Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

_2_

Daga cikin wayar yayi murmushi yace "Karki damu ma naga hasken idaniyar tawa."

Da sauri ta d'auke wayar daga kunne ta juya hagu bata ganshi, tana juyawa dama ta hangoshi yana fitowa daga motar, a hankali ta fara takawa wajen shi sai Maryama dake biye da ita a baya wacce bata san meke faruwa ba, saida taga Iklima ta tsaya wajenshi kad'ai ta fahimci mayenta ne ya sake dawowa, tsaki tayi ta tafi a harzuk'e zata wucesu kamar bata gansu ba ma, da sauri ya tare gabanta da gudu gudu, kallon juna sukayi kafin tace "Malam matsa min a hanya ko."

Kai ya girgiza duk yayi kalar tausayi yace "Ba zan iya ba Maryama."

Tab'e baki tayi tace "To saika zauna kayi gadin wurin ko, ai shi zaka iya na sani dan kamar kaine ka yankewa wahala cibiya lokacin da ta zo duniya."

Murmushi yayi dan kalaman da suka fi wannan ma ya jisu a bakinta, zata rab'a ta wuceshi ya sake tare gabanta yace "Dan Allah Maryama ki saurare ni, wai me ya sa har yanzu idonki sun kasa gane miki masoyinki na gaskiya ne? Maryama me ya sa ba zaki yarda da soyayyar da nake miki ba?"

Da k'arfi tace "Saboda duk maza halinku d'aya ne, kana son samun soyayyata ne saboda kawai kana son jikina, kuma na fad'a maka ni yanzu a ruwa nake, karuwa ce ni, ba buk'atar saika yaudareni kafin ka samu jikina, 2000f cfa (jaka biyu) kad'ai ka bani zan iya kwana tare da kai, saboda ni k'aramar karuwa ce da aka cewa *je ki kya gani*, abinci kawai nake nema da zan ciyar da kaina da kuma 'yata, tunda muma halitta ce ba zamu iya rayuwa babu abinci ba, amma kai ka tsaya sai wahalar da kanka kane kana b'ata min lokacin da rera min wani banzan wak'anka wai kana so na, mtssss."

Tunda ta fara magana ya saki baki yana kallon nata k'aramin bakin, har k'asan zuciyarshi tana birgeshi, yana son kallon kyakyawar fuskarta mai d'auke da tsagu har hud'u, wanda kowane kunci ya samu bibbiyu, amma ta kasa fahimtarshi har yanzu, wani murmushi yayi mai kama da ciwo yace "Yanzu akan jaka biyu kad'ai Maryama kike wofantar da kanki ga mazan da basu san ciwon kansu ba? Maryama akan kud'in da ba zasu iya siya miki ko zanin atamfa ba kike kwanciya da duk d'a namijin daya miki magana? Maryama taya zaki illatar da kanki da gangan alhalin kinsan ba kya da kud'in warakar matsalarki ba?"

Hannayenshi yasa aljihu ya lalaba ya fito da duka kud'in dake cikin ak'alla sun ba jaka d'ari biyu baya ya janyo hannunta ya damk'a mata kud'in a hannu kamar zaiyi kuka yace "Karb'i wannan kiyi duk buk'atunki iya na yau kawai, ni kuma na miki alk'awari kowace safiya zan kawo miki adadin wannan kud'in dan biyan buk'atar ki kawai data 'yarki, amma ki min alk'awarin babu ke babu sake kula wani namijin, ki bani tabbacin zaki kula min da kanki za kuma tsare min mutumcinki, dan Allah Maryama."

A hankali ta raba hannunta da nashi ta sakar masa kud'in a hannunsa tana kallon cikin idonshi tace " Bana buk'atar taimako daga wajen kowa, zanyi aiki da jikina wajen samo mana halak d'in da zamu ci, amma bana son kud'in ka, kad'an d'in da nake samu sunfi min masu yawan da zasu fito a hannun kowane d'a namiji."

"D'a namiji! D'a namiji! Maryama kullum maganarki kenan d'a namiji, wai wace irin ta'sa namiji yayi miki haka da har kika mana kud'in goro haka? Ki fad'a min ni kuma zan tsaya tsayin daka wajen ganin na goge waccen bak'in fantin da waccen mutumin yayi mana, sannan ki bar tunanin halak kike ci ke da yarki, kud'i ne da kika samu ta hanyar sab'awa ubangiji."

Kallon idonshi tayi wanda suka cicciko da hawaye tayi wani murmushi tace "Ba zaka tab'a iya goge wannan bak'in fantin ba, kamar yanda ba zaka iya dawo min da mahaifina dana rasa ba a dalilin wautar d'a namiji irinka, haka kuma ba zaka tab'a sawa mahaifiyata ta kalli idona ba bare harta min magana irin ta uwa da d'iya, dan haka dan Allah Junaid ka rabu dani nayi rayuwata, ka barni na k'arasa k'azamar rayuwa ta a haka ba tare daka tuna min da baya ba, ina farin ciki da hakan."

Murmushi ya mata yace "Magana kawai kikayi akan baya, amma gashi har na iya hango triste (damuwa) d'in da kike ciki, Maryama tu es en colère (kina cikin hushi), kamar fansa ce kike son d'auka ko kuma dai hushi ne ke sakaki abinda kikeyi."

Cikin k'ok'arin b'oye damuwarta tace "Laise moi en paix (ka bani lafiya)."

Wucewa tayi yabi bayanta da kallo, Iklima ce ta zo wucewa ta gabanshi ya bata kud'in nan yace "Dan Allah Iklima ki rik'e wannan kud'in kuyi wani anfanin dashi, sannan ki sanar da Maryama irin son da nake mata, wallahi ko misk'ala zarra bana da niyyar cutar da ita, aurenta nake so nayi, yau d'in nan har nayi magana da magabata na, kuma na samu amincewar kowa, ita kad'ai ta rage min na samu ta ta amincewar, na rok'e ki Iklima ki taimaka min na shawo kanta."

Da mamaki ta kalleshi tace "Kana nufin ka sanar a gidanku zaka aure ta?"

Cike da tabbatarwa yace "Na sanar mana."

"Kuma sun amince ka ce?"

"Sosai ma, wallahi da gaske nake Iklima."

Ajiyar zuciya ta sauke tace "Kuma ka fad'a musu irin matar da kake son aure?"

"Na fad'a musu Iklima, amma ban fad'a musu tana da 'ya ba, abu mai mahimmanci su san wacece zan aura."

Zata wuce yace "Kud'in fa?"

Juyowa tayi tace "Ka barshi kawai mun gode, idan na karb'a zamu samu matsala da Mari ne."

Wucewa tayi shi kam yabi bayansu da addu'ar shiriya, cikin sanyin jiki kamar kullum ya shiga motarshi ya kamo hanyar gida dan babu abinda zai tsinta a wajen.

➡️➡️➡️➡️➡️➡️➡️➡️


Su Hamna yan mata sune a falon sama tare da yara ta kunna wak'a a wayarta sai rawa take yaran na biyarta a baya, Amna na zaune tana kallonsu tana dariya, sai Umminsu Ammar da ita ma take kallonsu tana dariyar tare da mahaifiyar Junaid, a gefe ma k'anwar Junaid ce *Jamila* duk da ba ita ke bi mishi ba, amma ita ce daidai su ma'ana warin haihuwa, dan yayarta *Umaima* bata cika son hayaniya ba itama, tana da tsatsauran ra'ayi, ita d'in ce wacce suka zama k'awaye da ita suna ta kallonsu, wannan hayaniyar ce tasa Ammar daya dawo falon ya zauna yana danna wayarshi yayi tsaki yafi dubu, in dai yace yaje yanzu dan yayi musu magana Ummi za tace ai zai takura ma yaranta ne, kuma yana da tabbacin in yaje sai ranshi ya sake b'aci saboda *kankana* *(sunan daya sakawa Hamna kenan saboda soyayyarta da kankana*😂), su kam basu san tsiyar da yake ba sai rawarsu suke kwasa, wannan dum-dum d'in da wajen ke amsawa yasa yake jin kamar benen zai fad'o mishi a kai, wani wawan tsaki ya sake ja yace "Wannan yarinyar wallahi saina karya mata k'afa ta yanda gobe ba zata iya rawar ba ma, ayi yarinya kamar dujal ne ya haifeta, mtssss."

Wasu lambobi ya danna saiga lambar Amna ta bayyana a wayar tashi, kira ya aika mata da shi ta d'auka cikr da nutsuwa da fad'uwar gaba dan ita har ga Allah tana tsoronshi, duk da akwai banbanci tsakanin Hamna da Amna mai yawa, domin kuwa Hamna na da tsoron k'ananun dabbobi irun su k'adangare, kyankyaso, tsaka dacdai sauransu, Amna kuma bata tsoron wannan halittu kamar yanda take tsoron Ammar, Hamna kuma bata da zuciya da sanin ciwon kai, dan duk maganar da zaka fad'a mata komai zafinta saira karkad'e tace ko a kwalar rigarta, shiyasa duk maganganun da Ammar ke fad'a mata bata jin zafi, sai dai kuma akwai yab'a magana ita ma, dan tsoron da Amna ke masa ita bata mishi, idan taga ta shiga hannunshi kad'ai take tsorata da razana, sab'anin Amna kuma da magana ke mata mugun zafi, tana da zuciya da hushi, a tak'aice ma dai ita masifaffiyar amma fa ga wanda ya tab'a ta, idan kuma ka ganta zaka d'auka ko hannu ka saka mata a baki ba zata ciza ba, amma idan tana fad'a ko tayi zuciya to babu kyau, cikin sanyin murya ta amsa da "Na'am yaya Ammar."

Sai kace a gabanshi take saboda yanda ya wani sake had'e rai murya k'asan mak'oshi yace "Ki fad'awa yarinyar nan ta kashe mana kid'an nan, idan kuma na samesu a nan ran uban kowa saiya b'ace."

Yana fad'a ya kashe kiran tare da ci gaba da abinda yake, Amna kuma kallon wayar tayi kafin ta kalli Hamna tace "To shakira ya isa haka ko tunda *boss* yace a kashe wak'ar nan, da alama kuna damunsa ne."

Kallonta Hamna tayi masha Allah kam kyakyawa ne ajin farko, suna da diri da k'ira gwanin ban sha'awa, amma duk da haka Hamna tafi haske sosai da tsayi kad'an, tab'e baki tayi tace "Shine ya kiraki kenan?"

Da ido kawai ta mata alamar eh, ci gaba tayi da rawarta tace "Ki kira ki fad'a masa bai isa ya katse mana jin dad'in mu ba, dan haka yanzu muka fara."

*Hajia Zeinabu* (mahaifiyar Junaid) ce tace "Um um fa Hamna, hanyar lafiya abita da shekara, tunda yace ku kashe to ku kashe, ko kuma ki jasu kuje d'akin ku sai kuyi acan."

Wata kyakyawar mata mai k'aramin jiki ce fara kuma doguwa ce tace "Saboda yace baya so shikenan sai a daina? Me zai hana ya fita waje tunda namiji ne shi, amma yana cikin gida kamar wata garar kunya."

Zeinabu ce tace "Da dai kin basu shawara su koma ciki zaifi ai."

Hamna ce ta kalli yaran tace "Kai mu ci gaba da nishad'inmu, kunsan boss ba fara'a yake ba bare maganar nishad'i, shi ya sa yake kishi da duk wanda yake yinsu."

Tana maganar ne tana amma sai taga yaran kowa yayi zaune tare da mak'alewa wuri d'aya, tab'e baki tayi tace "Sai kace mala'ika nr shi daga ya turo sak'o ta waya amma duk kun tsorata."

Kallonta ne ya kai kan Amna data kafeta da ido, cikin dubara Amna ta d'ora hannunta a bakinta da yatsa d'aya take mata nuni da k'ofar shigowa falon, da k'yar ta fahimci abinda take nuna mata ta juya dan ganin ko meye, ai ko ido cikin ido suka kalli juna ita da Ammar wanda yake tsaye k'ik'am ya cije gefen labb'enshi na k'asa, ai da gudu Hamna ta koma bayan Ummi tana mata rad'a wai "Dan Allah Ummi ki bashi hak'uri mu samu ya bar gidan nan."

Ummi da tunda ta ganshi ta had'e rai kamar dai shi kalloshi take sosai, ganin yanda take kallonshi yasan sai ranshi ya b'ace in yayi magana, dan k'aramin aiki ne a gurin Ummi ta zageshi a gabansu har ma tayi yunk'urin marin shi, dan haka yayi k'wafa ya juya ya bar d'akin, yaran na gabin haka suka daka tsalle da shewa wai ya tafi bai dake su ba.

Yana barin nan kai tsaye asibitinsu ya wuce mai sunan *Clinik Aminci*, (na canza mata suna saboda kar na saka na ainahin sunan familyn ya fito fili), yana zuwa ya fito daga mota ya tunkari shiga ciki, a babban falon da mutane ke zama ya samu duk gurin zaman an cikeshi, kuma yana da tabbacin wanda yake da rendez-vous (appointment) da su ne, wata irin sallama ce yayi wanda na farko kawai yaji shi sai wanda suka ga bakinshi ya motsa, dan ranshi b'acewa yake idan ya zo asibitin ma, a ganinshi da yanzu watak'ila yana filin daga suna bada wuta, amma an zaunar dashi yana tambayar lafiyar mutane (mutum baya sanin abinda yake, haka kuma baka sanin mahimmancin abinda ke hannunka saika rasa shi), malamar asibitin dake zaune akan babban teburi wacce ita ke kula da wanda zasu shiga da kuma fara duba lafiyarsu, kallonshi kawai tayi dan ko ta gaishe shi ma ba amsawa zaiyi ba, tsaye yayi gabanta ya sauke jajayen idonshi akanta yace "Zan shiga, su bi layi da kyau, a kuma dinga shiga da hanzari saboda gudun b'ata min lokaci."

"Ok docteur." Ta fad'a tana bin bayanshi da kallo, tab'e baki tayi tana gunguni tana fad'in "Kamar dai ba *Sa'ada* ce ta haife shi, ita faran faran da mutane, shi kuma sai shegen tsamin rai, Allah ya sawak'e maka."

Yana shiga ya mayar da k'ofar ya rufe, makullin mota da wayarshi ya aje akan tamk'amemen teburin dake gabanshi tare da zagayawa wajen wani d'an dogon k'arfe ya zago fara kuma doguwar rigarshi ya saka, abin sauraren numfashi ya d'auko kamar zai saka a kunnuwa sai kuma ya sagalashi a wuya, kujera ya ja ya zauna ya gyarawa abin auna hawan jini zama, wani k'aramin coffre ya bud'e ya d'auko wani farin gilashi ya saka a idonshi, masha Allah, abinka ga kyakyawa kuma farin mutum, sai yayi kyau cikin shigar kamar ka daga da bredi, matsalar d'aya ita ce d'aurewar fuskar nan da babu annuri a cikinta, wani babban littafin ya d'auka ya ciro alk'alami a jikin rigarshi ta ciki ya fara rubutu, ba jimawa da fara rubutun kuma aka k'wank'wasa k'ofa tare da bud'awa aka shigo,sam baiyi alamar yasan da zuwan mutum ba saboda ko d'agowa baiyi ba, har saida matar ta zauna tare da kafeshi da ido, saida ya gama abinda yake ya d'ago a hankali ya sauke ido akan matar na yan dak'ik'u, hannu ya mik'o mata alamar ta bashi katinta da kuma takardun rahoton lafiyarta, da sauri ta mik'a mishi saboda ita tsoro ma ya bata, saida ya gama dubawa da rubuce rubuce bai kalleta ba yace "Ki kwanta kan gadon can."

Tashi tayi ta nufi wajen gadon da aka keyawa ba'a iya ganin wanda ke ciki ta kwanta, tashi yayi ya fara dubata na wasu mintoci kafin ya dawo ya zauna, dawowa tayi ta zauna ita ma tana kallonshi yana ci gaba da rubutu, ya jima kafin ya mik'o mata takardun sai takardar siyan magani yace "Wannan takardar ki bawa wannan likitar dake zaune."

Wata takardar ya mik'o mata yace "Wannan kuma asiyo wad'annan magungunan yanzu, dukansu kina buk'atarsu domin zasu taimaka miki."

Mayar da kanshi yayi k'asa ya fara rubuce rubuce, tashi tayi ita kuma ta fita jiki na rawa dan tayi abinda yace, da haka Ammar yake duba duk wani majinyaci daya shigo har saida lokacin tashinshi yayi, ak'alla awa biyu ya d'auka a asibitin kafin ya tattara ya nufi gida a gajiye, wasu mintuna ne suka kawo shi gida, yana zuwa kuma a k'ofar gida ya samu Hamna tare da wata k'awar ta akan moto da alama tafiya zatayi, tsaki yayi ya shige ciki kai tsaye kuma b'angarensu na samari ya wuce, tun a falon ya tarar da su Amar da su Junaid, kallonsu kawai yayi ya nufi na shi d'akin, Junaid ne yace "Likita bokan turai, baka so a mutu baka so a zauna lafiya, daga asibiti ake halan?"

Tsaye yayi ya rik'e k'ugu ya kalleshi kamar zaiyi magana sai kuma ya wuce, Jibril ne yace "Oh mu 'yasu, mu dai mun shiga uku kam, jama'a namiji da jan aji da yanga kamar wata sabuwar bazawara, wannan naga mai auren shi a duniyar nan."

Dariya Amar yayi yace "Za kuwa ka ganta da idonka, ai irinsu kuma Allah yake had'awa da masu shegen surutu."

Karaf Jibril yace "Kamar irinsu Hamna ba."

Wata harara Junaid ya wurgo masa yace "Ka rufa mana asiri kafin zaman d'akin nan ya gagare mu, yana jin wannan maganar a bakinka Allah saiya maka tiyata a baki."

Dariya suka saka inda suka ci gaba da tattaunawa cikin nishad'i, amma abin haushi duk hirar dangin nan da suke Ammar na d'aki na jin hayaniyarsu yayi shiru har bacci ya d'auke shi.


*Washe gari*

Jiniyar motoci ce ta tashi wasu daga cikin mutanen gidan, daga ciki har da Ammar da Hamna da kuma Amna, sanin ko waye yasa Hamna ko suturta jikinta bata tsaya yi ba daga kayan baccin dake jikinta ta fito, da gudu take saukowa daga matakalar tana fad'in "Abbanmu ya zo, Abbanmu ya zo, Abbanmu ya zo."

*GVR* de Maradi (gwamnan Maradi) *Harouna Suley Hassan Gaga* (Gambo) kenan, mahaifin Hamna da Amna, wanda suke kwashe watanni basu saka shi a ido ba saboda yanayin aikinshi, yanzu haka ma yayi sammakon zuwa ne sabida k'arfe *09:00* zai halarci wani taro na k'addamar da wata sabuwar gidauniya da za'a bud'e, shiyasa ya zo dan ya samu ko da awa biyu ne da iyayenshi, 'ya'yanshi wanda yan uwanshi ke kula dasu da kuma sauran 'yan uwa, kuma bayan rabuwarsu da mahaifiyar su Hamna ya auri wata mata mai sunan *Salamatou*, yar asalin garin Niamey ce bazabarma (zarma), suna tare da ita acan babban birnin niamey, shiyasa ganinshi ma ke zama aiki, dan ko a waya ka kirashi sai ka taki sa'a kake samunshi.

Masha Allahu, gaskiya 'yan biyu akwai kyau kuma kyauta ce ta Allah, uwa uba kuma 'yan uku, cikin d'an takon hanzari yake shigowa falon tare da yi wa masu tsaron lafiyarsa alamar su jira shi, Hassan da Hussein da suka fito cikin shirin fitarsu kowane da kayan aikinshi ne ke tunkarowa suma saboda ganin d'an uwansu rabin jikinsu, sak iri d'aya su ukun, kayan jikinsu ne kawai ya banbanta su, sai dai kuma shi Gambo ya d'an fisu kumari, ganin irin farin cikin dake kan fuskokinsu yasa ya yanke shawarar k'in fad'a musu abinda ya kawoshi, zaiyi shiru har kowa ya gama tafiya wajen aikinshi, kafin su dawo kuma yasan ya bar garin, rumgume juna sukayi dukansu saboda farin ciki, ba jimawa suka raba jikinsu suna kallonshi, Hassan ne ya d'an bugi tunbinshi yace "Meye haka kai kuma? So kake ka zama luti ka barmu, wato kana so a dinga cewa kaine babba garemu ko?"

Murmushi yayi ya gyara babbar rigarshi ta shaddarshi ruwan madara wacce ta dace da shi yace "Ai babba babba ne, kaifa ka fara zuwa duniyar nan kafin mu, kaga kuwa dole mu baka girmanka."

Cikin had'add'en fuskar da babu annuri Hussein dake gyara d'amarar shi ta kakinshi na soja yace "Girman guda nawa ne, ko na minti biyar fa bai kai ba."

Kallonshi Hassan yayi ya kai hannu yana k'arasa sakawa Hussein d'in mab'allan rigarshi kamar wani yaro yana fad'in "Soja mazan fama, ai ka ma rik'e girman nawa na bar maka."

Dukansu ne suka juya saboda muryar Hamna dake kiran Abbanmu ya zo suka kalleta, ganin riga da wando ne a jikinta na bacci yasa Gambo daka mata harara har yana mata nuni da yatsa yace "Maza kije ki canza kayan nan, wai ke yaushe zakiyi hankali ne?"

Cak ta tsaya tare da turo baki gaba, juyawa tayi harda bubbuga k'afa ita bata so ba, Hassan ne yace "Daga zuwanka fa ba zaka fara takura min 'ya ba."

A lokacin Hussein na gyara zaman jar hularsa mai d'auke da lambar girma yace "Idan ya takurata ka kira ka fad'a min, zan nuna maka inda nake ajiyar bindiga ta."

Yana fad'a yasa kai zai nufi d'akin Hajia dan gaisheta cikin wani irin tako kamar wani ingarman doki, (ni fa sai lokacin ma na ce duk d'abi'un shi kamar Ammar, ko kuwa Ammar d'in ne kamar shi) da sauri Gambo yace "Ina kuma zuwa bayan na zo?"

Ko juyowa baiyi ba yace "Zuwanka kuma ba zai dakatar dani daga tafiyar nan da zanyi ba."

Wata tattausan murya ce daga bayansu aka ce "Yallab'ai ga shayin."

Hassan ne ya juyo ya sauke idonshi akan kyakyawar matarshi, hannu yasa ya karb'a yace "Nagode uwarsu Ammar."

Murmushi ta sakar masa mai tsadar gaske tare da kallon Gambo tace "Sannu da zuwa gwamna, ya hanya?"

Da fara'a ya amsa mata da "Alhamdulillah madame, ya muka same ku?"

"Lafiya lau muke? Ya mutan can d'in?"

"Lafiya lau, ya 'yan rigamarki (su Hamna ba)?"

Murmushi tayi tace "Yara na ai sun girma yanzu sun daina rigima."

"To zan gani dai, dan banga alama ba sai dai ko Amna."

Hassan ne ya mik'a mata kofin shayin tare da karb'ar hularshi kalar shud'i ya d'ora akai ya daidaita mata zama yanda a dace, (ikon Allah, idan dai na fahimci wani abu wato duk gidan nan boko ce ta yanke musu cibiya, lallai wasu kayan sai amale), *lieutenant Hassan Suley Hassan Gaga* babban douane na garin Maradi, murmushi ya sakar mata yace "Mu zamu fita kuma sai Allah ya mana dawowa."

Murmushi ita ma tayi tace "To muje na raka ka ko, ko ba kya son addu'ar tawa yau?"

Murmushi yayi daya bayyanar da hak'oran shi yace "Zan iya hak'ura da tenue (kaki) na amma ba dai addu'ar ki ba."

Wucewa sukayi ya dafa kafad'ar Gambo yana fad'in "D'an lukuti saina dawo."

Murmushi kawai yayi yace "A dawo lafiya, madame ke ba zaki tafi wajen aikin ba yau?"

Juyowa Hassan yayi yace "Ai saita fara iza k'eyata gaba take tafiya."

Dariya sukayi suka fice shi kuma ya nufi d'akin Hajia dan ya fara kai mata gaisuwa, Hamna ce ta sake fitowa ta d'oro hijab akan kayan baccinta sai Amna a bayanta, kallonsu yayi da sauri Amna tace "Bonjour (ina kwana) Abba."

"Bonjour." Ya fad'a yana tafiya ya d'ora da "Attend moi ici (ku jira ni anan), je salut mes parents (zan gaida iyayena)."

Amna ce dai ta amsa da "Ok Abba."

Yana isa a lokacin kuma Hussein ya fito, sallama ya mishi ya fito da zuwan saiya dawo, ganin su Hamna zaune a falon yasa ya kallesu yace "Yarana ya dai?"

Gaishe shi suka fara yi, kafin suce wani abu kuma Ammar ya shigo ba sallama, hasalima fuskarshi had'e take saboda yaga kankana a wurin, amma yana ganin kawunshi sai kawai ya k'ame wuri d'aya tare da sara masa wai shi a dole soja ne, shi ma colonel d'in sara masa yayi tare da dafa kafad'ar shi yace "Bien réveillé (ka tashi lafiya)?"

Cikin k'amewa irin ta sojoji ya amsa da "Oui chef."

Kamar wanda suka had'u a filin daga haka shima colonel d'in yace "Da kyau, yanzu kaje ka fara da motsa jiki, kar ka ci abu mai nauyi sosai, sai ka wuce wajen aiki, compris (ka fahimta)?"

Da k'arfi ya amsa da "Tout de suite (yanzu kuwa) chef."

Sai lokacin ya saki jikinshi tare da d'an fad'awa jikin kawun nashi suka yi gaisuwa cikin nutsuwa, sai lokacin yace "Tonton (kawu) na d'auka hutu ka zo mana ai, ya kuma zaka fita yanzu?"

Ba tare daya saki hannunshi da sukayi musabaha ba yace "Ba jimawa zanyi ba, wani taro ne zanje anan *gazawa*."

Ba karsashi yace masa "Saika dawo tonton."

Fita yayi daga falon ya wuce inda zashi, Ammar kuma juyowa yayi inda su Hamna suke zaune, ai yana kallonsu sai kuwaHama ta bushe da dariya, Amna baiwar Allah tana so ta dara amma ba dama, k'ara tsumimiye fuska yayi yana kallonta baice komai ba, ita ko dariya take shek'awa kamar zararra harda tashi daga kan kujerar ta koma bayan Amna tana fad'in "Oui chef, hhhhhhhhhh, tout de suite chef, wayyo cikina harya k'ulle, yer uwa."

Ta fad'a tana tab'o Amna ta ci gaba da fad'in "Allah dai wani ya zare a gidan nan saboda bai samu abinda yake so ba, kullum shine fad'in, oui chef, a vos ordres chef, caca-caca, kai haba ina."

Kwabar dake gefenshi ya kallasai kuwa yayi sa'ar samun faranti na tangaren, d'auka yayi ya saita daidai kan Hamna zai jefa sai kawai kawunshi Gambo ya fito tare da Hajia da kuma Alhaji, sauya akalar farantin yayi cikin dubara ya aje shi mazauninshi, Hamna na ganin haka ta mishi gwalo tare da kwaso wata shegiyar shoki ta watso mishi a fuska tana fad'in "Eh, eh-eh-eh shokiii."

K'wafa yayi a zuciyarshi kawai ya juya ya bar d'akin, lokacin kuma Hajia Husseina da Soueba suka fito tare suma, da haka har falon ya sake cika da iyalin Gaga yara da manya, saidai kowa yana haramar tafiya sabgar gabanshi ne, yara da matasan école (school) suka nufa, sai samarin dake fitowa cikin nasu shirin tafiya ma'aikatunsu.

Hamna da suka saka mahaifinsu tsakiya sai shagwab'a suke masa, Ammar da Amar ne suka shigo tare, k'are musu kallo Hamna keyi tana son banbance boss da kuma Amar a ciki, dan dukansu riga ce chemise a jikinsu kuma fara k'al, kuma dukansu basu b'alla botira biyu ba na sama, haka ma wandon jikinsu mai duhu ne sai dai ba kala d'aya ba, zaka fahimci hakane idan sun matso kusa da kai, sannan takalmin k'afar su iri d'aya ne da
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment