Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

hakan yasa ya ga fuskar Ammar d'in, amma a tunaninshi Amar ne dan shi kad'ai ya sani, ajiyar zuciya ya sauke ya saki jikinshi yace "Sannu ko, Alhaji kana lafiya? Kaine a gidan yau? Ai kuwa yanzu mahaifin naku ma suka bar nan."

Baice mishi komai ba sai kallonshi da yake dan haka yace " Ai ban samu damar zuwa d'aurin aurenku saboda bana jin dad'i lokacin, ya hidima kuma?"

Wani kallo ya masa yace "Ka sanni ne?"

Kallonshi yayi da mamaki, d'an murmusawa yayi yace "Alhaji ai..." Ji yayi kalmomin sun tsaya kuma ya tabbatar bashi ya tsayar dasu ba, hannun da Ammar ya d'ora akan bindigar dake k'ugunsui ce ya tsorata shi, cikin firgita yayi niyyar komawa cikin gidan yana fad'in "To sai anjima."

Zai koma ciki Ammar yace "Dakata, ba kaine mahaifin yarinyar nan ba? umm wa take ma? Juuuuu...k'arasa min mana."

"Jumare, Jumare, Jumare take, amma ni ban santa ba." Duk yayi maganar ne cikin razani, sake had'e fuska yayi yace "Mu shiga daga ciki mana baba, magana na zo muyi."

Ai da sauri ya shiga cikin gidan yace "Taho taho."

Saida ya k'ara bud'a k'irji cikin tafiya irinta sojawa masu ji da k'arfi ya bi bayanshi, kawu da jiki ke ta rawa ya tattara yara ya turasu d'aki, Jumma ya ma tsawa yace "Ke baki da wayon kawo tabarma idan kinga mutane?"

Tana d'ago kai ta kalli wanda ke bayanshi ta hasken fitilar dake wajen gida da sauri ta tashi ita ma, d'aki ta shiga d'aukar tabarmar amma gabanta da zuciyarta bugawa suke, haka ta d'auko ta shinfid'a musu ta koma d'aki, ba tare daya cire takalmin ba ya zauna a tank'washe k'afafu amma wajen takalmin a k'asa, saida ya d'aga kai ya kalli kowace kusurwa kafin ya kalli kawu dake gefenshi tsaye ya had'e hannaye yana kallon ikon Allah, a kaikaice yace "Fulani ne ku ko?"

"Eh Alhaji."

Kallonshi yayi ya saki fuska yace "Za'a samu nono?"

Kallonshi kawu Mamu yayi, nono kuma? Lallai yau farar rana ce a wurinshi, basu cika aiki da fura da nono ba sosai, amma yau saiya aiki Jumare ta siyo mishi fura da kuma nono mai yawa har da sukari (sugar), da sauri yace "Eh akwai, Alhaji ai ba'a rasa nono a wurin bafulatani."

Murmushi ya mishi yace "To a kawo min, sannan a sa sukari."

Da sauri ya shiga bukkar Jumma ya sameta, a k'warya yace ta zuba dan watak'ila bafulatani ne shima, dan duk da tsoro bai bari ya mishi kallon tsaf ba yaga sufarshi, yana zuwa ya kawo mishi ya juya zai koma ciki yace "...


*Alhamdulillah*
14/10/2020 ร  00:58 - Ummulkhairi: ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ
*BADAK'ALA*
๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ

*Labarin Gaske*

*NA*

_SAMIRA HAROUNA_

*Litattafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._

*SADAUKARWA GA*

๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ _*AHALI NA*_๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

๐Ÿ‡ณ๐Ÿ‡ช *TAURARIN NIGER*
```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)```

โœช{T . N}โœช๐Ÿ“–๐Ÿ–Š๏ธ

https://www.facebook.com/101305508365889/posts/101311008365339/?substory_index=0&app=fbl


_Bismillahir rahamanir rahim_

_41_


"Zauna mana Abba, ai wurinka na zo."

Dawowa yayi ya zauna jiki na ci gaba da mishi rawa ya d'an zauna kan turmin dake kwance yana kallon Ammar, saida ya kifa k'waryar nonon nan bakinshi yasha kafin ya sauke ya kalli kawu yace "Abba, Abba na ya fad'a min 'yarka ce na mara d'azu da safe, kuma ya fad'a min ranka ya b'ace sosai har kana cewa ma zaka je ka rama mata, shine na hutar da kai ta hanyar kawo kaina."

Zaro mishi ido yayi yace "Ni? Yaushe akayi haka! Allah yaro inaga dai bai fahimce ni bane, ni kam ina ni ina tab'a jikinka yallab'ai."

Wani kakkausan kallo ya masa yace "Kana nufin Abba na k'arya ya min kenan?"

Da sauri yace "A'a Qur'ani, gaskiya ya fad'a, amma bani na fad'a ba Jumma ce, uwar yarinyar."

๐Ÿ˜‚Jumma na d'aki tana jinsu gatsal tayi daga d'aki ta fito tana fad'in "A'a Baffan Jumare, kaji tsoron Allah fa."

Kallonta Ammar yayi, wani irin juya mata kai yayi alamar ta koma ciki kamar maciji, juyawa tayi ta koma tana kallon kawu Mamu, shi kuma binta yayi da fulatanci kafin ya kalki Ammar wanda shima ke kallonshi, saida ya sake kallon bukkokin sannan yace "Ina yarinyar take ne?"

"Tana ciki, ai bata jin magana ne." Murmushi ya masa yace "Ko zan iya ganinta?"

Da sauri ya mik'e yana fad'in "Ba damuwa, yanzu kuwa."

D'akinsu ya shiga ya sameta kwance, murya k'asa k'asa cikin harshensu yace "Kin jawo mana bala'i, to tasoyana nemanki kema, kuma karki kuskura naga kina juya bakin nan ko a b'oye ne, ki barmu mu rabu dashi lafiya dan naga ba mai hankali bane."

Fitowa sukayi tare inda ya zauna inda yake ita kuma ta durk'usa k'asa tana kallonshi, wannan mutumin ne, hakan yasa ta k'ara shan jinin jikinta, kallonta yayi yana kurb'an nonon shi yana mata murmushi yace "Jumare ya kike?"

A tak'aice ta kalleshi ta kuma yin k'asa da kanta, murmushin gefen labb'a ya mata yace "Jumy."

Da sauri ta kalleshi, Jumy kuma? Murmushi tayi saboda sunan ya mata dad'i ita kam, ganin kallon da take masa da murmushi yasa shi cewa "Sunan ya miki dad'i?"

Murmushi ta sake yi ta rufe bakinta hakan yasa yace " Kina sona Jumare?"

Rufe fuska tayi da hannayenta ta mik'e tsaye ta daka da gudu d'aki, binta yayi da kallo yana murmushin mugunta, dawo da kallonshi yayi kan kawu da shima ke murmushi cike da kunyar yaron, wani murmushin ya sake mishi yace "Idan ta amince ai kaga ni da Abbana duk mun zama surukanka."

D'an kawar da kai kawu yayi irin fa shi har ya fara jin kunyarshi ma a matsayin suruki, yana ganin haka ya tab'e baki ya sake kurb'an nononshi, aje k'waryar yayi ya tashi tsaye yace "Abba ni zan tunda kun yafe min."

_Yaushe suka ce sun yafe?_

Gyara zaman bindigar nan yayi tare da nufa hanyar fita, bin bayanshi kawu yayi suna kaiwa k'ofar gidan yayi daidai da zuwan Jano, Ammar ya sanshi farin sani, yasan ba mutumin kirki bane, mamakin abinda ya kawo shi gidan yake yi, dan haka ko sallama bai yi wa kawu ba yace "Kai kuma fa?"

Kamar yanda ya sanshi haka shi ma ya sanshi dan dukansu matasa ne masu ji da kud'i, babu alamar sakin fuska ya bashi hannu alamar suyi musabaha yana fad'in "K'alau."

Bai bashi hannun ba sai kallon kawu da yayi yace "Ka san shi ne?"

Jano d'auke idonshi yayi daga kansu yana kallon titi yana murmushi, yasan bala'i ne yake nema dashi kawai, shi kuma bai shirya wujijjiga kanshi ba bare ya biye mishi, kawu kuma da baya so Ammar yasan abinda ke faruwa da k'arfi ya kama hannun Jano suka koma gefe yana waiwayen Ammar dake binsu da tuhumammen kallo, yana kallo kawu ya fito da kudin da lieutenant ya bashi ya damk'awa Jano yana fad'in "Gashi malam, na biyaka dan Allah ka shafa min lafiya yanzu, karka sake zuwa gidan nan."

Wani kallo ya mishi yana yatsina fuska yace "Ko saboda waccen ne ka hana min 'yar taka? To ka sani waccen babu abinda zaiyi da ita wallahi, kawai zai yaudareta ne sannan ya mayar maka da ita sunan da zaka gagara kiranta dashi."

Wani kallon kai kauce kawu ya mishi yace "Kai dallah, ana babbakar giwa wa yake jiyo k'aurin zomo, ai 'yata tafi k'arfin dukanku wallahi, sai dai uban waccen d'in."

Wata dariya Jano yasa yana fad'in "Babban arne kenan."

Ammar dake cike da shakku matsowa yayi wurinsu ya kalli kawu rai a b'ace yace "Me yake faruwa ne tsakaninka da shi? Kasan waye wannan kuwa? Ba mutumin kirki bane."

Wani kallo Jano ya mishi yace "Ammar, ka sanni na sanka, karka shiga sabgata mana tunda bansa da kai ba, kayi abinda ya kawoka nayi abinda ya kawo ni."

Daf dashi ya matsa yana fad'in "Ba zanyi sabgar tawa ba Jano kayi abinda za kayi, kai ka sanni wallahi ba zan lamunci iskancin nan daga gareka ba."

K'asa da sama ya kalleshi yace "Bana jin rigima, kai kuma kullum a cikinta kake kamar wanda aka haifa ana dabbatuwa, dan haka banda lok..."

Bai yarda ya k'arasa fad'a ba ya kai mishi bugu a baki, baya baya yayi ya kaiwa motarshi karo ya dafeta yana kuma dafe da bakinshi, idonshi jawur sukayi har da k'wallar wahala, da sauri kawu ya shiga tsakani yana bawa Ammar baki ya rabu dashi, cikin jin bala'i da masifa yake nuna kanshi yana fad'in "Ni d'in? Ni ne aka haifa kamar ana dambe? To bani ne ba sai dai in kaine ubanka ya haifa yana dambe."

Tasowa Jano yayi yana tofar da yawun bakinshi da yake jin sunyi gishiri alamar jini yace "Ni ka wa haka Ammar? Ni? Tak'amarka akwai iko da masu saka kakia gidanku? To wallahi sai kayi nadamar dukan nan daka min, in kuma bansa kayi dana sanin haihuwarka ba to kace ba d'an halak bane ni."

Cikin d'aga sauti ya fara fad'in "Yeeee, kai ba d'an halak bane, da gani ma ai ana ganewa, banza mata-maza kawai, ashe k'aramin d'an jagaliya ne kai, to kaji da kyau Jano, ba boka babu malam babu d'an bori, kuma a haka zan ci uwarka, ruwan randa kawai zansha na ma iskancin da baka tsammani, idan har kuka gagara kai da matsafan naka to ka nemi lambata a wurin wanda ya sani, ka zab'i rana da lokacin da zamu had'u da kai a bayan gari saika sa min hannu, watak'ila ka iya huce haushinka ta hanyar rama dukanka."

Juyawa yayi ya kama murfin motarshi ya bud'a zai shiga, tsaya yayi ya kalleshi da kyau ya d'aga mishi yatsarshi ta tsakiya wacce tafi tsawo tana kallon sama, sannan yayi alama da yatsunshi cewa sai sun had'u shiga yayi ya tayar ya wuce. Suna had'a ido kawu ya sunkuyar da kanshi yana murmushin mugunta, a ranshi yana fad'in "Ashe kowa da wanda ya raina."

Tsaki yayi ya juya a fusace shima ya bar wurin, Ammar ma daga nan asibiti ya sake komawa, wannan kayan ya cire dan baya so kowa na gida yasan shi dasu ya mayar da nashi kafin ya sake komawa gida.

Jano na barin nan ya so ya zarce ofishin yan sanda, ba wai dan ya dake shi sai dan ganinshi da kakin soja da yasan ba soja bane kuma yake sawa, yasan inhar doka ce ya taka ta hanyar sa kayan dole hukunci zai hau kanshi, amma saiya bari har safiya tayi sai yayi k'ararshi. Ammar kuma na ko da yaje gida kai tsaye wajen amaryarshi ya nufa, tana zaune kan kujera tana kallo ya same ta, tsaye yayi ya bud'e mata hannayenshi alamar ta rumgume shi, bata fahimce shi ba sai cewa da tayi "Sannu da zuwa yah Ammar."

Mik'ewa tayi ta nufe shi tana k'ara fad'ad'a murmushinta, tana zuwa ta tsaya bata matsa kusa dashi ba, saida ya mata kallon zan ci... kafin ya fizgota da k'arfi ta fad'a jikinshi, saida zaman d'an kwalinta ya canza inda tayi fiki'fiki da idonta, matseta yayi sosai yana sauke numfashi, d'agata yayi daga jikinshi ya kalleta yace "Daga yau kika ga na shigo haka zaki min, kuma ko gaban waye ban yarda ki nuna jin kunya ba, haka nake so kuma dole kiyi."

Yana fad'a ya wuce ya barta tsaye, juyawa tayi da baki bud'e ta bishi da kallo, d'aga ido tayi sama tace "Allah gani gare ka, ka shirya min bawan nan naka."

Zaune ta koma tayi tana ci gaba da kallo, amma duk in taji motsi daga d'akinshi sai gabanta ya fad'i, ana haka dai har ya fito sanye da farin wando iya gwiwa mai aljihu da farar singlet d'in data kama shi sosai, yana zuwa ya zauna kamar zai fad'a mata yana fad'in "Kiyi hak'uri ba zan iya yi miki kwalliya ba, yunwa nake ji kuma na gaji, amma ki sani ni makwoyin sunnar annabi ne."

Dariya tayi ta mik'e tsaye ta nufi teburin abinci, da kallo ya bi manyan kayan dake birge shi tare da ayyana luguden da zasu sha yau a hannunshi, cije leb'en k'asa yayi yana lumshe ido, yana kallo ta d'auko kwanukan abinci ta juyo tana takowa, nan ma ido ya k'ura mata yana kallon komai na hallitarta, bai sani ba ko dan komai nasu iri d'aya ne da kankana, ko kuma dan suna da k'ira da hallita irin yanda yake son mace, dan shi dai yafi son mace mai cika hannu yar dumul dumul, ko gajera ce yana sonta a haka bare kuma su dake da tsayi, sannan ga kyawun fuska masha Allah, haka kuma Amna tafi kyau akan kankanarshi, kawai dai haske kankana tafi waccen, shi dai kawai yasan komai nasu yana birgeshi, tana zuwa ta sunkuya ta aje kayan ta durk'usa ta fara zuba mishi, kallon fuskarta yake yace "Amna yanzu ma abincin kika dafa?"

Ba tare data d'ago ba tace "Yah Ammar idan ban dafa ba to me zaka ci?"

Yatsina fuska yayi yace "Da gaskiyarki kuma, dan kinga banyi tunanin siyo abinci ba."

D'an murmushi kawai tayi tare da kallonshi tace "Na aje maka anan ne?"

Kai kawai ya d'aga mata, gyara wurin tayi sannan ta aje mishi ta zaune yanda suke fuskantar juna, kallonshi ta sake yi tace "Bismillah."

Saukewa yayi ya tank'washe k'afafu yana fad'in "Amma ko baki dafa ba ai ga Hajiarmu, sai muje mu ci na su."

Shiru tayi ita dai ko kallonshi ba tayi ba, loma ya fara kaiwa tare da bismillah, saida ya tauna ya had'iye ya kalleta kamar mai karanta wani abu a fuskarta kafin yace "Kinyi kyau sosai."

Sunkuyar da kai ta sake yi tace "Nagode."

Da mamaki ya kalleta yace "Ke ba zaki ci ba?"

Kallonshi tayi tace "Ka fara ci ka k'oshi."

Tab'e baki yayi ya jawota ya zaunar da ita kan d'aya cinyarshi, k'ara sunkuyar da kai tayi tana sissinewa kamar ta shige k'asa, d'ebo abincin yayi ya kai mata a baki tana fad'in "Gani ni k'aton banza kenan, na zauna ina cin abinci ke kina kallo na."

Tun tana gocewa har ta fara karb'a ita ma, bai barta ba saida ta shagwab'e fuska tace "Wallahi yah Ammar na k'oshi, cikina kamar zai fashe."

Kallon rainin hankali ya mata yace "Wannan d'an abincin da kika ci ne zai fasa miki ciki? To gidan ubanwa kika kwaso wannan k'ibar?"

Tab'e fuska tayi kamar za tayi kuka a zuciyarta tace "Ai ba kowace k'iba ta cin abinci ba, kuma ubana ba siriri bane bare kace banda inda na gadota."

Saida ya shafa cikinta kad'ai ya daina bata ya ci gabada ci har ya k'oshi sannan yayi hamdala, tashi tayi ta d'auke kwanukan ta dawo ta zauna k'asa dan har yanzu shima bai tashi ba, d'aga k'afafunta tayi ta d'ora hannayenta saman gwiwan, bata ankara ba taji ya finciko k'afafunta ya mik'ar dasu, tana kallo ya d'ora kanshi ya juyo da kanshi yana kallon fuskarta, zagaya hannunshi yayi ta bayanta ya d'an zage zip d'in rigarta, d'aya hannun kuma ya zura shi ta cikin rigarta yana wasa da cibiyarta, sam bata yarda sun had'a ido ba sai kawar da kai take yi, abun kamar wasa saiya d'aga rigarta ya zura harshenshi a cibiyarta yana ta karkad'a shi idonshi rufe kamar mai bacci, ita kanta baccin taji yana son figarta ga tsikar jikinta da take mugun tashi, jikinta duk yayi sanyi k'alau d'an d'aya hannun ma bayanta ya zura shi har ya b'alle mata bras data saka wanda dama take jin ta dameta saboda rashin sabo, a hankali ya fara zarmewa ta hanyar zamar da rigarta ya cire mata hannayen, ita kanta bras cireta yayi ya cilla gefe, da sauri ta jawo rigarta zata mayar ya bud'a idonshi da suka bata tsoro saboda canzawar da sukayi, tashi yayi tsaye tare da kama hannunta ya nufi d'akinshi da ita, tunda ta ga inda suka nufa take addu'a a zuciyarta wanda bata ma san me take karantawa ba, tsabar yanda zuciyarta ke bugawa da kakkarwa da jikinta ya fara yi yasa hawaye fara zubo mata, yau kam babu tsumi babu dubara ta shiga hannu kenan.

*Wani* k'akk'arfan nishi ta sauke mai tafiya da numfashi, hannayenta gaba d'aya ta luma kan damatsanshi wanda yasa faratunta shigewa sosai a damtsen shi, idonta rufe suke ruf sai kai da take girgizawa hawaye na fitowa a idonta suna bi ta bayan kunne, Inna lillahiwa'inna ilaihi raju'un da kalmar shahada ne a bakinta, zafi ne mai tafiya da k'walwa, lokaci d'aya taji shigar abinda ba tayi tsammani ba, abu ne da bata isa ta kwatanta girmansa ba, ita dai tasan a lokacin daya shiga ne ruhinta ya bar gangar jikinta, mamakinta d'aya shine yanda akayi take motsi bayan kuma tasan gawa bata motsawa. Babu alamar raguwa sai k'aruwa da rad'ad'in keyi, dan haka ta sake lik'e idonta sosai ta cije leb'enta na k'asa tana jan hannunta kan damtsenshi, hakanne yayi sanadiyar fitar da jini daga damtsenshi saboda kaifin akaifunta masu d'an tsayi saboda gyaran da aka musu saboda bikin, tumurmusa kanta kawai takeyi tsakiyar tattausan pillown, inda take ta yin sama tana son zamewa amma sai k'ara lik'e mata yake.

Duk abinda ke faruwa bai sani ba, abinda ke zautar da tunaninshi kawai yake son yaji ya samu sauk'inshi, amma abun ya ci tura sai k'ara lik'ewa yar mutane yake, ba ita ba da a jikinta suke shi kanshi da yake tsutsarsu har bakinshi yayi zafi, ya gyara kwanciyar yafi kala hud'u duk dan yana so ya hutar da ita, amma ya jarabar ta k'i kwantawa, a daidai lokacin da yaji zafin yaginshi da tayi a lokacin yayi wata zabura ya sake k'amk'ameta yana wani jijjiga yana k'ara shiga jikinta, daga haka kuma sai yayi sanyi zufa ta keto mishi lokaci d'aya, gefenta ya fad'a yayi ruf da ciki yana sauke numfashin samun nutsuwa, ya jila haka kafin ya iya d'aga kanshi ya kalleta, ganin kanta na kallon gefe d'aya yasa hannu ya juyo da ita, murmushi ya saki ganin har yanzu idonta rufe suke, yunk'urawa yayi ya sauka daga kan gadon ya d'auki gajeran wandonshi ya mayar ya shiga ban d'aki.

Zaune ta mik'e tana cije leb'e, saida taji ta wartsake kafin ta tashi ta d'auki kayanta tayi saurin barin d'akin kafin ya fito, tana zuwa d'akinta ban d'aki ta shiga ta saka rigar wanka sannan ta fito, madafa ta shiga ta dafa ruwan zafi masu yawa kafin ta juye a bokiti ta shiga dasu d'aki, tana shirin shiga ban d'aki taji ya shigo d'akin, garin saurin shigewa ban d'akin yasa bokitin ya bugi k'ofar ban d'akin ruwan suka zuba a k'afarta, sakin bokitin tayi tare da sakin k'ara lokaci d'ayakuma take furta Inna lillahi wa'innailaihi raju'un, da gudu ya k'araso ya fitoda ita yana kallon fuskarta cikin fad'a yace "Meye haka? Kina haukane? Wa yace ki fito daga can?"

Hijabinta tasa tana goge hawaye, tausayinta ne yasa shi rumgumeta yana shafata yace "Yi hak'uri to, amma me yasa kika taso? Ba zaki iya kula da kanki ba, ko baki yarda dani bane?"

Girgiza kai tayi dan haka ya kama hannunta suka shiga ban d'akin, da kanshi ya had'a mata ruwan ya kalleta yace "Zaki iya ko na taimaka miki?"

Girgiza kai tayi alamar a'a, barinta yayi ta gyara kanta tsawon lokaci kafin ta kammala ta fito, kwantar da ita yayi yaja mata bargo, kallon fuskarta yayi yana murmushi mai tsadar gaske yace "...


*Comment*

*Alhamdulillah*
14/10/2020 ร  00:58 - Ummulkhairi: ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ
*BADAK'ALA*
๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ

*Labarin Gaske*

*NA*

_SAMIRA HAROUNA_

*Litattafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._

*SADAUKARWA GA*

๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ _*AHALI NA*_๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

๐Ÿ‡ณ๐Ÿ‡ช *TAURARIN NIGER*
```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)```

โœช{T . N}โœช๐Ÿ“–๐Ÿ–Š๏ธ

https://www.facebook.com/101305508365889/posts/101311008365339/?substory_index=0&app=fbl


_Bismillahir rahamanir rahim_

_42_


"Nagode, aljannata."

Murmushi ta masa mai tafiya da imanin mutum kafin ta fara lumshe ido, sumbatar goshinta yayi tare da gyara mata bargon sannan ya kwanta gefenta, bata jima ba bacci yayi awon gaba da ita, amma shi bai samu damar yin baccin ba sai durmiya da yayi tunanin rayuwa a sanda yake wanke zanin gadon da yaji matsa shi kanshi, yana wankin yana tunanin waccen ranar ma da halak d'inshi ce da shi zai wanke zanin nan, amma baisan waya wanke ba tsabar masifa. Yasan da babbar matsala a gaba idan asirin abinda ya aikata ya fito, amma a shirye yake da duk wanda zai tuhume shi, yana da hujjjojin kare kanshi ko da ba'a gamsu ba. Ko ya take? Ita ce tambayar daya ma kanshi, nan ma zurfafa tunani yayi sai yaga watak'ila tafiyartata zama alkairi a gare shi, tunda ya auri k'anwarta, hakan zaisa ya mayar da hankalinshi kan matarshi. Amma me yasa Ummy ta shiga firgici sosai daga yana son duba kankana? Me yasa daya anbaci ciki duk suka rud'e kamar dai cikin ne da ita? Akwai wani abu! Shine abinda zuciyarshi ta fad'a masa, da wannan tunanin bacci b'arawo yayi gaba dashi.

Tun *08:00* na safe colonel ya gama haramar tafiya shi da yaranshi masu tsaron lafiyarsa, yayi sallama da kowa sannan ya fito, a lokacin Ammar ya zo sukayi sallama, colonel zai shiga mota mai gadi ya taho da sauri ya gaishe shi, amsawa yayi kafin ya mik'e daga rusunawar da yayi ya bawa Ammar wata takarda yana fad'in "Wannan wani ne ya bayar yace a baka."

Karb'a yayi ya bud'e ya fara karantawa ba tare da yace mishi komai ba, wani shegen murmushi ya saki kamar an bashi katin shiga aljanna, ganin haka yasa colonel tsayawa yace "Yaro na ya dai? Lafiya ko?"

Ba tare daya daina wannan murmushin ba ya kalleshi yace "Lafiya lau tonton, wani k'aramin d'an daba ne zai min iskanci, amma zan nuna mishi na fishi iya buru'uba."

Yana fad'a ya tunkari hanyar komawa b'angaren shi yana fad'in "Za muyi waya tonton."

Cike da bala'i colonel yace "Da kyau yaro, karka ragamar duk uban da yace zai taka ka, a shirye muke muyi shari'a da uban ko waye, kaje Allah ya tsare."

*Da sannu halin kowa zai fito*

Yana shiga d'akinshi ya wuce ya d'auko makulin mota da wayarshi ya fito, ba dan ta fito daga d'akin ba a lokacin da ba zata san fitarshi ba, amma yana ganinta saiya jawota jikinshi yana kallon fuskarta yace "Matarmu zan fita, ki kula da kanki sannan ki ci abinci idan kin dafa, karki saka dani kuma karki jirani, ba zan dawo da wuri ba."

Tsoro ne ya fara bayyana a fuskarta tace "Lafiya yah Ammar? Ina zaka je?"

Shafa kumatunta yayi yace "Ba komai, zan dawo amma ba da wuri ba."

Yana fad'a ya saketa ya tunkari k'ofa kamar zai tashi sama, da kallo ta bishi sai gabanta da taji yana d'an fad'uwa, ba komai ta gani a idonshi ba sai bala'i, tana jin tsoron amsa gayyatar katin masifa ne yayi daga gurin wani, ita kam ina zata saka kanta da tashin hankalin bawan Allahn nan? K'arasawa tayi ta zauna kan kujera ta zuba tagumin zaman jiran tsammani. Jikinshi har rawa yake ya matsu ko ya isa ofishin, tunda ya cije leb'e ya kasa sakinshi sai k'yaci da yake yafi dubu, to wai shi Jano zaiyi k'ara? To ai ya ma raina masa hankali da baiyi k'ararshi wajen sojawa ba ko jendarme, sai wajen masu saka kakin police, jar uba! Da wannan bala'in ya isa wurin har gaban inspecteur d'in daya shirya sulhunta tsakaninsu da kanshi, dan baya so rikicin yayi girman da sunan gidan Gaga zai b'ace.

Daga zaman rashin mutumcin da yayi kamar zaiyi kwance a kujerar tare da d'ora k'afar dama a ta hagu yana kallon kowa da wutsiyar ido zaka san babu arzik'i, kuma k'irirs yake jira ya ta fara zazzage kwandon bala'in daya d'ebo, inspecteur d'in ne ya kalle shi yace "Malam Ammar, wannan ya shigar da k'ararka akan dukan daka mishi, sannan akwai tuhuma da ake maka ta cewa kana anfani da kakin soja alhalin kai ba soja bane,
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment