawai taji ranta na b'acewa sai kumbura take, kamar Ammar yasan me take ji a zuciyarta sai kuwa ya biyewa k'awar suna ta hira, saida aka kawo inda zasu sauka tace "Mai kyau zaka iya aje ni anan ma."

Da murmushi yace "To mai kyau." Pakawa yayi su biyu suka sauka ya zuro kanshi yace "Bansan nawa ne farashin lambar wayarki ba, amma zan so ki fad'a min komai tsadarta zan biya dan a bani."

Cike da duniyanci tace "Farashinta mai tsadar gaske ne, amma kai na musamman ne, dan haka kawo wayarka na saka maka kyauta."

Cikin fara'a ya mik'o mata wayar yace "Ina godiya da wannan karamcin."

Tana cikin saka masa tace "Ai karrama mai karamci yafi k'arfin iyawata ni kad'ai, kai babban mutum ne."

Saida ya saci kallon Hamna yayi murmushi yace "Kinsan ba kowa yake gane girma da darajarka ba, wasu idan sukaga suna rayuwa tare da kai sai su mayar da kai kamar abun banza."

Bashi wayar tayi ya amsa tana fad'in "Ka rabu da su kawai, zasu fahimta ne a sannu duk ranar daka mallaki wacce zata dinga nuna musu darajar taka."

Wani murmushi yayi na iskanci yana goge lambar yayin da ita kuma take tunanin yana saka lambar ne a wayarshi yace "Ke wasu fa mahaukata ne basa fahimta duk yanda zakiyi da su, ki barsu da shan kayan ruwa kawai suna cika musu mafitsara."

Dariya tayi sosai yayin da sauran kuma sukaji kunya, kamar tasan da Hamna yake sai cewa tayi "Barta kawai, zan dinga fahimtar da ita matsayinka ko ta fara ganin girmanka."

Ammar ne yace "Amma zan iya sanin adadin matakan tsaron dake gidanku? Domin idan na tashi zuwa nasan irin shirin da zanyi."

Murmushi ta masa tace "Ka zo duk sanda kake so, zaka samu k'ofa a bud'e."

Da wani yanayin shegantaka yace "Allah ko?" Ita ma a salon wayewa ta marmad'a masa ido, hannu ya zuro ya bata da niyyar su gaisa yana fad'in "Saina kiraki mai kyau."

Bashi hannu tayi wanda yasha akaihu zargama zargama ita ma suka gaisa tace "Sai na jika mai kyau."

Kashe mata ido yayi ba tare daya saki hannunta ba yace "Za dai ki jini a waya mai kyau, amma jina ai sai bayan aure."

Murmushi tayi harda sunkuyar da kai tana d'an matsa hannunshi mai laushin gaske tace "Har kasa na fara tunanin kaina a matsayin matarka."

Kallon wannan mahaukaciya ce ya mata yace "Ni fa tunda na ganki nake jin ina k'amshin lalle."

Cikin b'acin rai da jin kamar ta rufe shi da duka tace "Dan Allah ni muje ka kaini gida na gaji da jin wannan zancen na ku."

Juyowa yayi ya mata wani kallon zan ma ci ubanki ne yarinya, kawar da kai tayi shi kuma ya saki hannun k'awar ta ta yana fad'in "Saida safe."

Jan motar yayi suka wuce har saida ya aje sauran ma kafin suka d'auki hanyar gida, babu mai magana ko kallon wani har suka kusa isa gida, a daidai su sha kwana motar police ke nan da alama wucewa zasuyi motar ta samu matsala, haka kawai wani police ya tsayar dasu, tsayawa yayi ya sauke madubin motar yana kallonshi daga shi har shi kowa fuska babu annuri, police d'in ne yace a harshen fransanci " Malam daga ina haka a daren nan?"

A hankali Ammar ya kalli agogon hannunshi k'irar gucci ta fata, ganin duka yanzu ne k'arfe *11:18* na dare yasa ya kalleshi yace "Daga inda ka aike mu mana."

Da alamar tambaya police d'in yace "Me? Malam wace irin amsa ce haka? Tambayarka muke daga ina kake?"

"Amsar kenan na baka, akan me zaka tare ni yanzu kana tambayata daga ina nake?"

Hassala yayi yace "Wai waye kai da zaka ce ba za'a tambayeka ba? Kafi k'arfin doka ne ko me? To fito daga motar sannan ka bamu takardun motar."

Murmushi yi wanda har yasa Hamna tsorata dan tasan k'aramin aiki ne yayi bala'i da shi yasa su kwana a gark'ame, murfin motar ya kama zai fito yana fad'in "Bara na fito kaga tsawo na to."

Cak ya tsaya saboda hannunshi da Hamna ta rik'e, yana kallonta ya ga hawaye har sun cika idonta, cikin rawar murya tace "Dan Allah ka basu takardun mu wuce."

Fizge hannunshi yayi yace "Sake ni dallah, ni zai nunawa wannan k'azamin kakin nashi, waye shi da har zai tambaye ni waye ni? Bari na nuna masa daidai nake da shi, uban wa ma ya bashi damar tsayawa nan d'in."

Zai fito ta sake rik'e rigarshi hawaye suka zubo mata tace "Dan Allah fa nace yah Ammar, ina jin tsoro."

Da k'arfi ya kawar da kanshi daga kallonta saboda jin zafin ganin hawayenta da yayi, police d'in dake tsaye ne yace "Kai nake jira ai ka fito, madame ki barshi mana naga me zaiyi, naji kana fad'in wai k'azamin kaki na, to fito na nuna maka k'arfin ikon kakin nawa."

Cikin hassala da k'ufula ya daki sitiyarin motar da k'arfi, yana son ya fita ya nuna mishi bai tsoronshi sai dai ya kulleshi, amma kuma baya son ganin Hamna cikin damuwar nan, ganin hawayen ta ma yasa shi jin babu dad'i haka yasa shi dole ya juyo ya kalle shi ya saisaita nutsuwarsa ya k'ak'aro murmushin na ganeka kuma zamu had'u ya masa yace "Yallab'ai, ka barmu mu tafi mana, madame d'in nan rigima ce da ita, kasan mace mai ciki saurin hawa."

Jin haka sai police d'in ya k'ara jin wata izza ai sai yace "Kawai ka fito daga motar ka bamu takardunka, yo har mu zaka d'auka wasu sakarkaru har kake fad'a mana magana, yau zaka gani."

Kallon Hamna yayi ita ma ta mishi kallon taimaka ka basu dan Allah, hakan yasa yace mata "Akwai takardun, amma wallahi ba zan bashi ba."

D'aya daga cikin wanda suke tare ne yana duba motar ya matso yace "Ya dai? Lafiya?"

Kafin police d'in yayi magana Ammar yace "Abokina wannan mutumin ne ke son b'ata min lokaci, to wai halan baya da aure ne? Inba haka ba ai da zai fahimci larurar da kan iya saka miji fitowa a dare kuma tare da iyalinshi, ka ganta nan."

Ya fad'a yana nuna mishi Hamna da gabanta fad'uwa yake ido taf da hawaye ya ci gaba da cewa "Tun sallah isha'i ta sani zagaye garin nan da neman wani wai karas, na fad'a mata yanzu ba lokacin karas bane amma ta k'i yarda, kai har karas d'in da Allah ya hore min na ce ta gatsa ☹️ amma tace bai mata ba, da k'yar na samu yanzu na lallab'a ta ita da d'an baba na siya mata alewa zamu koma gida, yanzu gashi kasa min ita kuka, domin Allah haka ya dace?"

Jami'in da yaga Ammar daban ne da mamaki yace "Dan Allah me sunanka?"

Murmushi ya masa yace "Ammar,
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment