Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ko babu laifin ma zai iya kunyataka ya tsinka ka a cikin jama'a, yau ita ce a k'irjin shi a matsayin mata? Bata tab'a kawo haka a ranta ba, dan a wajenta abune da ba zai yiwu ba, tayi tunanin tsaf zai nuna ta yace baya sonta, ta d'auka zai kalleta ne yace Allahya tsare shi da aurenta. Kai ita kanta fa taso tace bata son shi, amma ganin shi bai furta ba yasa ta yin shiru da fammun d'inta, dan idan har ta kuskura kalmar bana sonka ta fito daga bakinta, to tsaf zai iya tisata a gaba da tab'arya yace sai yaji dalili, wannan dalilin ne ita kuma yasa bata iya fad'a ba. Tana wannan duniyar taji ya d'ago kanta ya kalleta yace "Kin iya girki ne dama?"

Kallonshi tayi a sagale, na iya girki? Me yake nufi? Kafin ta bashi amsa ya nufi wajen abincin yana fad'in "Na ga dai waccen kakar taku tafi damuwa da al'amarin tsaronku ta yanda bata barinku fita, amma kulawa daku kuma wannan bata ma san me takeyi ba."

Bin bayanshi tayi ya zauna kan kujera ita kuma ta fara zuba mishi farar shinkafar da tayi warwara gwanin kyau, sai kabeji data zagayeta da su sannan ta kuma zagayeta da karas wanda duk ta gurzasu, sai dunk'ulallen naman data jera shima kafin ta zuba sauce d'in albassar a tsakiya, tab'e baki yayi ya janyo farantin ya d'auki cokali ya kai lomar farko, kallonta yayi ya mata alama da hannu πŸ‘Œcewa komai yayi, murmushi tayi ta ja kujera ta zauna cikin d'ard'ar tace "Ai ba ido kawai Hajia take saka mana ba, har yanda zamu kyautata rayuwarmu tasa an koya mana."

Murmushin baki da hankali ya mata ba tare daya kalleta ba, saida yayi loma bakwai har ta manta da zaiyi magana sannan taji yace "Amna."

"Um." Ta fad'a tana mayar da hankalinta kanshi, saida ya kalleta yayi kalar tausayi sosai yace "Dan Allah ki dinga girka min abinci kullum ina ci, ina yawon zama da yunwa, ki min wannan alfarmar kinji?"

"To amma yah Ammar me yasa baka san cin abinci?"

Kallonta yayi babu annuri a fuskarshi, har zai bata amsa sai kuma ya canza maganar yace "Bana da wanda zai rik'a bani a baki ne."

Sunkuyar da kai tayi a zuciyarta tace "Uban wani kakan wani ka zauna sai an baka abinci a baki? Lallai ma mutumin nan."

Kafin wata magana ta sake shiga tsakaninsu aka bud'a k'ofar d'akin aka shigo, dukansu kallon k'ofar sukayi a tare, da sakin fuska Amna tace "Autan Ummy ne?"

Bai ce komai ba kamar yanda bai saki fuskarsa daga had'ewar daya mata ba, saida ya zo inda suke yace "Zuba min nima zan ci."

Murmushi tayi tana kallonsa ta fara k'ok'arin zuba masa tana fad'in "Autan Ummy kamar ranka a b'ace? Waya tab'aka ne?"

Kujera yaja zai zauna Ammar ya sauke mishi jajayen idonshi, kallo ne da zai iya saka fitsari a wando, kallo ne dake tattare da aika sak'onni dayawa, ba kayi sallama ba, baka gaishe da mutane ba, sannan kana wani d'aurawa mutane fuska, baka ga wurin zama ba sai a nan? Sannan me ma ya kawo ka?πŸ˜‚ To bashi Amsa Kamal.

Kallon Amna yayi wacce ita ma ta kalleshi dan ta lura da kallon daya mishi, murmushi ta sake yi tace "Wai waya tab'a ka ne Kamal?"

Turo baki yayi yace "Tonton Gambo ne zai koma Niamey yanzu, shine na ce zan bishi Hajia tace a'a, wai sai dai su tafi da Hamna."

Dukansu sake bashi hankalinsu sukayi inda Ammar ya d'ora da cewa "Saboda me?"

"Nima ban sani ba." Ya fad'a yana zaunawa kan kujerar, kallonshi Amna tayi da mamaki tace "Me yasa Hajia zata tura Hamna can kuma?"

"Ba haka kawai tayi ba." Yana fad'a ya mik'e da hanzari zai bar falon, da sauri Amna ta bi bayanshi tace "Yah Ammar zan iya zuwa na ga yer uwata? Wallahi nasan ba'a son ranta zata je ba, daga ni har ita babu mai son zuwa wajen Abba saboda tanti Aissata ba k'aunarmu take ba."

Hannunta ya kamo kawai suka fita, ta k'ofar dake cikin gidan suka shiga, kai tsaye falo suka nufa ba tare daya saki hannunta ba, suna shiga Amna tayi sallama amma banda gogan, hankalinshi na kan mutanen dake cikin d'akin yana kallonsu d'aya bayan d'aya, a hankali ya saki hannunta ta gaishe da mutanen wurin, kowa ya amsa amma banda Hajia dake kallonta a hargitse, kallon mahaifinsu tayi dake zaune kan. kujera tace "Abba yanzu zaku tafi?"

"Yanzu zamu koma auta ta, amma tare da Hamna zan tafi." Duk yayi maganar ne jiki a sanyaye, da d'an mamaki tace "Amma Abba me yasa zaka tafi da ita yanzu? Kai fa kake cewa kafi son zamanmu anan."

"Yanzu kuma ya sauya, zai tafi da ita tunda anyi hutu, kuma ba aure ne da ita ba tunda ta k'i aure."

A tare suka kalleta ita da Ammar, kallon ladabi da tsoro ta mata, yayin da shi kuma ya bita da kallon to sai akayi yaya kuma? Hajia kifa kiyaye ni, meye na wani d'auketa daga nan d'in? Jin bbu wanda yace wani abu yasa Amna ta tunkari d'akinsu na sama da sauri dan ta samu Hamna, tana shiga ta sameta zaune bakin gado da alama kuka take, k'arasawa tayi ta zauna kusanta ta dafata tace "Rabin jikina, kuka kike? Na sani dama ba zaki so tafiya ba, amma me yasa Hajia tace a tafi dake?"

D'an d'ago kanta tayi ta kalleta tace "Nima bansan dalilinta ba rabin jiki, kawai dan bata son gani na a gidan nan."

Da sauri tace "A'a rabin jiki, karki fad'i haka mana, kinfi kowa sanin yanda Hajia bata san muyi nesa da ita, ina ga dai ko dan baki amince da auren yah Junaid bane."

Tab'e baki tayi alamar ko oho, jin ba tace komai ba yasa Amna mik'ewa tsaye ta kamata tana fad'in"Taso, tashi muje ki bata hak'uri dan Allah, ba zan yarda ta rabani dake ba a lokacin da nafi buk'atarki a kusa da ni."

Mik'ewa tayi cike da kasala tace "Amna ba zata hak'ura ba, kefa kin sani."

Janta tayi da k'arfi suka nufi hanyar fita, a lokacin ne wani tunani ya zo ma Hamna, a take sai taji tana buk'atar yin nisa da gidan ma ko dan yer uwarta, dan har yanzu bata iya kallon k'wayar idonta idan ta tuna tasan mijinta kafin ita, duk da tursasata akayi amma abun kunya ne a wurinta. Sai dai kuma Ummy na buk'atar zamanta anan ko dan abinda ke cikinta, *ciki?* Shine abinda ta sake maimaitawa, hawaye taji sun taho mata a wannan lokacin, bata ankara ba sai ji tayi sua sauka kan matattakala suna sauka k'asa, yanayinta ne ya sake canzawa gaba d'aya, sanyin jijiyoyinta suka rub'anya ta yanda suke daf da tsinkewa, tun daga nesa take kallon mutanen dake k'asa, hawayen ne ke ci gaba da zubo mata saboda tasan a halin yanzu yer uwarta ba zata ji dad'in abinda zata mata ba, dan kuwa k'aryata ta ne zatayi a gaban mutane, tasan za taji zafi sosai sai dai zata fahimci dalilinta, sai dai kuma bata san yaushe ne ba?.

Tunda suka taho ya k'ura mata ido, kallon k'wak'waf ne yake mata na son gano yanayin da take ciki, sai dai garin kallon nan na jaraba ne ya fara hango wani abun, canji ne sosai wanda shi dai bai santa da shi ba, amma ganin baida hujjar da zai tabbatarwa kanshi yasa shi faa fafutukar neman hujjar, bai daina binta da wannan kallon mai firgita wanda ake ma ba suka k'araso, Amna na rik'e da hannunta suka tunkari wurin Hajia da niyyar mata magana, amma sai Ammar yasha gabansu kamar sojon da zai bincikesu, idon Hamna ya kalla sosai tare da mata wani tuhumammen kallo ya nuna idonta da yatsa kamar zai tsoneta yace "Sai kace wata mai ciki sai k'yak'yabta ido kike, ko tafiyarce ba kya so?"

Wandon dake jikin Ummy ne kawai ya mata shamaki da saurin b'allowar fitsari, sai dai ta tabbatar kayan cikinta zamansu ya sauya, dan juyawar da sukayi mota ce kawai za tayi wannan harurun da kai yayin da ta jirkice ta fantsama katantawwa da kai. Hamna kuma numfashinta ne taji ta nema ta rasa, hakan ne ya haddasa mata rufe ido sai k'wayar idonta dake juyawa, Amna kuma kallonshi tayi ba tare da tunanin komai ba tana murmushi, dan ita yanzu ta fara fahimtar mijin nata, sannan da yace yana sane yake komai yasa tayi damarar shanye duk wata katob'ara tashi, kowa madale wajen abinda yayi tunani kenan ba Hajia kad'ai ba, wato rashin kunyar ce ko? Kamar a mafarki sai gani sukayi yasa hannu ya tallaba kanta yana k'ok'arin bud'e mata ido, dan shi dai a matsayinshi na likita duk da ba abinda ya karanta ba kenan, amma da kallo da kuma ji zai iya gane larurar wani majinyacin, yana cikin kiciniyar nan Ummy dake kallonsa kamar mahaukaci ganin yana neman b'alle mata lik'i yasa ta tahowa da k'arfin tsiya, k'arfin da yafi k'arfin kuzarinta da d'ab'iarta, tana zuwa gabanshi ta d'aga hannu iya k'arfinta ta wanke fuskarshi da mari.

K'arfin marin yasa shi duk'ar da kai gefe d'aya dafe da kunci, ya jima haka yana sauraron masifar da Ummy ke mishi, cikin hargagi da zautuwar tunani take fad'in "Baka da hankali ne? Wannan wace irin fitsara ce? A gidan uban wa ka koyo wannan tarbiyar? Anya Ammar kai d'ana ne kuwa? Ka sani fa a hanyar aure na same ka ba da zina ba."

Hannun Hamna ta kama da niyyar barin wurin taji Hajia tace "...


*Saboda farin cikin isar da yarinyata lafiya d'akin mijinta.*πŸ’ƒ
09/09/2020 Γ  17:58 - Ummulkhairi: πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨
*BADAK'ALA*
πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨

*Labarin Gaske*

*NA*

_SAMIRA HAROUNA_

*Litattafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_ (sai Allah)
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura...)_
*14* _BADAK'ALA..._

*SADAUKARWA GA*

πŸ‘¨β€πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘¦ *AHALI NA*πŸ‘¨β€πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘¦

©🌠

*πŸ‡³πŸ‡ͺTAURARIN NIGER..*
```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)```

βœͺ{T . N}βœͺπŸ“–πŸ–ŠοΈ

https://www.facebook.com/Taurarin-Niger-100155928500614/

_Bismillahir rahamanir rahim_

_39_


Hajia ce tace "Malama meye na tunzura haka? So kike ki rufe bakinmu mu kasa fad'ar rashin kunyar d'an ki? To dawo da ita tafiya zasuyi."

Juyowa sukayi suka tsaya sai rarraba ido suke alamar rashin gaskiya, a lokacin ne Hajia ta kalli Hamna da kyau, kallabi ne jikinta wanda bai rufe mata jiki ba, tabbas Hajia tasan ita da Amna ba ma'abota bras bane, dan gabansu a cike yake kuma pampam dashi, su Umaimah ne sarakan sawa kullum, amma ganin yau sun mata wata irin cikowa kamar mai ciki yasa ita kanta sai taji ba dan Ammar ba mutuminta bane data yarda da abinda ya fad'a, Ummy dake cike da razani da tsoro tuni ta ga kallon da Hajia ke mata, da sauri tace "Hajia kinsan shi da shirmen banza, bai san me yake fad'a ba wani lokacin, komai ya zo bakinshi saiya fad'a."

Amna ce ta kalli Ummy ranta a matuk'ar b'ace na marin data wa mijinta, d'an k'aramin iska ta furzar irin na rashin jin dad'in nan kafin ta matsa kusa da Ammar da har yanzu ya k'asa d'agowa, a hankali ta kama hannunshi tana kallonshi, ganin bai kulata ba yasa ta kalli Hajia tace "Hajia dan Allah kiyi hak'uri ki barta anan, wallahi bata san tafiya ita ma."

Wani kallo ta mata tace "Ita ta fad'a miki bata so? Ko kin ari bakinta ne kin ci mata albassa?"

Kallon Hamna tayi tace "Na sani bata so, kuma gata nan ku tambayeta."

Mahaifinsu ne yace "To ko bata so ba dole ta hak'ura ta so ba tunda Hajia tace a tafi da ita."

Hajia ce ta kalli Hamna tace "Ke kika fad'a mata ba kya son tafiyar?"

Kallon Hajia tayi ta kalli Amna da ita ma ta kafeta da ido, kallon kiyi hak'uri ta mata sannan ta kalli Ummy dake kusa da ita, a k'wayar idon Ummy ta hangi abinda ta kasa fahimta, shin tana son tafiyarta ne ko kuma a'a, rashin sanin amsa yasa ta kalli Hajia ta sunkuyar da kai tace "Ni ban fad'a mata ba, ina so na tafi tare da Abba."

Kallon mamaki da takaici Amna ta mata, me yasa za tayi haka? Cikin jin haushi tace "Amma ai ni nasan ba kya son tafiyar, kuma idan kin manta na tuna miki, kina shirye shiryen tafiyarki koyon kwalliya ne."

Idan har ba bak'ar magana ta fad'a mata ba tasan ba zata rabu da ita cikin sauk'i ba, dan haka tace "Ni bana son koyon wata kwalliya, wajen mahaifina zan koma da zama."

Murmushin rainin hankali Hajia ta bisu da shi tace "To kinji abinda ta fad'a da bakinta, dan haka ki barta ta tafi can, idan da rabo ma ta samu miji acan aure zan mata, sai dai kawai kije bikinta idan da hali."

Da k'arfi ya kalleta, *miji*? kuma *aure*? acan d'in? Hummm! Juyawa yayi da sauri ya nufi hanyar barin d'akin, da sauri Amna ba tabi bayanshi dan bata ga abinda zata zauna tayi ba, kai tsaye b'angarensu suka koma.

Kallonta Hajia tayi tace "Ki d'auko kayanki ki zo ku wuce."

Juyawa tayi ta koma sama, ba b'ata lokaci ta d'auko ta sauko k'asa, tana zuwa Gombo ya mik'e yana wa mutanen wajen sallama, tafiya sula fara yi suna barin falon, anan Ummy ta samu damar fad'awa Hamna cewa "Karki damu Hamna, ki tafi dasu yanzu, tunda Hajia ta yanke hukuncin nan babu mai hanawa, amma ina so duk abinda kike ji a jikinki karki bari kowa ya sani, ki kira ki fad'a min zansan abun yi, kafin lokaci mai tsayi kuma nasan ta hak'ura tasa a dawo dake."

Jinjina kai kawai tayi suka fita, a farfajiya daidai k'ofar fita suka samu an saita hancin motocin, anan suka samu Aissata tsaye tana amsa waya da harshen zarma, saida ta gama wayar kafin ta kallesu cike da izza da d'aga kai sama tace "Sai anjima."

Zeituna da Zeinabu ne suka amsa da "Sai anjima, Allah ya kiyaye hanya."

Mai aikin data taho da ita ce ta bud'e mata k'ofa zata shiga, tsayawa tayi ganin Hamna na shirin shiga motar gabansu ansa jakarta a but d'in motar, da mamaki tace "A'a! Me wannan kuma take yi ne haka? Ina zata je ne?"

Mai aikin ce ta girgiza tace alamar bata sani ba ita ma, Gambo ne ya tsaya daga shirin shiga motar yana kallonta yace "Tare zamu tafi da ita."

Yamutsa fuska tayi tace "Ban gane tare zamu tafi ba? Tare muka zo da ita ne?"

"Umarnin Hajia ne, dole haka za ayi madame." Cewar Zeinabu, rai a b'ace ta juya ta kalli Gambo, kallon kiyi hak'uri mana har muje gidan ya mata, saida ta matse baki alamar akwai magana kafin ta shiga motar, tasan kawai dan Hajia ta muzguna mata ne ta had'a su tafiya da Hamna, amma inba haka ba meye na sawa a tafi da ita, yaran da ko da k'uruciya basu tafi ba bare yanzu da girmansu, suna kallo suka ja motoci suka fita daga gidan anata jiniya, basu zame ko ina ba sai filin jirgi, daga nan kuma suka d'aga zuwa Niamey.

D'akinshi ya shiga ya rufe zauna kan gado, tunanin abinda ya faru yake yi, yaji zafi sosai, ba wai marin data masa bane ya b'ata masa rai, marinshi da tayi a gaban wacce zai iya kira da matarshi, ta d'aga hannu ta dalla mishi mari, jin bugun zuciyarshi ya fara canzawa yasa shi mik'ewa da sauri ya fito daga d'akin yana fad'in "Ina! Ba zan tab'a bari damuwarku ta sa min ciwon zuciya ba, idan na mutu ma ba ciwo zakuji ba."

Falon ya dawo ya nufi wajen fridge ya bud'a ya d'auki ruwa, saida yasha sosai sannan ya dawo ya zauna kan kujera, tv ya kunna yana kallo sai kuma ya tuna da Amna, tunda ya nufi d'akinshi ita ma tabi bayanshi, amma kallon daya mata yasa ta shiga d'akin ta ita ma. Mik'ewa yayi ya shig d'akin, kwance take kan gado tayi ruf da ciki, k'arasawa yayi ya zauna kusa da ita yana ci gaba da kallonta, sai dai yafi mayar da hankalinshi kan hannunta na hagu wanda ta mik'ar dashi, ta kifa hannun ta mik'e yatsunta wanda ke rufe da jan lalle, amma yatsanta manuniya sai bubbugashi take akan katifar da sauri sauri kamar tana bubbugashi akan tebur, shafa hannun nata yayi hakan yasa ta tashi zaune tana kallonshi, sunkuyar da kanta tayi sanda taji wasu hawaye sun taho mata, da alamar damuwa ya kalleta yace "Kuka ne kike? To me akayi kuma yanzu? Amna bana son kuka fa ko da na yaro ne."

Abinda ya fad'a ne yasa ta rushewa da kuka ta d'ora kanta akan kafad'arshi, cikin kuka take fad'in "Yah Ammar bana jin dad'i, zuciyata kamar zata fashe, yer uwata yau tayi nesa dani, sannan Ummy ta mare mijina a gabana, banji dad'i ba ko kad'an, kawai dan babu yanda zanyi ne."

Murmushi yayi duk da bata kallon fuskarshi, cikin wata k'asaitacciyar murya yace "Hakan na nufin zaki iya tsayawa sosai akan kare min mutumci na?"

D'agowa tayi ta kalli k'wayar idonshi abinda ta jima ba tayi ba tace "Yah Ammar kai fa mijina ne, zan iya yin komai akan kare mutumcinka."

Wani murmushin ya kuma yi tare da jawota ya rumgume, shafa yake yi a hankali yana fad'in "Dama na fad'a miki Amna, ina so ki zama farin ciki na da kwanciyar hankali na."

Da sauri ta sake d'agowa tace "Zan zama, zan zama yah Ammar, ka kwantar da hankalinka."

Sake dawo da ita yayi jikinshi ya sauke k'akk'arfar ajiyar zuciya har iskan bakinshi ya sauka kanta kafin yace "Allah na gode maka, ka bani uwa ta gari da fari yanzu kuma ka ban mata wacce zata kula dani."

Ummy na shiga d'akinta Zeituna tabi bayanta, tana shiga ta same ta tsaye tana kai da kawowa da alama hankalinta ba kwance ba, k'arasawa tayi da girmamawa tace "Ummyn Ammar dan Allah zamu iya yin magana idan ba damuwa?"

Babu alamar sakin fuska a tare da ita ta tsaya wuri d'aya ta kalleta tace "Ina jinki."

Saida ta numfasa ta d'an kalleta tace "Aunty akan abinda ya faru ne yanzun dama, sai nake ganin kamar kinyi saurin marin yah Ammar, shi fa yanzu ba yaro bane, ya mallaki hankalin kanshi sannan yana da iyali, ko kamar Kamal yanzu a wannan zamanin duka baya gyara shi bare kuma kamar yah Ammar, ina ganin zaifi kyau idan kika jawo shi jikinshi, idan kikayi haka zaku fahimce shi da kyau kusan matsalarshi, dan na fahimci daga ke har Alhaji babu wanda yake nuna damuwarsa akan shi, wallahi wani lokacin sai kuyi kamar ba iyayenshi ba."

Tunda ta fara maganar Ummy ta rumgume hannaye tana mata wani kallo, saida ta dasa aya cikin mamakin k'arfin halinta tace "Zeituna wacece ke? Meye ruwanki da sabgar data shafi ni da d'ana? Me kike ji dashi da har zaki tare ni da maganar nan? In haifi d'an a ciki na ki nemi ki koya min yanda zan tafiyar da al'amarin daya shafi tsakani na da shi? Akan wane dalili?"

Kallonta Zeituna tayi a wannan karan babu wani girmamawa tace "Kawai dai ina so na ankarar dake ne da wuri kafin lokacin nadama ya zo muku, dan n..."

Tsawa Ummy ta mata ta hanyar fad'in "Shiru."

Shirun tayi tana kallon babu alamar jin tsoro ko makamancin haka, d'orawa tayi da "Bari kiji Zeituna, wannan ba abinda ya shafeki bane, ki fita a harkata tsakanina da yaro na, idan kuma ba haka ba zaki ga wata Sa'ada wacce baki tab'a tunanin zaki santa ba."

Girgiza kai tayi tace "Allah ya baki hak'uri, Allah yasa ku gane gaskiya." Tana fad'a ta juya ta bar d'akin, da harara ta bi ta dan dama ranta a b'ace yake, zaune tayi bakin gado ta soma tunanin abunyi na gaba tunda Hajia ta wargaza musu shirinsu.

*Zuwa* magrib duk wani bak'o daya zo bikin nan ya koma garinsu, ana sallah magriba lieutenant ya d'auki Zeituna suka tafi ganin kawu Mamu, a k'ofar gidan ya tsaya ita ta shiga ciki da sallama, babu wanda ya amsa sallamarta sai Jumma dake cikin garken awaki da tace "Wake sallama?"

Saida ta zagaya inda taji muryarta tace "Inna Jumare nice."

Duk da ta d'auki muryarta saida tace "Ke ce wa?"

"Zeituna." Ta bata amsa, da sauri ta saki k'afar akuyar da zata d'aure ta taho da sauri tana gyara d'aurin k'irjinta tana fad'in "Yawwa sannu da zuwa, naji dad'in zuwanki, kamar kinsan ina nemanki dama."

Tsaye tayi tana kallonta inda ita kuma ta fara masifa cikin fulatanci tana fad'in "Zeituna wane rashin mutumci ne wannan? Daga an aiki yarinya gidanki sai yaron gida ya mareta, me ta mishi to? Kuma ke a gabanki amma babu abinda kikayi, dama had'a baki kukayi dan a ci mutumcinta ko, ke tunda muke dake a gidan nan kin tab'a ganin ni ko ubanta wani ya d'aga hannu ya daketa? Sai wani d'an k'ato kawai kamar ya samu jaka ya marar min yarinya."

Masifar da take yi ce tasa kawu Mamu fitowa daga d'aki, yana ganin Zeituna shima ya d'ora tashi masifar har da cewa "To ki fad'a min d'an uban waye shi a gidan? Wallahi sai naje har gidan da kaina na rama mata marinta, ke a gaban uwarshi da ubanshi ma zan rama mata dan ya gane tana da gata, dan ba zai kumbura min fuskar yarinya kuma ya tafi a banza ba."

Ita dai kallonsu kawai take, saida kawu ya gama sannan tace "Kawu ya jikin naka? Da sauk'i?"

Cike da tijara yace "Wane jiki kuma? Ni dama lafiyata lau, kawai nace ta fad'a miki hakane dan na samu kud'i a hannunki, dan naga baki damu da mu ba tunda kikayi auren nan, yanzu gashi wannan shegen Janu (Jano) yake ko uban wa ya saka ni gaba akan kud'in shi har yana ikrarin cewa zai rufe ni, to ba dole na samu kud'i ko ta halin yaya ba na biyashi kafin ya rufe ni."

Cikin rashin jin dad'i tace "Kawu har nawa yake biyanka ne?"

"To ni na sani ne? Kawai ba dai ya bani kud'in na karb'a ba a lokacin ina jin dad'in ganinsu, amma dai nasan zasu kai jaka d'ari biyu."

D'an zaro ido tayi tace "Kawu d'ari biyu?" Jumma ce tace "Eh, sunyi yawa ne? Ke yanzu a matsayin da kike ai wannan kud'in ba komai bane a wurink."

Kallonta tayi cike da damuwa tace "Inna Jumare wallahi bana da wannan kud'in, ina zan samu d'ari biyu ni kuma?"

Kallon sama da k'asa ta mata tace "Kiji tsoron Allah Zeituna, dubi kayan jikinki fa, dubi sark'a da d'an kunnen dake jikinki, dubi jakarki ma abar kallo ce, kuma kice baki da wannan kud'in?"

"Amma Inna..." Kawu Mamu ne ya katse da fad'in "Ni ban damu da wannan ba, ba lallai sai ke zaki bayar ba ai, ba ga mijinki ba? Ki fad'a masa halin da nake ciki mana, shi da girmanshi da komai zai bari ne a d'aure sirikinshi a garin nan, kawai ki fad'a masa ke dai zaisan abunyi."

Iska ta furzar cike da damuwa da halinsu tana tunanin yanda zata fara tambayarsa kud'i masu yawa haka, sai yanzu ta fara nadamar k'in amsar kyautar da yake yawan yi mata lokuta da dama, yakan bata kud'i yace ko zatayi wani abun ba sai ta tambaye shi ba, tunda yer uwarta na zuwa aiki ita kuma bata damu ba, amma sai tace bata so bata buk'atar komai, idan ya matsata sai tace ya rik'e idan ta tashi zata tambaye shi. Yanzu gashi bukatar kud'in ta taso mata sai dai masu yawan da ba zata iya tambayarshi ba, ajiyar zuciya tasauke kallesu tace "Shikenan kawu, zan san abunyi dai."

"Da dai yafi." Cewar kawu Mamu, Jumma ce tace "Zeituna wai uban waye ya marar min yarinya?"

D'an murmushi Zeituna tayi tace "Inna Jumare d'an shi ne fa."

"D'an shi? Kuma shine baki rama mata ba saboda kina so ki nuna mishi ba kya k'aunarta."

Wani kallo Zeituna ta mata, na rama mata? Yah Ammar d'in zan mara? Lallai baki san waye shi ba, to ai ko ni har yanzu ban wuce ya galla min mari
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment