Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

kai k'arshen abinda take son fad'a, d'ago kai yayi ya kalleta ido cikin ido, idonshi sun canza kala sunyi ja, maganarta ta sokeshi fiye da tunanin mai tunani, ta kassara zuciyarshi da kalamanta, ta sa shi jin kunyar soyayyar da yake mata, zai kuma nuna mata a aikace ba yanda take tunani yake ba.

A sukwane ya mik'e yayi kanta, saida ya tsaya gabanta ya d'aga hannunshi mai d'auke da zarta zartan yatsu ya sauke mata kyakyawan mari a fuskarta, kafin ta d'ago daga sunkuyawar da tayi tare da k'ara ya sake sauke mata wasu yatsun, ta dafe kunci zata d'ago a karo na uku ya sake gabza mata wani marin, rud'ewa tayi ta ja baki tayi shiru daga ihun da take tana murza kumatu da taji suna mata wani zuuuu zuuuu zuuuu kamar zasu tsinke, daga wayarta jaka da makullin mota duk ta jefar dasu, sam babu abinda take ji sai ko take gani, tana cikin wannan halin ya sunkuya ya nunatada hannu yace "...


*Alhamdulillah*
14/10/2020 Γ  00:58 - Ummulkhairi: πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨
*BADAK'ALA*
πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨

*Labarin Gaske*

*NA*

_SAMIRA HAROUNA_

*Litattafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._

*SADAUKARWA GA*

πŸ‘¨β€πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘¦ _*AHALI NA*_πŸ‘¨β€πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘¦

πŸ’«βœ¨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🀝

β˜† *[ T.M.N.A]* β˜† πŸ“–πŸ–ŠοΈ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_

_59_

Cikin matsanancin b'acin rai yace "Hamna ni? Ni zaki kalla ki fad'a ma wannan maganar? Yaushe aka haifeki? Yaushe har na miki caccakar da kike ganin ta isa ta zama katangar da zaki b'uya a bayanta ki raina ni? Ko yar uwarki da nake kwana tare da ita na tashi tare da ita babu kaya a jikina bata isa ta min rainin da kike son min ba, har ki kalle ni wai kice na fad'a miki ina zamu had'u, ke yanzu nan har kin shirya zaki iya dani? To saurara kiji Hamna ba tsananin so ko kishinki bane yasa nake takuraki kan dinga suturta jikinki, mutumci ne nake so na kankaro miki a idon jama'a, duk idon mutane yana kanki saboda daga babban gida kika fito kuma yar babban mutum ce, amma daga son taimaka miki sai abu ya zama tashin hankali."

Kujerar daya tashi daga kai yasa k'afa ya tokara cikin b'acin rai kujerar tayi baya da k'arfi ta daki kwabar gilas d'in turare, hakan yasa wasu daga cikin kwalaben girgizawa suka fad'o k'asa hakan ya haddasa sauti marar dad'i mai kayar da gaba, bai kula ba yasa hannu yana dukan k'irjinshi yana fad'in "Allah ma shida ne, sannan kuma ku zama shaida."

Ya fad'a yana nuna duk mutanen dake d'akin yace "Inhar na k'ara magana kan Hamna ta suturta jikinta ku ce ta hanyar zina aka haife, na kuma yarda ba zanyi gadon mahaifina ba, ba wai iya dukiyarshi ko d'aukakar shi kawai ba, har da sunan shi, na yarda ba zan sake saka sunanshi a gaban suna na ba."

Kallonta yayi yace "Kiyi duk abinda kike so da rayuwarki, banda matsala a kai Hamna."

Da saurin bala'i ya fita daga falon zuwa barin gidan gaba d'aya, yana tuk'i yana dukan sitiyari da k'arfi. Falo yayi shiru ko numfashin mutane baka ji, wasu tunda suka rintse ido sakamakon fad'owar kwalaban turare basu bud'e ba har yanzu, Ummy da hankalinta ya gama tashi tasan yau asirinsu zai tonu, dan dukansu sunyi magana ne a yaran da duk mai hankali zai fahimta, kallon Hajia take da taga kanta k'asa tayi shiru, a hankali ta juya kanta ta kalli Hajjo, sai taji tsohuwar ta bata haushi dan duk ita ta b'abb'ako musu aikin nan, data barta ta tafiyarta da yanzu an rabu lafiya.

Kakkauran numfashi Hajjo ta sauke cikin muryar alhini tace "Hajia, dama haka yaron nan yake?"

Hajia ma da tasan komai kuma bata so abun ya fito kallonta tayi cikin jin haushi tace "Duk ke kika ja mana wanan sababin fa, da bakiyi maganar gaisuwar nan ba duk da haka bata faru ba."

Kallon Hamna tayi da sai yanzu kad'ai take jin magana a hankali a hankali tace "Ki tashi daga nan ki bani wuri, kije kiyi ta fita duk yanda kike so babu mai hana ki, idan kina so ma ki tafi tsirara, amma karki kuskura ki zubar mana da mutumcin gida kinji na fad'a miki."

Tana fad'a ta mik'e tayi d'akinta, Ummy na ganin haka wata ajiyar zuciya ta sauke tana godiya ga Allah, ita ma sulalewa tayi ta bar wurin ko Hamna bata kula ba dan maganar gaskiya tasan Hamna ce ta jawo magana, shi kuma dama ba hak'uri gare shi ko na k'wayar zarra. Hamna ma mik'ewa tayi cikin hassala ta d'auki jaka wayarta da makulli ta fita, ko da ta shiga mota saida ta gyara fuskarta da duk sawun hannayensa suka fito, wannan haushin na cin zarafin daya mata da kuma abinda Hajia ta fad'a mata yasa ta niyyar ba zata canza d'in ba, haka ita ma ta fita daga gidan rai a b'ace, ko da taje salon saida tasa aka nemo mata maganin ciwon kai tasha dan gaskiya fa tasan ta maru, mari ne data tabbata daya sake mata na hud'u to kunnenta ko idonta zasu iya barin k'wallon kanta.

Mutanen wurin babu wanda bai fahimci me ake nufi ba, anyi shiru ne kawai saboda babu wanda ya isa yayi magana, sai dai kowa ya yarda Hajia ma tayi shiru ne yanzu saboda abin daga iyalinta ya fito, amma da wasu ne da tuni ta cire musu wando ta kai ta bisu da dariya, sannu sannu maganar ta fita daga falon ta kai farfajiyar gida, daga farfajiyar gida ta fita k'ofar gida, to fa iska na surarta yayi gaba da ita har wasu garin ma saida aka ji wannan tsirku, inda aka ma maganar ado da kwalliya cewa Hamna yar iska ce kawai, shiyasa ba tayi aure ba kuma ana gani an saka mata ido, iskancin ne ma ke tsakaninta da mijin yer uwarta, nan fa kowa ke fad'in albarkacin bakinshi, inda wasu ke fad'in ai muna ganinta cikin garin, tun tana hawan moto dama take more rayuwarta, yanzu kuma da take hawa mota ko magana ba ayi ba, wasu kuma fad'i suke ai sun ganta biki kaza da kaza ko kuma wacce da wacce ce k'awayenta, mutum kenan mugun icce.

Haka akayi rabon gadon Alhaji inda kowa yaja nashi babban raboπŸ˜‚, kowa ya k'ara yawan jari ya kud'ence abinshi, shagali kawai ake iyaye da yaransu, kowa ya k'ara d'ora yaranshi kan manyan harkoki, hakan ya tilastawa Ammar dawowa wata ukun bai cika ba aka duk'ufa harkokin duniya, wani lokacin kamar kanshi zaiyi bindiga tsabar abunuwa, yaje asibiti yaje station shaguna da sauransu, a hakan ma wai dan Amar ma da inda yake kulawa haka ma Kamal suna saka shi kowane b'angare tunda ya fara mallakar hankalinshi shi ma.

Tunda abun nan ya faru ko sannu shi da ita bata sake had'asu ba, ya watsar da al'amuranta ya sake rumgumar matarsa hannu bibbiyu, sau da dama sukan had'u ko wajen shiga mota ko farfajiya ko k'ofar gida ko kuma falon Hajia, amma kallonta ma baya yi bare yaga shigar jikinta abun ya dame shi, hasalima ko ganinta yayi canza fuska yake yi yayi abinda ya kawoshi yayi gaba.

*Wannan* shi ake kira da kisan mummuk'e, gashi dai ya fita harkarta kamar yanda take fad'a a kullum, ya daina ko kallon fuskarta, ko d'akin matarshi zai shiga ya ji tana ciki saida ya koma har sai ta fita, tun tana jin kamar dad'i take ji har ta fahimci ba dad'i take ji ba a zuciyarta, kawai tana nuna tana jin dad'in ne a zahiri, ita ma bata kula shi kamar yanda yake yi, sai dai bata jin dad'i ko kad'an. Amma kuma hakan baisa ta canza abinda duk shine ya jawo matsalar ba, sabon babin rashin mutumci da fitsara ta bud'e, Amie dama ita ma ba aure tayi ba dan haka ta taya b'era b'ari suke sharholiyarsu, yawan biki da bi-gari kullum cikinshi suke, sun shiga sahun manyan matan da ake kiran sunansu, wannan matsatsun kayan dai kullum sune jikinta, wani lokacin ko gyale bata d'orawa haka zata shiga mota.

Kud'i kullum cikin kashesu take wajen siyan anko na k'awaye da d'inki, anko ba wai guda d'aya ba a'a sama da haka, abune daya zama na yayi kowa na so a fad'i bikinshi, hakan yasa kamu bridel party kan amarya damu, duk wannan abubuwan anko ake fiddowa kuma tana siya da kud'i, wasu lokutan d'inkin da akayi iri d'aya akeyi duka yan mata, wani d'inkin ko wata shigar idan kaga sunyita ka rantse ba yayan musulmi bane.

Amar ne ma ya d'an fara k'orafi kan abinda take, shima daga baya ya ja bakinshi yayi shiru, Hajia na gani amma an rasa dalilinta na saka mata ido tana abinda ta ga dama, Ummy ce ke tsaye kanta take mata fad'a da magana, amma magana d'aya ce "Ummy ki yarda dani wallahi ba zan tab'a zubar muku da mutumci ba, ko ban fita biki ba ai zan je wajen sana'ata, dan haka ki kauda idonki daga abinda mutane zasu ce ko suke fad'a."

Hadiza taga canji sosai a game da yar ta ta, hakan yasa ta tambayi yar uwarta Amna, a lokacin Amna ta ji a cikin gidan cewa Hamna ta ma Ammar rashin kunya shi kuma yace ba zai k'ara mata magana ba, yanda taji ta fad'a ma uwar wanda hakan yasa ranta b'aci fiye da kima, a waya ta kirata ta fad'a mata tana son ganinta, wannan karan ko da ta zo ko wurin zama ba'a bata ba bare ruwa aka balbaleta da masifa, ta inda Hadiza ta fita bata nan take fita ba, ta mata fad'a sosai kamar yawun bakinta zasu k'afe, tana gamawa kuma tace ta tashi ta koma bayan ta bata umarnin ta fito da miji wata d'aya kawai idan ba haka ba kuma zata dawo da ita gabanta ko da hakan zaisa sai tayi shari'a da dangin uban nata, haka ta juyo ta dawo tun a hanya take tunanin abinda mahaifiyarta ta fad'a, cikin jin haushi take tambayar kanta waya fad'a mata abinda ya faru? Wa zata fitar a matsayin miji? Ita fa bata shirya aure yanzu ba ma, idan fa tayi auren ma asiri ya tonu fa?Tsaki tayi ta d'an daki sitiyari saboda tuna abinda mama ta fad'a, a hankali ta shiga jero kalmomin data fad'a mata a k'walwarta.

*"Ashe shiyasa kika zama tsagera, saboda mai fad'a aji a gidan ya tsame hannayensa daga kanki, to ke inba hauka irin naki ba duk gidan nan waye zai tsawatar miki inba Ammar ba? Sa'ada dama ba mazauniya gida bace, sannan tun farko ita da lieutenant sun riga da sun lalata ku da sangarta, colonel a shekara d'aya zaman da yake a gidan lissafaffe ne, Labaran kuma dama tun farko baya shiga sabgar iyalin Hajia saboda baya son ta ci zarafin mahaifiyarshi, dan shi zai iya yin laifi amma har Hajiarshi saita wanke ta tas, to Amar Junaid Jibril dukansu aikin banza ne, babu wanda ya damu dake ko tsirara zaki fita, mahaifinku kuma kinfi kowa sanin baya da lokacinku, to ki fad'a min inba Ammar ba waye zai sa ido akan ki? Ke ba ma ke kad'ai ba kaf yaran gidan shi kad'ai ne mai taka musu birki, dan haka ki same shi ki bashi hak'uri in ba so kike kiga b'acin rai na ba."*


Shawarar Amie tayi aiki da ita wajen fito da *Habib* a matsayin wanda zata aura, ba wai dan tana son shi bane sai dan shine yafi tsarin da take son mijin aurenta ya kasance, ba'a wani tsaya bata lokaci ba aka shigar da manya maganar kuma suma suka nuna manyantaka, dan danan aka saka rana inda aka kawo kaya, k'ok'arinshi ya birgeta dan yayi bajinta sosai. Matashi ne dake da jini a jika da ji da dala, nan fa, matarshi d'aya da yara biyu, nan aka fara shirye shiryen bikin Hamna su Amie aka fara shiga da fita, sai lokacin take tambayar Hamna me ke tsakaninsu da Ammar? Saboda taga sun had'u shi zai fita su zasu shigo ko kallonsu baiyi ba, data fad'a mata abinda ya faru sai ita kanta taji ta samu damar da zatayi aure, dan dole ta shigar da kanta wajenshi, ta mayar da wasa gaskiya ta zama mallakinshi, fad'ansu da Hamna kuma nasara ce wurinta, dan hakan na nuna Hamna ba zata shiga abinda ya shafeki ba, ma'ana ba zaisan komai a kanta ba, tunda k'awayence ne ake abisa taka dokar mutumtaka, Hamna tasan Amie sarai tasan rikakkiyar karuwar alhazan birni ce, amma duk da haka tana tare da ita, wanda hakan ma ya taka rawa sosai wajen goga mata pantin da ake mata kallon mutuniyar banza ita kanta.

An fito da anko kala har hud'u, sun shirya sun had'u da abokan ango sun fad'a musu abubuwan buk'atarsu, sun d'auki wanda hankali zai d'auka sun aje musu sauran, shirye shirye sunyi nisa sosai, amma har yanzu Hamna bata jin farin cikin da wannan aure, tana yin komai babu kuzari a ciki ko alamar so, idan suna hira da Habib wani lokacin Ammar ya kan shigo gidan, a matsayinsa na musulmi kuma wanda ya ga mutane yana sallama ya kuma bawa Habib hannu su gaisa, amma bai tab'a yarda idonshi da nata sun had'u ba sai dai ya fice, haka zata bishi da kallo har ya b'ace ma ganinta, haka ita dai take sukuku sai lokaci kuma dake k'aratowa.

*Har* bacci ya fara gaba dashi Amna ta tashe shi kan ya manta bai siyo madaran daya yara sabonta ba, kowa zai iya bacci bai sha ba amma banda *Ameera*, saida ya lumshe ido yace "Ke dai kina jin bak'in cikin kiga na kwanta baccin alhalin ke ma baki kwanta ba ko?"

Dariya tayi tace "Ta ya ba zan so ganinka kana hutawa ba? Ai farin ciki na ne."

K'ok'arin saukowa daga kan gadon yayi yana fad'in "K'arya kike, ai da sai ki tuna min tun kafin na shigo gidan."

A hankali tace "Wallahi na manta ne gaba d'aya, kuma naga tun kafin ta ida kake kawo wata."

Cikin sumalin bacci yace "Bansan ya akayi bane na manta wallahi, yanzu kuma zata hana kowa bacci a gidan nan in babu ita."

Da kallo ta bishi har ya canza kaya zuwa k'anana ya d'auki makulli yana fad'in "Allah yasa a samu a kusa."

Suna fitowa a falo ta samu Ameera kwance yanda ta barta tana ta latsa remonte tana canza tasha, kusanta ya matsa ya sunkuya yace "Gimbiya Ameera, yarinyar mamanta da babanta, yarinya yar baiwa mai sa'a, shalelen Ummy da Abba, zaki sha bonbon (alawa)?"

Kai ta girgiza mishi tare da cunno baki gaba cikin muryarta ta yara tace "A'a ni madaya na ke co."

D'agowa yayi ya kalli Amna yace "Duk yanda akayi ke kika sa mata akai ta daina yarda duk wayon da za'a mata."

Dariya tayi tace "Banda abun uban yan biyu waye zai shiga tsakaninka da yaranka?"

Ameera ya kalla yace "Muje to ki raka ni na siyo ko."

Tsil ta diro daga kujerar tana jujjuyawa inda zata ga takalminta, tana ganinsu ta d'auka tasa ta rik'e hannunshi, saida ta juyo ta ma Amna bye bye tace "Ummy sai mun dawo."

"A dawo lafiya." Ta fad'a tana zama, kallonta yayi yace "Me kike so na taho miki dashi?"

D'an d'aga ido tayi alamar zatayi tunani yace "Zaki sha ayaba?"

Kallonshi tayi saita yamutsa fuska tace "Bana jin dad'inta yanzu."

Tsayawa yayi yana mata wani shu'umin kallo yace "Tunda kika samu tawa ko?"

Bushewa tayi da dariya tare da rufe fuskarta da hannu d'aya tana fad'in "Ba haka bane."

Hararanta yayi yace "Ba haka bane kamar ya? Kin samu lafiyayya kina ta moreta tana zazzaga miki yara bigu biyu biyu dole ki ce wannan ta fita a ranki, to kiji da kyau ita wannan d'in da kika raina sanfirin aubangiji ce."

Tsayar da dariyarta tayi tace "To ai ita ma waccen d'in hakane."

Juyawa yayi yana fad'in "Tunda kince haka bari na dawo yau zan sake baki ajiyar wasu yaran, amma wannan karan uku zan ajiye."

Murmushi kawai tayi ta bisu da kallo, wannan magana kamar ya fad'a ne daidai amsawar mala'ikun rahama, a ranar ta gama al'adarta ta kimtsa kanta dan farin cikin mijinta, dama magani ne Ummy ke d'orata akai wanda shi tafi so, a ranar ma tasha zuciyarta babu tunanin komai, amma da yake akwai tsananin rabo sai gashi duk da babu tabbacin a wannan dare ya shiga amma daga lissafi za'a gane a wannan lokacin ne.

Sanda ta fara jin alamu ta d'auka ucler d'inta ce kawai ta zo mata da sabon salo, amma sai abun ya fara damunta ganin tana shan maganinta kuma a banza, saida taji bata son warin gas d'in da take aiki dashi ta fara tunanin ciki ne da ita, da sauri ta d'auki tsinken gwaji ta ma kanta, ai kuwa dai ta tabbata abinda take tunani, zaune tayi kan gado jiki a sanyaye ta dafe kai da hannaye biyu, k'walla taji sun cika mata ido tana shirin yin kuka, shigowarshi tasa ta zabura tana goge hawayen, b'oye tsinken tayi a hannunta tana kallonshi, shi ma wani tuhumammen kallo yake mata har ya tsaya gabanta yace "Lafiya?"

Kai ta girgiza masa kawai tana shirin fita daga d'akin, rik'ota yayi yana kallon fuskarta yace "Fad'a min me ya faru?"

Fuskarshi ta kalla sai kawai ta fashe da kuka ta fad'a jikinshi, cikin tashin hankali yace "Ke Amna lafiya? Me ya faru ne wai? Me aka miki? Ni ne na tab'a ki?"

Share hawayen ta fara yi hakan yasa shi tallabo fuskarta yana fad'in "Kiyi hak'uri idan nine na b'ata miki rai kinji, ban sani ba wallahi."

Girgiza kai tayi alamar a'a, had'e girar sama da k'asa yayi yace "To me ye kike ma kuka?"

A hankali ta nuna masa hannunta ta bud'eshi daga dunk'ulewar data masa, hannu yasa ya d'auki tsinken ya duba sai kawai ya kalleta yana murmushi yace "Kice min har na cika aiki?"

Cike da damuwa tace "Yah Ammar bana so? Ciki ne fa?"

Da mamaki yace "Ba kya so Amna? Cikin na wa?"

Marairaicewa tayi tace "Yah Ammar ka fahimta mana, duka fa aurenmu har yanzu bamuyi shekara hud'u ba."

Ba alamar wasa yace "Sai akayi me?"

Turo baki tayi tana d'an juyawa tana fad'in "Ni gaskiya bana so, haba kamar wata kaza."

A hankali ya juyo da ita gabanshi yana kallon idonta yace "Shin ni ne kike so ki kira zakara a fakaice ko me? Amna miye na damuwa dan kin haihu sau uku a cikin shekaru hud'u? Haihuwar ince ba Allah bane ke bayarwa ba?"

Kamar za tayi kuka ta kalleshi tace "Eh hakane yah Ammar, amma kuma ai ana so a d'an huta, ka dubi su Alhaji fa ba suyi wayo ba har yanzu.

Saida ya gyara tsayuwa yace "Amna ince dai ni na miki cikin?"

D'aga kai tayi alamar eh, d'orawa yayi da "Kuma ni zaki haifa ma yaran ko?"

Nan ma kai ta d'aga sannan yace "To indai nine uban ina son kayana, ko duk wata ne ki bultso min su zan karb'a, duk wanda kika ga ya miki kallon rashin mutumci kallon daya nuna ana mamakin haihuwarki, to ki kalli k'wayar idon mace ki fad'a mata duk macen da mijinta ke sonta ita ke rirritsa."

*To fa kunji wanda basa son haihuwa*

Cire kayan jikinsa ya fara yi zai shiga wanka yana fad'in "Ke ba ma dan baki da hankali ba sakarya ce ke, to miye na ki na damuwa ke da bake kika ma kanki cikin ba, ba saida na tab'a ki ba sannan kika yi cikin, wacce miji bai damu da ita ba zai tab'ata ne, yanzu fa da a shekara hud'un nan bamu samu haihuwa bane saiya zama tashin hankali har ana nuna mu da baki, a'a ka na daddage nayi cikin shima sai an min uya shege da buru-uba, to naje nayi d'in kiyi abinda za kiyi idan kin isa."

Ban d'akin ya shiga tana ganin haka ta fito daga d'akin bata zame ko ina ba sai b'angaren Hajia, dan in ta zauna ya fito ma d'orawa zaiyi har jarabar ta motsa ya tattausheta a banza, dan yanzu ya fad'a mata ba duka ba zagi amma taji a jikinta, ita kuma a yanda Allah ya halliceta har tafi son dukan ma kan irin wawurar daya mata wani lokaci wacce ta kwana tana amai ga zazzab'i, duk da dai tasan yafi ta ma damuwa da kanta indai aka ce tana da ciki ko tana shayarwa, tanan b'angaren kam sai san barka.

Ai kam dai kamar yanda tayi tunani ne, dan ko da ya fito da masifar ya fito yana fad'in "Ke ni ban ma yarda dake ba, wallahi sai kin fad'a min ni ne ba kya so ko yaran ne kike bak'in cikin haifa min, in kuma raino da shayarwa ne baki iyawa fad'a min na ji."

Shirun da yaji yasa ya d'auka ko tana falo, haka ya fito da towel d'in niyyar shi in tayi wasa ta sha matsa, amma sai bai same ta ba, murmushi yayi ya jinjina kai yace "Wato ta bar min gidan ma gaba d'aya ko, ga dodo wanda baisan ciwon kansa ba, ga mahaukaci idan nayi na gaji na bari kenan."

Komawa yayi ciki yayi k'wafa yace "Zaki dawo ai zan ritsaki ne."

*Sati uku* ya rage bikin Hamna, yau kuma ta tashi da shagalin bikin k'awarta da ita ma zatayi aure, ta shirya ma bikin sosai saboda a cewarta shine fitarta na k'arshe kafin ta fara gyaran jiki, d'aya daga cikin abokan Ammar ne na gaban goshinshi zaiyi mata ta biyu, dan haka babu abinda bai shirya halarta ba shima dan saka mishi da alkairin daya mishi. Rana ta farko anyi k'umshi, ta ganshi ya ganta sanda suka je d'aukar abinci, amma kai ka rantse wasu abokan hamayya ne dan babu wanda ya nuna yasan wani ma, a daren ranar akayi kamu inda aka rak'ashe sosai, ya kalleta yafi sau cikin carbi, tana wahalar da zuciyarshi sosai, tana gigita lissafinshi, tana sage mishi duk gwiwoyinshi, yana kishinta fiye da hangen mai tunani, yana jin zafin ganin tana bayyanar da abinda ya kamata ace ta mayar dashi sirrinsa shi kad'ai, sai dai babu ta yanda zai fahimtar da ita haka, baisan ta wace hanya zai bi ya nuna mata yafi kowa son ganin ta killace kanta, amma ya zaiyi da abinda yafi k'arfin wuta inji kishiyar k'onanniya, ya zuba mata ido tayi abinda take so, ko ba komai ma ai ta kusa zama ta wani, mallakin wanin shi ce ita.

Anyi bridel a rana ta biyu inda yan mata ne zalla da amarya, sai kuma rana ta uku da angaye ne suka shirya tasu didimar, ya jima da shiryawa ya fita saboda kai da kawonshi yawa gare shi, lokacin da suka zo yana k'ofar gidan da ake gwangwajewar tare da wasu abokinsu suna shigar da ruwan roba ciki, yana juyowa motarsu ta danno wajen, ta glishin motarta ya fara hangosu suna fitowa daga ciki, su hud'u babu mai k'asa da shekara ashirin da biyar a cikin, sun rik'a sun tumbatsa sai haniniya sukeπŸ™ˆ, in ba wanda yasan su ba kai kace ba girman garin musulmi bane, dogaye riguna ne duka jikinsu iri d'aya, kalar pink ce sai yar kwalliyar da aka musu a tsakiyar k'ugun rigar, sun kama su sosai a jiki sun fito da duka hallitinsu, dogayen takalmi ne k'afar kowace sai k'ananan poshet a hannayensu, biyu daga ciki haka suka zuba atach d'in babu kitso babu d'an kwali, Amie kuma kitso ne na atach mai kamar na roba, sai Hamna dake da korde a kanta kitson yayi kyau sosai, kallabin Amie a hannunta yake ta rik'e, Hamna kuma ta d'an d'aura shi ne tsakiyar kan wanda kamar jira yake a tab'a shi ma ya b'are, dukansu sun sha uwar kwalliya mai d'aukar hankali. Har sun fara d'aukar hotuna ko da ta ganshi sai kawai ta shige ita ma, Amie ce ta zo kusanshi tace "Namijin duniya barka."

Juyowa yayi ya kalleta
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment