Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ita? Kinsan me yale damunta ne? Ai kamata yayi ace ke kika fi kowa sanin abinda ke damunta duba da 'yan biyunki ce."

Mayar da hankalinta tayi kan Hamna da har yanzu take kuka ta jata suka zauna kan kujerun wurin ta ci gaba da tambayarta, amma sai Hamna ta share hawaye cikin shagwab'a tace "Mama kawai nayi kewarki ne sosai, munfi shekara bamu ganki ba fa, muna so mu zo amma Hajia ta hana mu, na fidda rai da zan ganki sai kawai boss ya kawo mu, dole nayi kukan farin ciki."

Dangware mata kai Hadiza tayi tace "Ke dai akwai sakarya wallahi, yanzu akan hakane kika d'aga min hankali."

Amna ce ta cire takalmi ta shiga d'akin tana fad'in "Ai dama na fad'a miki iskanci ne."

Da kallon jin haushi Hamna ta bita tace "Ke wallahi bana son iskanci kinji ko, ni sa'arki ce da zaki tsaya kina fad'a min abinda kika ga dama?"

Daga cikin d'akin tana cire kaya tace "Aje anyi d'in, inba raina mutane ba meye na duk wani canzawa lokaci d'aya? Tun jiya da kika je karatu d'akin Ummy kika zama wata iri dake."

Mik'ewa Hamna tayi ta shiga cikin d'akin tana fad'in "Wallahi kika min rashin kunya saina ci ubanki a wurin nan, ina ruwanki da canzawata to? Idan kinji haushi ki fita harkata mana, yar jaraba kai."

Daga waje Hadiza tace "Ya isa haka to, kar na sake ji bakin kowa a wurin nan."

Amna ce tace "Mama ki rabu da ita ta ci uban nawa mana idan zata iya."

Kallon Hamna tayi tace "Ke kinsan ko gawata wallahi tafi k'arfin ki, dan kin rigani fitowa duniya bafa tazara mai tsayi kika ban ba."

K'wafa Hamna tayi ita ma ta fara cire kayanta da nufin shiga wanka, kusan a tare suka jero kowace da d'aurin k'irji da zanin Hadiza na atamfa zasu fito hakan yasa suka matse junansu, ture juna sukayi inda Hamna ta bita da harara da tsaki, Hadiza dai na kallonsu tana jin dad'i dan ko ba komai yau tana jin hayaniya a gidanta na yara, Amna ce ta d'auki bokiti ta tara ruwa a bakin panpo inda Hamna ta d'auke kwandon sabulun wankan, Amna ce ta kalli mahaifiyar tasu tace "Mama ki fad'a mata ta ban kwandon nan."

Kallonta Maman tayi tace "Hamna ki bata kwandon idan ta fito kya shiga."

Cikin turo baki Hamna tace "Wallahi Mama ba zan bata ba saina fara yi, tun a hanya fa tasan ina cewa fitsari nake ji."

Hadiza ce tace "To ki shiga kiyi fitsarin ki fito saiki bata wurin."

Cikin yanayin sangarta tace "Mama kawai ki k'yalemu kiyi kallonmu, karki sa wannan sakaryar ta raina ni saboda kina d'aukar ta autarki."

Hadiza ce tace "To shikenan na saka muku ido, kafin nan ku fad'a min ina yaron kirkin yake ne? Kunce shi ya kawoku kuma banga ya shigo ba har yanzu."

Tab'e baki Hamna tayi tace "Waya sanin masa mugun kawai, Allah yasa ma ya tafi ya barmu nan mu kwana."

Girgiza kai kawai Hadiza tayi ta ci gaba da duba girkinta, tana kallo Hamna ta damk'i bokitin ruwan tana so ta raba Amna dashi, ita ma rik'ewa tayi sosai tace ba zata saki ba, hakan ne ya janyo musu kokawa da bokitin ruwan har suna ta zubewa a banza, wajen wannan tak'ak'abuwa bokitin ya fad'i k'asa ruwan suka watse a banza, da sauri Hadiza ta lek'o daga yar rumfar tana fad'in "La'ilaha illalahu, wai ku yanzu haka abun naku ya zama? Meye ha...?" Shiru tayi saboda ganin Ammar ya shigo cikin gidan.

Amna ce tayi k'asa da kanta yayin da Hamna kuma ta zabga mishi harara ta d'auke kanta, Ammar kam kawar da idonshi yayi daga kallonsu saboda ganinsu kamar 'ya'yan gwarawa, kowace da d'aurin k'irji hallitarsu ta fito fili, ta bayan Amna ya bi ya wuce yana kallon Hamna dake masa wani kallon iya shege, tun kafin ya k'arasa Hadiza ta aje masa kujera tana fad'in "Ammar ina ka shiga? Sun ce kai ka kawosu amma shiru baka shigo ba."

Sam babu fara'a a fuskarshi ya zauna akan labb'anshi ya amsa da "Masallaci na tafi Tanti."

Da fara'a sosai tace "Haba shiyasa, to anyi sallah lafiya?"

Ciki ciki ya amsa da "Lafiya lau." Kallonshi Tanti tayi tana murmushi a zuciyarta tana ayyanawa yau 'yan mulkin ne akan shi shiyasa ko gaisheta ya kasa yi, kallonsu Amna tayi da har yanzu suka kasa sulhunta kansu, girgiza kai tayi tace "Auta, ki barta tayi sai kiyi kinji, ki zo ki kawowa yayanku ruwa yasha kya samu lada ma."

Da sauri Hamna ta kalli Hadiza Amna ita kuma turo baki tayi ta sakar mata bokitin tana hararanta, cikin sand'a take takowa kamar wata marar gaskiya saboda ganin yanda Ammar ya had'e rai kamar hadarin gabas, cikin tsoron kar ya daketa ta samu ta shige d'akin ta d'auko hijab ta saka ta fito, ruwa ta d'auko mishi ta zuba ta bashi a lokacin da Hadiza ke tambayarshi meyasa bai tsaya d'aurin auren babban shi ba? Saida ya karb'i ruwan ya d'an kurb'a ya kalli Amna da jajayen ido yace "Wuce d'aki."

Kallonshi tayi kamar zatayi kuka cikin muryar tsoro tace "Yah Ammar..dama...alwala zanyi kafin ta fito."

Sake wurgo mata idonshi yayi wanda yasa gabanta fad'uwa, dan a yanda suka sani ko gaban mahaifiyarsu ta kama saiya kasheka da mari har ma ya d'auki madaki, ajiyar zuciya ta sauke mai sautin gaske saboda alamar daya mata da ido ta wuce, da sauri ta nufi wajen buta ta zuwa ruwa lokacin Hamna ta shiga wanka, bai sake tankawa ba har saida ya ga shigar Amna d'aki kafin ya kalli Hadiza dake kwashe abinci a kwanuka ya tab'e baki yace "Me yasa zanje d'aurin auren?"

Juyowa tayi ta kalleshi ita har ta manta ma data tambayeshi, tun yana k'aramin yaro take k'aunar shi har zuciyarta, ta sanshi tasan halinshi fiye da uwar data haifeshi, hakan yasa bata damu ba saima murmushi da tayi tace "Saboda mahaifinka ne mana, kuma zaiyi farin cikin ganinka a wurin a kusa da shi."

Murmushin rainin hankali yayi tare da kallon farfajiyar gidan yace "Ba zan iya wannan abun kunyar ba, tsofai-tsofai da kai kayi wani wai aure, auren ma ba da babbar mace ba ko wata bazawara, yarinya mai k'ananun shekaru, ko ni dake d'ansa wannan yarinyar ta min kad'an na aureta wallahi bare kuma shi."

Wani wawan tsaki yayi alamun dai abun ya dameshi sosai, banda dariya ba abinda Hadiza keyi kafin tace "Yaron kirki kenan, amma me yasa kake ganin ta maka kad'an?"

Sam babu alamar wasa ko kunya yace "Saboda ba zata iya d'aukata ba, zata iya mutuwa tun kafin aje ko ina, sannan ni banga albarkatun dake jikinta ba wanda zasu iya d'ebewa mutum kewa."

Murje ido Hadiza tayi ta nuna abun bai wani dameta ba dan tasan halin katob'aran yaronta tace "To dama wacece zata iya da kai yarona? Ai sai yar baiwa, amma fa duk da haka ita yarinyar ta dace da mahaifinku, tunda kaga kai sabon jini ne ka mata yawa, shi kuma an kwana biyu zai iya tafiya da ita yanda ya dace."

Cike da jin an fasa mishi kai yayi wani shak'iyin murmushi yace "Hmm; shi ma fa da sauranshi, dan yanzu haka zai iya samo mana cikakken k'ane."

Kafin tayi magana Hamna ta fito daga wanka, har tayi alwala bakin panpo ta basu sake magana ba, saida ta zo daf dashi zata wuce ta gabanshi dan hanyar da zata iya sadaka da d'akin ce kawai yace "Tanti ai duk wacce na kwanta da ita na tashi ita ma kuma ta mik'e da k'afafunta, to wannan ita ce daidai dani saboda ni jaruma nake so ba raguwa ba."

Da k'arfi Hamna ta kalleshi amma kash kamar ma baisan da tsayuwarta a wurin ba, cikin murmushi Hadiza tace "Zaka sameta mai jarumta yaro na, zanyi k'ok'arin ganin haka ta faru ko saboda jin dad'in ka."

Juyawa tayi ta kalli mahaifiyar tasu dake ta harkar gabanta, sake juyowa tayi ta kalle shi tayi k'wafa ta wuce, zata shiga ciki taji ya sake cewa"Kankana."

Cak ta tsaya ta juyo tana aika mishi wani mugun kallo, kallonta yayi ya gyara zama tare da shafar gemunshi yana dariyar iskanci ya kashe mata ido d'aya yace "...


*Alhamdulillah Allah*๐Ÿ‘
09/09/2020 ร  17:58 - Ummulkhairi: ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ
*BADAK'ALA*
๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ

*Labarin Gaske*

*NA*

_SAMIRA HAROUNA_

*Litattafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._

*SADAUKARWA GA*

๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ _*AHALI NA*_๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

๐Ÿ‡ณ๐Ÿ‡ช *TAURARIN NIGER*
```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)```

_Bismillahir rahamanir rahim_

_26_


Kallonta yayi ya gyara zama tare da shafar gemunshi yana dariyar iskanci ya kashe mata ido d'aya yace "Fita zanyi yanzu, zaki sha kankana ne na taho miki da ita?"

Sama da k'asa ta harareshi taja dogon tsaki ta wuce d'aki, ba tare daya daina murmushin ba ya bita da kallon *zaki gane kurenki*, Hadiza ce ta juyo ta bita da kallo tace "Ke Hamna lafiyarki kuwa? Meye na tsakin daga abun arzik'i? Bana son iskanci kinji na fad'a miki, wannan ba yayanki bane? Ko dan kinga yau ya sakar muku fuska ne."

Mik'ewa yayi tsaye yana gyara zaman doguwar rigarshi yana fad'in "Tanti ni zan fita na dawo."

Kallonshi tayi cike da kulawa tace "A'a, ka zauna mana ka ci abinci saika fita, nasan dai yanzu bakin ruwa zaka je ko?"

Murmushi kawai ya mata ya nufi k'ofar fita, da kallo ta bishi a ranta tana mamakin wani sauyi data gani a tare da shi tana fad'in "Yau Ammar babu saurin kai duka, har Hamna ta mishi tsaki amma ya nuna ko a jikinshi, lallai yau farar juma'a ce, ba dan haka ba ai da sai dai ta jiyo ihunta a d'akin."

Wata zuciyar ta fad'a mata "Dama ai yau da gobe sai Allah, mutum yana canzawa kamar yanda zamani ke canzawa."

Ba tare data daina kallonshi ba tace "Ko kuma dai dan za'a had'a shi da Amna ne, tabbas ma hakane, watak'ila kunyarta yake ji yanzu saboda sun zama surukai."

Bata gushe daga tunanin ba taji muryarshi cikin d'aga murya yana fad'in "Mutumin ya kake?"

Da kallo ta bisu ganin shi da mai gidan nata suna gaisuwa irinta yaran zamani marasa jin magana, murmushi kawai take saboda yanda suka birgeta kamar wani d'a da uba, dawowa sukayi ciki har cikin runfar inda Shu'aibu ya kama hancin Hadiza yaja sosai yana mik'a mata sallayar hannunshi yana fad'in "Matanmu ya aiki? Ashe bak'i kikayi bayan tafiyata?"

Hadiza data saba take kuma jin dad'in zama da mijin nata murmushi ta masa tace "Sannu da zuwa, bak'i kuma ba bak'i ba kam."

Ammar da soyayyar dattawan ke birgeshi sagala hannunshi yayi a kafad'ar Shu'aibu ya ja hancinshi yana fad'in "Duk ka jaye mana hanci uwa har yayi tsayi kamar karas, ka canza wani salo mana."

Shima kama wuyanshi yayi suna dariya yace "Uwar ka dai ce ka shammata bani ba ja'iri kawai, kuma ma wani salo zan canza bayan na saba da wannan."

Kashe mishi ido d'aya yayi yace "Muje waje zan fad'a maka irin wanda zaka sauya."

Hararan wasa Shu'aibu ya masa yace "Me yasa sai mun fita? A sani na dai baka jin kunyar fad'an komai ko a gaban wa."

D'ora kanshi yayi a kafad'ar Shu'aibu tare da jawo rigarshi yana rufe ido wai kunya๐Ÿ™„๐Ÿค” (bala'i, ban tab'a gani ba), cikin nuna jin kunya yace "Nima bansan ya akayi ba yau na ji na sauya, kawai dai muje waje na fad'a maka sabon yayi."

Ture shi Shu'aibu yayi daga jikinshi ya kalli Hadiza da banda dariya da girgiza kai babu abinda take yace "Wai ina yan biyuna ne ikon Allah? Amma dai banda Hamna aka zo ko?"

Hadiza ce tace "Har da ita ko, yau dai matsiyata ne bisa kanta shiyasa, dan da farko data shigo ma kuka ta saka mana, duk ta canza dai tayi wata iri."

Daga cikin d'akin cikin taushin murya Amna "Kawu ina wuni."

Cikin sakin fuska ya amsa da "Lafiya lau yan biyu ikon Allah, amma wace tayi magana? Kinsan ban cika gane ku ba har yanzu."

Amna ce tayi dariya zatayi magana Ammar yace mishi "Ba kankanar bace, d'ayar ce."

Kallonshi Shu'aibu yayi yace "Kai kam dama ai ko mahaifiyarsu ba zata nuna maka saninsu ba, Allah ya maka wannan baiwar tun haihuwarsu."

Murmushin jin dad'i yayi ya shafo gemunshi yace "Da wayona fa akayi auren Tanti da Tonton, sannan tare da ni tanti ta ci amarcinta, tare dani tayi laulayin cikinsu, hasalima ni nake shafa cikinta ina fad'a mata zata haifi yan biyu kamar ni da d'an uwa na, sannan a idona ta fara nak'udarsu ni ne ma na kira mutanen gida aka kaita asibi, tare dani akayi jegonsu, sannan tare da ni Ummy ta rainesu har sukayi wayo, to ni kam meye zai shige min duhu a tare dasu?"

Duk da Shu'aibu ya ji kishi a zuciyarshi lokacin da Ammar yace sun ci amarci, amma kuma bai nuna ba ko a fuska sai darewa da yayi yace "Gaskiyar kam, amma yanzu dai bari na gano kankanar ta bakinka."

Zai shiga d'akin Ammar ya rik'o hannunshi yace "Muje waje haba muyi hira, rabu da kankana nasan matsalarta."

Daga d'aki Amna tace "Kawu sallah ma take."

"Shiyasa dai banji muryarta ba ashe." Cewar Shu'aibu kafin ya kalli Hadiza yace "Idan kin gama abincin ki aiko mana shi k'ofar gida, wannan sarkin zancen ba zai barni na gama kallonki ba."

Dariyar shak'iyanci yasa suka nufi waje yana fad'in "Ai mutumina shiyasa nake so muje waje na k'ara baka wasu shawarwarin yanda zaka ci gaba da kula mana da tantinmu, dan naga ba tsufa kuke ba ku, shiyasa nake so naga kullum kana nan a jaruminka kana bada wuta a ciki."

Shu'aibu dariya yayi yace "Cikin me?"

Sunkuyar da kai yayi yace "Kai ma dai har saina fad'a? Ka sani mana."

Shu'aibu ne ya d'auki tabarma suka fita, suna zuwa ya shinfid'a a k'ark'ashin bishiyar dake k'ofar gidan tare da wata k'atuwar darduma suka zauna, a cikin gida kuma Hadiza k'walla kiran Amna tayi tana fitowa tace ta d'auki abinci ta kai musu, cikin ladabi ta d'auka har da ruwa ta kai musu.

*Gaga's House*๐Ÿ˜

Hankalin Ummy ne ya fara tashi ganin babu Hamna kuma babu Amna, wayarta ta fara kira amma abun mamaki saita samu wayar a d'akinta, alama dai wahalar da tasha tasa ta manta da wayar ma a d'akinta, Amna ta koma kira ita kuma kashe wayar dan tunda zasu shiga aji ta kashe oga boss kuma yasa ta manta bata kunna ba, saida rana tayi sosai lokacin su Hamna na cin abinci ta d'auki wayar ta kunna, ganin kiran da Ummy tayi bata samu ba yasa ta mayar da kira, da sauri Ummy ta d'auka tana fad'in "Amna, lafiyarku k'alau kuwa? Ina kuka tsaya ne haka?"

Da murmushi a fuskarta tace "Ummy kiyi hak'uri banga kiranki ba sai yanzu na kunna wayar, wallahi muna lafiya lau babu komai."

"To kuna ina har yanzu baku zo gida ba?" Ta fad'a cike da k'aguwa, kallon Hamna tayi da ita ma ke kallonta tace "Ummy gamu nan gida wajen Mama."

Da k'arfi Ummy ta zaro ido tace "Me? Mamanku? Ke da wa?"

Jin yanda Ummy ta rud'e yasa tayi dariya tace "Ummy kwantar da hankalinki, yah Ammar ne ya kawo mu tare da Hamna muke."

Da sauri cike da tsoron abinda Hamna zata fad'awa mahaifiyarta Ummy tace "Ina Hamnar take? Bani ita."

Mik'awa Hamna wayar tayi ta ci gaba da cin abincinta Hamna kuma ta amsa da "Ummy lafiya lau muke fa."

Ajiyar zuciya ta sauke tace "Hamna ina cikin damuwa sosai, kar Hadiza ta fahimci wani abu ya faru dake, dan Allah ku dawo yanzu Hamna kafin Hajia ta ankare da rashin dawowarku, kinsan a kaina k'urar zata sauka tace da sani na kuka tafi babu izininta."

Cikin rashin karsashi Hamna tace "Ummy wallahi ba laifinmu bane, kawai muna fitowa daga makaranta ya zo ya d'auke mu da k'arfi."

Cikin rashin kulawa Ummy tace "Ni ban damu da lamarinshi ba, ko da kun dawo ma yasan yanda zaiyi ya fitar da kanshi wajen Hajia ko kuma ya sake tsula mata wata tsiyar, ku kawai nake ji Hamna, dan Allah ku k'ok'arta ku dawo kafin sallah la'asar, kunga gida anata hidima kuma ana tambayar ina kuke."

Cikin sanyin murya tace "Ummy yanzu ba zamu iya kwana a nan ba? Mun jima fa rabonmu da nan."

Da sauri tace "A'a Hamna rufa min asiri dan Allah, ni dai na rok'eku ku dawo yanzu kinji, inba haka ba ni zan zo garin na taho da ku, Hamna ko kin manta kina buk'atar kulawa ne?"

Turo baki tayi kamar tana gabanta tace "Shikenan Ummy zamu dawo."

Murmushi tayi mai sauti tana fad'in "Yawwa yar albarka, sai kun zo kinji, ina maman taku ne?"

"Tana waje." Cewar Hamna a dak'ile kafin Ummy tace "Bani ita mu gaisa."

"To." Ta fad'a tare da mik'awa Amna wayar tace "Kaiwa Mama."

Figar wayar tayi tana dalla mata harara da fad'in "Ke musaka ce da ba zaki iya tashi ba ko me?"

K'ala ba tace mata ba har ta fice ta kaiwa Mamansu wayar, sosai suka gaisa inda Hadiza take sake godewa Ummy kan kula mata da yaranta da take, sannan ta d'ora da "Munji kuma abun alkairi had'in da Hajia tayi, Allah ubangiji yasa alkairi yasa ayi muna raye."

Ummy ce ta amsa da "Ameen, insha Allahu ma ai zan zo ko dan muyi magana da shirye shiryen abinda ya kamata na bikin, ina jira ne a gama wannan sabgar lokacin an kawo komai da komai sai na zo."

Ita ma Hadiza murmushi tayi tace "Sa'ada kenan, ai ke ce uwar yaran nan, duk abinda kikayi wallahi d'aya ne, babu abinda zan ce muku ke da lieutenant ai sai godiya."

"Ba komai wallahi yiwa kaine ai." Da haka sukayi sallama ta mayarwa da Amna wayar d'aki wanda ta same su suna rigima Hamna ta dage sai Amna taje waje ta fad'awa Ammar Ummy tace su tafi, ita kuma tace ba zata ba salon ya mata rashin mutumci, dariya Hadiza tayi tace "To ke da zai aureki kina shakkar yi masa magana tun yanzu, ya kenan idan anyi auren?"

Hamna ce tace "Sai ya raina ta mana ya juyata yanda ya ga dama."

Hararanta tayi tace "To ina ruwanki idan ya juya nin? Ai ba ke ya juya ba ko? Kuma dama haka ake so mace ta zama k'asan mijinta."

Wata dariyar shak'iyanci ta mata tace "Lallai ma yarinya, to ki zama k'asan wannan mahaukacin, wallahi wata rana saiya saki kin lashe tafin k'afar shi."

Cikin jin haushi tace "To sai me idan na lashe? Ai k'afar mijina ce."

Hadiza ce tace "Kinga ku bar rigimar nan tashi kije ki fad'a masa."

Mik'ewa tayi ta fito ta wanke hannunta ta d'auki hijabinta ta saka ta fita rai a b'ace, data same shi ta fad'a mishi cewa yayi sai bayan sallah la'asar zasu tafi dan haka su jira, ba tace komai ba face to ta dawo ciki.

*A can gida* kuma ba laifi ana ta bikin lieutenant da Zeituna, anci an sha sosai ana gwangwajewa, kuma daga Ummy har lieutenant babu wanda ya damu da rashin kasancewar Ammar a wurin hidimar, a wurinsu ma hakan ya fi musu kwanciyar hankali a madadin yana nan d'in, rana tsaka babbar mota ta paka k'ofar gidan aka fara shiga da kaya ciki, saida aka shiga dasu tsaf farfajiyar gidan sannan suka nemi inda za'a zuba, Zeinabu ce ta tambaya daga ina suke suka ce Alhajin gidan ne ya aiko su, Hajia suka fad'awa inda ta kira Alhaji ta tambaye shi kayan meye? A cewarshi na amarya ne a ware d'aki na musamman a zuba mata a ciki, nan aka ware mata d'aki ita ma a falon k'asa aka shiga da kayan ciki, Alhaji ne ya umarci Zeinabu da Soueiba su jagoranci al'amarin a gyara d'akin, ba b'ata lokaci suka shiga gyara tare da taimakawar mutane dayawa, cikin k'ank'anin lokacin saiga d'aki ya d'auki saiti sai zuba k'amshi, Hajia data shigo ganin gyaran ranta ya b'ace sosai, dan kayan daya zuba mata ba kad'an bane ba kuma masu arha ba, tana al'ajabin yanda yar aikin gidanta k'azama zata shigo gidan nan a matsayin matar baban d'anta, haka dai aka rufe d'akin ana jiran lokacin da mai shi zata shigo.

Sai bayan sallah la'asar ne Hajia ta fahimci rashin ganinsu Hamna da batayi ba, ta so tambayar Ummy ina yan rainonta suke, amma kuma daga ita har Ummy d'in suna tare da bak'i, hakan yasa tana cin karo da Jamila a falonta ta kalleta tace "Ke ina su Hamna suke?"

Da d'ard'ar tace "Eh to Hajia wallahi nima ban sani ba, tunda safe rabona da su."

Kallon tuhuma ta mata tace "Amma ai jarabawarsu sauka d'aya ne ake ko?"

"Eh Hajia." Ta fad'a kanta k'asa, a kaikaice tace mata "Ki kira min shalele a k'ofar gida."

"To." Ta fad'a tana fita daga falon, a k'ofar gida ta samu Amar tare da abokanansu da duk samarin gidan suna ta hira da raha, sallama tayi suka amsa kafin ta d'ora da "Ina wuni."

Jibril daya kafeta da ido duk yaji haushinta ya cika mishi zuciya saboda masha Allah d'inkin dake jikinta ya bi k'irarta sosai tare da fito mata da komai, kuma wani gyale ne ta sab'a a kafad'a wanda dashi gwara babu, amsawa sukayi inda shi kuma ya bita da harara, suna had'a ido ta k'ura mishi ido tana mishi kallon mamakin meye na harara kuma? Bata d'auke idonta ba taji yace "Me kike nema anan kuma?"

Saisaita kallonta tayi tace "Dama Hajia ce tace na kira mata yah Amar."

Amar ne yayi saurin kallonta yace "Ni kuma? Lafiya?"

Girgiza kai tayi tace "Ni ma ban sani ba." Juyawa tayi zata tafi Jibril ya bita da kallo, abokinshi ya kalla zaiyi mishi magana sai kuma yaga shima ita yake bi da kallo, wani wurga ido yayi alamar jin haushi tare da zabura daga kan kujerar ya mik'e ya bi bayanta, rufe ta yayi ta yanda ba'a ganinta yana binta har suka shiga cikin gidan, sam a tunaninta Amar ne ke biye da ita ashe ko tahowa ma baiyi ba, k'eyar ta taji an zungura ta baya da fad'in "Ke miye haka?"

Juyowa tayi tana dafe wurin ta kalleshi, ganin shine yasa tace "Yah Jibril."

Saida ya matsa daf da ita kamar zai had'e ta ya kalli idonta yace "Baki san da maza a wurin bane zaki fito haka babu hijabi?"

Cikin rashin fahimtar kalamanshi tace "Ban gane ba yah Jibril? Naga biki akeyi a gidanmu ai..."

"Ai me?" Ya katseta da k'arfi har saida ta d'an zabura, nunata da hannu yayi yace "Allah kika sake fitowa waje babu hijabi saina karyaki a wurin nan, maza wuce ciki malama."

Turo baki tayi irin na ranta ya b'ace ta juya a fusace zata shige, hannunta taji ya fizgo ya dawo da ita gabanshi ba tare daya saki hannun ba yace "Wa kike turowa bakin?"

Kawar da kanta tayi gefe bata daina zunto bakin ba, yatsunshi biyu yasa ya jawo leb'en ya murd'e sosai yana fad'in "Ni kike turowa bakin Jamila, saboda na miki magana kisa hijab shine zaki zage ni."

Bud'a idonta tayi da sukayi jawur dasu hawaye suka zubo mata ta kalleshi tace "Wallahi yah ni ban zage ka ba."

Sakin leb'en nata yayi yace "To me kikayi kenan? Meye marabar wannan da kika min da zagi?"

Jin ya saki bakin nata yasa taja baya tace "Kayi hak'uri to."

Juyawa ta sakeyi ta shige har saida ya daina ganinta kad'ai ya koma waje, Amar kuma na zuwa Hajia tace "Ka kira min yaran nan kaji ina suke?"

Da kallo ya bita yace "Wane yara kuma?"

Fuskarta a sake tace "Su Amna mana, har yanzu fa basu dawo daga makaranta ba, kira min su kaji uban me ya tsayar dasu, naga alama yaran nan suna nema su zamar min yan iska."

Cikin rashin jin dad'i ya soma danna wayarshi, da sauri tace "Ka kira lambar Hamna, dan ita ce fitsararriyar cikinsu, duk yanda akayi ita ce zata ja yer uwar koma ina suka tafi."

Danna kiran lambar Hamna yayi amma tana ta k'ara ba'a d'aga ba, dan Ummy data ga wayar ma b'oye mata tayi har ta dawo, dole ya kira Amna amma Hamna na ganin kiran tace mata
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment