Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ba, wayarta ce tayi k'ara ta fito da ita daga jaka, saida ta ga sunan kad'ai ta iya tuna ashe fa tare suke, da sauri ta juyo dan fitowa ta same shi tana fad'in "Na manta ashe yana waje."

Kallon juna sukayi inda kawu Mamu yace "Kinji shiririta, tare suke ta baro shi waje."

Duk hayaniyar da suke a cikin gidan yana ji, sai dai rabi fulatanci ne rabi kuma hausa, hakanne yasa shi cabko matsalar da suke magana akai, sannan yaji sunan d'an shi ma ya fito da kuma ta'asar da yayi, dan haka ya kirata a waya dan da alama ta manta shi a k'ofar gidan. Tana zuwa ta marairaice tace "Alhaji kayi hak'uri dan Allah na barka k'ofar gida, wallahi su kawu ne suka rik'e ni da magana."

Babu alamar wasa a tare dashi yace "Me yake faruwa? waye zai rufe shi akan kud'i? Me kuma ya had'a Ammar da Jumare?"

Baki ta saki tana kallonshi da mamaki da kuma rashin jin dad'i, kenan ya ji komai? Oh Allah, cikin taushin murya tace "Ba komai."

Kafeta yayi da ido yace "Ya zaki ce ba komai, duk da ban ji komai ba amma ai na fahimci inda zancen ya dosa, fad'a min meke faruwa?"

Cike da rangaji tace "Idan mun koma gida zan fad'a maka, amma Abban Ammar ban so kayi hushi."

"Shikenan, yanzu ya mai jikin?" Dariya ce ta kubce mata ta rufe baki, dan ya bata dariya sosai data tambaya, hakan na nufin baiji abinda aka fad'a anan ba kam, klonta yayi yace "Meye?"

Girgiza kai kawai tayi ba tace komai ba tace "Shigo muje." Girgiza kai yayi da sauri yace "A'a, idan dai zasu iya ki fad'a musu ina waje, in kuma kwance suke kawai ki gaishe min su sai ki fito mu koma."

Kamar zata fashe da kuka tace "Lahh, na d'auka fa nan zaka barni da naga mun taho da wuri."

Hararanta yayi yace "Lafiya kike? A halin da kike ciki kulawa kike buk'ata, sannan hidimar da akayi duk kin gama wahalar min da kanki da baby na, dan haka ba zan barki ba, ki shiga ki fito mu koma daga baya kya dawo ganinsu."

Juyawa tayi ta nufi ciki har da buga k'afafu take tana kukan shagwab'a, da murmushin birgewa ya bita cike da k'aunar yarinyar. Tare suka fito da kawu Mamu suka gaisa sosai, da zai tafi ma wasu kud'in ya sake bashi, babu kunya babu kawaici ya karb'a yana godiya kafin ya koma ciki suma suka tafi.

Tun a hanya ya sake tambayarta abinda ke faruwa, tsaf ta fad'a mishi amma banda marin da Ammar ya wa Jumare, dan haka yace "To ita kuma Jumare da waccen ya mareta fa?"

Cikin turo baki tace "Jumare fa rashin kunya ta min shine ya hukunta ta."

Kallonta yayi yace "Ban gane ba? To shi shi ta wa da zai mareta? Ke fa naga alama kin d'aukeshi wani mutumin arzik'i."

Wani kallo ta mishi mai kama da na tsani kalmar daka fad'a, sake kallonta yayi sai yaga ta k'ura mishi ido tana kallo, d'aga mata gira yayi yace "Lafiya?"

Had'e rai tayi sosai alamar bata ji dad'i ba tare da kawar da kanta gefe, cikin d'an d'aga murya yace "Wai meye? Wani abu na fad'a daya b'ata miki rai ne?"

Juyowa tayi cikin tsananin masifa har ta manta dawa za tayi magana sai ta fara fulatanci tana fad'in "Gaskiya ni na baku kyautawa, d'an da kuka haifa a ciki kuna fad'a mishi duk abinda ya zo bakinku, yanzu meye na wani cewa wai ina ganinshi kamar mutumin arzik'i, to mutumin banza ne dama? Akan me zaka fad'i haka a kanshi?"

Tunda ta fara magana ya saki baki yana kallon nata bakin, yanda ko wane harafi ke fita na bakinta abun birgewa, masifa take amma kuma ta mata kyau, sai dai abun takaicin baiji komai data fad'a ba, bakinta kawai ya gani yana motsawa da sautin harrufan da take furtawa, kallon gabanshi yayi yace "Idan kin gama fad'an saiki fad'a min me kika ce ko."

Sak'e tayi ta kalleshi, wai dama ba da hausa tayi magana ba? Kawar da kanta kawai tayi ita ma har suka isa gida, katari kam suna shiga sun aje motarsu Ammar shi kuma zai shiga tashi motar, da mutuntawa ta kalli Zeituna yace "Uwa barka, daga pakarey ake?"

Murmushi tayi duk da bata san me yake nufi da pakarey d'in ba, kallon lieutenant yayi yace "Alhaji ya ake ciki?"

Banza yayi da shi zai wuce Zeituna ta d'an rik'o rigarshi, tsayawa yayi ya juyo ya kalleta da alamar tambayar lafiya, saida tayi kamar zata fad'a jikinshi ta kashe murya sosai tace "Magana fa yake maka, dan Allah ka amsa mishi, laifin me yayi maka?"

Cikin fad'a yace "Ke baki ji me yayi bane? Ina ubanshi zai wani ce min ya ake ciki, dallah rabu dani."

Fizge rigarshi yayi ya juya zai wuce, kukan shagwab'a ta saka tana fad'in "Shikenan nagode da abinda ka min."

Juyowa yayi yana ganinta ya dawo yana fad'in "Wai ke meye haka? Dan Allah wuce muje."

Juyawa tayi ta kalli Ammar daya ke daf da shiga mota sannan ta kalle shi tace "Babu inda zanje yau sai na gani da ido na kuma naji da kunnuwa na ka lokacin da zaka sa mishi albarka, inba haka ba kuma yanzun nan na koma inda muka je yanzun."

Yanda tayi maganar ya nuna rigima take ji, sai dai shi a wurin shi ba wani abu bane da ita take kambama shi har haka, turo baki yayi kamar yaro yace "Kira shi to."

Take murmushi ya maye gurbin fuskar shanun nan, sam farin ciki yasa ta manta sai ta k'walla kiran sunan Ammar daya shiga mota har ya tayar, bai ji kiran farko ba saida ta kura shi sau uku sannan ya fito daga motar, cike da takon k'asaita ya zo gabansu ya tsaya yana kallonsu.

Kallonshi lieutenant yayi babu annuri yace "...


*Alhamdulillah*
14/10/2020 ร  00:58 - Ummulkhairi: ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ
*BADAK'ALA*
๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ

*Labarin Gaske*

*NA*

_SAMIRA HAROUNA_

*Litattafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._

*SADAUKARWA GA*

๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ _*AHALI NA*_๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

๐Ÿ‡ณ๐Ÿ‡ช *TAURARIN NIGER*
```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)```

โœช{T . N}โœช๐Ÿ“–๐Ÿ–Š๏ธ

https://www.facebook.com/101305508365889/posts/101311008365339/?substory_index=0&app=fbl


_Bismillahir rahamanir rahim_

_40_


"Ina zaka je yanzu da dare? Baka san yanzu ka girma bane?"

Wata yar banzar dariya ya bushe da ita kamar da bakin k'warya, galala Zeituna ke kallonshi inda lieutenant ya nuna mata da yatsa yace " Kin gani? Ina fatan yanzu kin fahimci wani abu."

Babu alamar wasa a fuskarta ta kalleshi tace "Tambayar daka mishi ai tana nuna damuwarka ne a kanshi, shi kuma abun ya zo mishi a bazata ne, na tabbata abinda ya bashi dariya kenan, idan kuma baka yarda ba ka tambaye shi kaji."

Kallon Ammar yayi da har yanzu ke dariya har da rik'e ciki yace "Dallah ka mana shiru malam."

Shirun yayi yana kallonshi, saida ya saisaita nutsuwarsa sannan yace "Zan fita ne Alhaji, asibiti zanje, akwai marasa lafiyan da zan gani nan da minti ashirin."

D'an jinjina kai lieutenant yayi alamar gamsuwa tare da cewa "Saika dawo, amma karka cika dare ka bar min 'yata ita kad'ai, kasan har yanzu bak'i ne su."

Juyawa yayi bai ce komai zai tafi sai kuma lieutenant yace
"Dama ina son ganinka." Dawowa yayi yana fad'in "Gani."

Saida ya saci kallon Zeituna kafin yace "Yarinyar da ta zo d'azu gidan nan me yasa ka mareta? Baka san yer uwarta ce ba?"

Kallon daya ma Zeituna yasa lieutenant cewa "To ba ita ta fad'a min ba, yanzu daga gidan muke kuma ran iyayenta ya b'ace, har naji mahaifinta na cewa ma zai zo har gidan nan ya rama mata."

Wani murmushin yau ga banza ta samu ya ma lieutenant, mayar da kallonshi yayi ga Zeituna yace "Uwa ni kam ina ne gidanku ma?"

"Babu nisa da nan ai, kana shiga kwanar..." A firgice lieutenant ya kalleta saboda jin zata kwafsa, shi fa ya fita sanin waye d'anshi, shi ya haifi abinshi, dakatar da ita yayi da cewa "Ke kuma miye haka? Daga ya tambayeki saiki fad'a masa."

Kallon ashe ka harbo jirgin ya masa tare da sakin murmushi yace "Abba hak'uri zanje na basu, kace yace zai zo har nan, ku surukai ne bai kamata a samu matsala a tsakaninsu a dalilina ba."

Da sauri Zeituna tace "Kwanar beautรฉ salon, a jerin gidan Alhaji Chapi'u cikin bukkokin nan."

Murmushi yayi sosai wanda yasa hak'oranshi fitowa saboda jin dad'i, lumshe ido lieutenant yayi alamar shikenan, ta fad'a an gama kuma, juyawa ya sake yi sai kuma Zeituna ta kalli lieutenant kallon dake ankarar dashi bai mishi addua'r ba, yanda ya kalli Ammar yasa shi tsayawa yace "Alhaji kana son wani abu ne?"

Saida ya k'ara gimtse fuska sannan ya d'aga mishi hannu alamar ya zo, matsowa yayi kusa da shi a lokacin ya dafa kanshi ba tare daya kalle shi ba yace "Allah ya maka albarka, saika dawo, ka kula da kyau, kada kayi abinda zaka zubar mana da mutumci."

D'ago kai yayi ya kalle shi, tabbas dai shine daya sani ya saka mishi albarka, sai dai ba yayi ne saboda ya cancanta ba, baiyi ba saboda ya haife shi, yayi ne saboda an sa shi, jinjina kai yayi alamar to tare da kallon Zeituna, murmushi ya mata na jin dad'in namijin k'ok'arin da tayi yace " Nagode uwa."

Kallonshi yayi tare da juyo mishi kumatunshi yace "Ka k'arasa kadarka Abba na."

Kallon ban fahimta ba ya mishi yace "Ban gane ba? Me kake nufi?"

Kallonshi yayi yace "Sumbata ta zakayi, yaushe rabon da kayi haka dan Allah, ko da muna yara ma baka cika yi ba saboda kai ba mazauni bane."

Kallon Zeituna lieutenant yayi ya gimtse fuska, da ido ta masa alamar kayi mana, sake matsowa yayi yace "Abba sauri nake fa."

Saida ya rufe ido ya fara matso da fuskarshi kusan tashi, a hankali ya sake bakinshi kan lallausan kumatunshi had'e da k'asumbarshi, a hankali ya sauke mishi sumba mai kyau inda Zeituna taji sautin "Mtsss."

Wangale baki tayi tsabar farin ciki kamar an mata albishir da gidan aljanna tace "Weeee, munyi nasara."

Kallonshi Ammar yayi ya rik'o hannunshi, yana so yayi magana amma yana jin kamar ba zai iya ba, sai dai daga kallon da yake aika masa zaka fahimci shauk'inshi da kuma kaunar mahaifinshi, sakin hannunshi yayi ya juya zai tafi sai kuma ya tsaya ya juyo, kallonshi yayi yace "Nagode Abba, da ina samun irin haka kullum kaso hamsin na abinda ke zuciyata zai warke."

Kallon Zeituna yayi yace "Uwa ce ke mai wuyar samu, uwa mai tsadar gaske."

Yana fad'a ya juya barsu nan tsaye, kallon Zeituna yayi yace "To yanzu kinji dad'i."

Turo baki tayi gaba ta girgiza tace "Fiye da zatonka."Juyawa tayi da sauri ita ma ta nufi babban falo ta manta da lieutenant tsaye, bin bayanta yayi yana mamakin halinta da yarinta, wato dole indai ka auri yarinya komai tsufanka sai tasa wata rana kayi k'uruciya kai ma.

Tun magriba ta shirya tare da Huda tana jiran shigowar Junaid dan yasan abinda ke faruwa, tayi niyya zata zauna anan tare da yarta, idan kuma yace bai yarda ba zata nuna mishi sai dai ta bar gidan, tasan kuma yana sonta ba zai yarda ta bar gidan ba. Bai shigo ba sai bayan sallah isha'i, yana sallama Huda ta tafi a guje ta rumgume shi saboda sabon da sukayi na kwanakin baya, shima rumgumeta yayi cikin farin ciki yana fad'in "Huda ke ce a gidan namu? Yaushe kika zo?"

Saida ta d'ago ta kalleshi tace "D'azu muka zo ni da tanti Iklima."

Da farin ciki yace "Da kyau, kice ziyara kika kawo mana, amma dai zaki kwanar mana anan ko?"

Juyawa tayi ta kalli mahaifiyarta dake tsaye bayansu, k'arasa mik'ewa yayi tsaye shima yana kallonta, kwalliya ce tayi ta d'aukar hankali da fitar hayyaci, k'ananan kaya ne jikinta wanda suka nuna komai, murmushi ta sakar masa tare da matsowa ta rumgume shi, cikin kunne ta rad'a mishi cewa "Sannu da zuwa gwarzona."

D'an sumbatar kumatunta yayi tare da cewa "Sannu da gida."

Juyawa Huda tayi ta koma kan kujera ta zauna, binta yayi da kallo sannan ya kalli Maryama yace "Amma anan zata kwana ko?"

Kama shi tayi suka nufi d'aki tana rik'e da k'ugunshi tace "Eh, ai dama da aka taho da ita ba dan ta koma bane, zata zauna anan ne tare dani, tunda kaga Mama ba lafiya ne da ita ba, Inna kuma girma ya zo ba zata iya kula da ita ba."

Sam shi dai baiji wani abu ba a game da zaman Huda anan, sai dai yasan zasu samu matsala da Hajia, haka ma mahaifiyarshi dake da tsegumi, zata ga kamar yarinyar zata gaje shi ne, jin shiru yasa ta lek'a fuskarshi tace "Ya dai? Ko baka amince bane?"

Kallonta yayi yace "Haba dai, wacece Huda da har zan kasa amincewa? Ko ba komai fa yarinya na samu a sauk'i."

Murmushin jin dad'i tayi ta rumgume shi tace "Nagode gwarzona, Allah ya bar min kai."

Tun daga falo sautin kuka ke tashi har zuwa uwar d'akin, yayi rarrashin duniya da ban baki amma ta k'i dainawa, yayi duk yan dubarun daya sani amma maganar d'aya ce har yanzu ita ce "Wallahi zafi, ciwo nake ji, shikenan mutuwa zanyi, ni kawai ka kaini wurin Mama na."

Tagumi ya zuba yana kallonta, da farko tausayi take bashi saboda shi kanshi yasan ta aikatu sosai, bai d'auka zata jure wahalar daya bata ba, amma da tafiya ta tafi saita fara bashi haushi saboda ganin kamar da gangan take yi, amma yanzu mamaki kawai take bashi, dan shi dai baiga abun jininin ba. Duk da taga irin kallon da yake mata baisa ta daina kukan ba, har ga Allah zafi take ji ta yanda tana zaune ne kawai saboda kar yaga rakinta yayi yawa, ganin ya k'ura mata ido ya daina rarrashinta ma wanda ke sa ta d'anji dad'i yasa ta k'ara bud'a murya tana murza k'afafu k'asa da yarfa hannaye tana fad'in "Ni kawai ka kaini wajen uwata, Allah ba zan zauna da kai ba yah Jibril, haka kawai duk ka rugurguza ni daga wasa, ni ba zan iya ba ka kaini gida kawai."

Cire tagumi yayi ya rufe baki yana dariyar mugunta, lallai yayi babban laifi, domin kuwa daga yan shafe shafe ko da taga zai wuce gona da iri ta fara tsora ta so zille masa, amma saiya kwantar mata da hankali da cewa ai kawai wasa ce yake mata, data tambaye shi da mamaki tace "Wasa fa?" Sai cewa yayi "Eh mana, Hajia ta had'a mu da k'annanmu ba dole mu dinga muku wasa ba."

To fa daga nan ne aka yi tazarce ya mata baja-baja, ko da ta lura dariya yake mata saita k'ara himma, cikin dariya ya jawota jikinshi ya rumgume, d'ago kanta yayi ya saita bakinshi cikin kunnenta yace "Yi hak'uri mana 'yar k'anwata, ba zan sake ba daga yau kinji, kukan ya isa haka kar kisa na d'auka ke raguwa ce ba zaki iya dani ba."

Da sauri ta mayar da kanta cikin k'irjinshi ta rufe fuska, dariya yayi yana k'ara matseta yace "Kin hak'ura yanzu?"

Kai ta d'aga mishi alamar eh, sake matseta yayi ya jingina bayanshi a kujerar yana shafata, cikin saisaita murya yace "Idan Allah ya tashe mu gobe ki tasheni da wuri, dan dole naje na gaishe da kakarku na kuma gode mata data bani ke."

D'an d'agowa tayi tace "Kakarmu? Kai fa?" Girgiza kai yayi yace "Jamila ba zan uya da kakarku ba, ku dai kuyita hak'uri da ita wata rana sai labari."

Jinjina kai tayi tace "Lallai ma, ai kuwa zanje na fad'a mata abinda ka ce."

Murmushi yayi ya sumbaci goshinta yace "Ni ma saina had'ata da hawan jininta."

Kallonshi tayi tace "Hawan jininta kuma?"

"Eh mana, babban yayanmu ba, Ammar." Murmushi tayi ita ma tace "Allah sarki besty Amna, ko a wani hali take?"

Bushewa sukayi da dariya dukansu inda yace "Bana jin a shekara goma zata fahimci mutumin nan."

Cikin sanyi jiki Jamila tace "Zuwa lokacin da zata fahimce shi kuma jikinta ya farfashe da duka, zagi kuma tayi buhu buhu har ta fara siyarwa ita ma."

Cikin dariya Jibril yace "Bak'ar magana, yab'a magana, gatse, habaici, maganar rashin kunya kuma zasu zama abincinta ne, shiyasa na so Hajia ta had'a shi da kankana, ko ba komai mun daina kallon tv daga ranar, dan kullum da dramar da zamu gani a wajensu."

Girgiza kai Jamila tayi tace "Zasu wahalar da junansu ne ai, ita dai bata jin magana, cikin sauk'i ba zai ce ta bari ta bari ba, shi kuma ba nauyin duka yake ji ba, amma kaga Amna tana tsoronshi dama, ko had'a ido bata iya wa dashi, kaga za'a samu sauk'i."

"Kema kince wani abu." Ya fad'a yana kallon tvn dake aiki, haka suka ci gaba da hirarsu akan Ammar suna yi suna dariya, a irin hakane har Jibril ya bata labarin wani abu daya faru a shekarun bata da yawo.

*A duk cikin labarin nan wannan labarin da Jibril ya bayar shi yafi sani dariya.*๐Ÿ˜‚

Abun ya faru ne shekara d'aya da dawowar Ammar daga Canada, a lokacin ba'a gyara wurin hutawar dake bayan gidan ba, da sassafe ne tashinshi kenan ya zagaya da wayarshi a hannu, yana zuwa ya samu Hamna da Amna suna nishad'unsu bakin bishiya, kamar an koreshi daga sama saiko k'adangaren nan ya fad'o saman hannun Hamna, wanda yanzu haka akwai shatin yagin daya mata, k'wala k'ara tayi ta zabura ta mik'e tsaye ta fara rawar disko a wurin ido rufe tana ihu tana neman a taimaka mata, Amna da ita Allah bai saka mata tsoron wannan abubuwan ba rik'ota tayi jikinta ta buge k'adangaren da shima ya gigice yake neman hanyar barinta, tana bugeshi ya kama gabanshi shima, shiru tayi suna kallon k'adangaren daya bar wurin, daga bayansu Ammar dake ganin komai yace "Shegiyar kankana, ashe sakara ce ke, d'an waccen abun ne kike ma wannan zullon har kina neman cire da siket d'inki."

Juyowa sukayi suka kalleshi, turo baki tayi ta harareshi tace "Eh d'in, ina ruwanka?"

Dalla mata harara yayi yace "Ke ki kiyaye ni wallahi, ni ne maraininki kenan da zaki juya min d'an banzan baki kamar na tsaka."

Murgud'a baki tayi amma ba tace komai ba, juyawa yayi zai bar wurin Hamna ta bishi da harara tace "K'aton wofi, dube shi watak'ila shima tsoronsu yake."

Tsaf a kunnenshi, a hankali ya juyo ya fara takowa kansu yana saka wayarshi aljihu, haba ai sai tattare siket tana shirin zabgawa a guje, tako biyu yayi ya fizgota ta dawo baya, rik'e hannunta yayi sosai ya fara kallon bangon wurin yana fad'in "Yanzu zakiyi tsallen mai digri idan ya shiga rigarki ya sosa miki baya."

Ko da taji haka ta durk'ushe duk da yana rik'e da hannunta ta fara kuka tana bashi hak'uri, cire slipas d'inshi yayi ya wurga ma wani k'adangare da ya zo wucewa, tip ya fad'o k'asa a mace, janta yayi k'iiii saida ya kaita kusan k'adangaren ya sunkuya ya d'aukeshi da hannu, tana ganin ya d'auka ta k'ara zabga wata k'ara iya k'arfinta, yana nufowa dashi kusanta ta lumshe ido ta lamgab'e tana shirin fad'uwa k'asa, da sauri ya rik'ota yana kallonta, suma tayi da gaske, d'ago idon shi yayi ya kalli Amna dake gefe d'aya ta takure, cikin shan kunu yace "Kawo ruwa."

Da gudu ta juya dan kawo ruwan, yana ganin ta tafi ya saki Hamna ta fad'i k'asa da k'arfi, wayar shi ya fiddo ya ci gaba da latsawa, Amna na zuwa jikinta sai rawa yake kamar ita ce ya damk'a, mik'a mishi ruwan tayi ya juyo ya mata wani kallo, har zata bud'e ta zuba mata sai kuma yasa hannu ya karb'a, yana bud'e bakin robar ya shek'a mata su a fuska, a firgice ta mik'e tana sakin yar k'ara, yana ganin ta mik'e ya jefa mata robar ya nufi hanyar fita, Hamna da takaici ya gama kasheta sai cewa tayi "Allah ya isa sojan banza sojan wofi, k'wara da baka zama sojan ba nasan da duk ka harbe kowa, dan ba k'aramin marar imani za ayi ba."

Juyowa ya sake yi da sauri ya nufota yana sa wayarshi aljihu, Amna ce tayi saurin cewa "Dan Allah yah Ammar ka..." Bai bari ta fad'a ba ya mata wani jan kallo yace "Kina son kanki da rahama?"

Cikin tsoro tace "Ina so yah Ammar, haka kuma ina so wa yar uwata ma, dan Allah ka k'yaleta ba zata k'ara ba."

"To ina zuwa." Ya fad'a yana yin kan Hamna data mik'e tsaye tana kakkab'ar kayanta, kamar guguwa, guguwar wacce ta taso a tsakiyar sahara, haka taji ya sunkuceta yayi sama da ita baki d'aya, saida yaje bakin bishiyar daya same su zaune ya tsaya, kamar a tsarin film sai kuwa ya sab'ata a kafad'a ya rik'e bishiyar ya fara takawa yana hawa da ita, zullo take tana k'ara tana kiran sunan Ummy duk da tasan tana asibiti. Amna ma da gudu ta tafi tana fad'in "Dan Allah yah Ammar kayi hak'uri ka sauko da ita."

Ita a tunaninta idan ya hau zai sakota ne ta b'are baya kamar yanda yake wayan cewa wata rana saiya b'are mata baya, saida yaji ya hau inda ya mishi sannan ya tsaya ya tallabota ya mata d'aukar jarirai ya azata kan bishiyar, zaunar da ita yayi sannan ya dirko daga kan bishiyar da k'arfi, d'aga kai yayi ya kalleta yace "Dan ubanki kice tak ki gani idan ban sa aka kawo min zaki ba na d'ora shi anan shima, kedai kinsan me zai faru ai."

Juyawa yayi zai fita cikin matsanancin kuka harda shashek'a tace "Dan Allah kayi hak'uri boss, wallahi Allah ba zan sake ba na tuba."

Hannuwa yasa aljihu ya d'aga kafad'a yace "Kin tab'a ganin boss yayi niyyar shek'e mutum kuma ya hak'ura ya barshi a raye?"

Tafiya yayi ya barsu nan sai Amna data fara k'ok'arin taimaka mata ta sauko, amma ita tayi nisa ba zata iya kama hannunta ba bare ta sauko, kallonta tayi tace "Bari na duba a waje na samo wani ya taimaka miki."

Fita tayi inda Hamna ta gumtse baki a zuciyarta tana fad'in "Azzalumi mai bak'ar zuciya mugu."

Jim kad'an sai ga Amna tare da Jibril da Iya sun shigo, tunda ya ganta saman bishiya ya kece da dariya, saida ya ci mai isarsa kafin yace "Ke kuma me kika mishi haka daya d'oraki kan bishiya?"

Shiru ta masa sai kumbura take kafin ya taka da k'yar ya kamo hannunta, saida ya sauko sannan ya k'ara kamata ta k'arasa dirowa, duk gidan babu wanda bai ji abinda ya faru ba, wasu sunyi dariya sosai inda su Ummy kuma suka yi ta masifa da fad'a.

*Ci gaba*

Zuwa *09:30* na dare ya kammala da majinyatanshi, ban d'akin dake cikin ofishin ya shiga ya fito, wata coffre ya bud'a ya fito da wasu kaya, wandon jikinshi ya fara cirewa ya sauya da wannan sannan ya zauna ya d'aura wannan guma'gumen takalman bak'ak'e, cire riga yayi ya saka wannan ya b'alla botiran ya d'an rage ma hayyanen tsayi ta hanyar nad'esu sannan ya soka rigar cikin wandon, d'amara ya d'aura sosai ya zarge kafin ya d'auki bindiga a cikin gidanta ya mak'alata a wandon, saida ya b'alle buton ya fito da ita ya kalla yayi murmushi ya mayar ya rufe, turare ya d'auka ya fesa sannan ya fito ya rufe ofishin ya d'auko hanyar gida, bai zame ko ina ba sai kwatancen da Zeituna ta masa na gidansu, fitowa yayi a cikin mota ya samu wani ya tambaye shi gidan aka nuna mishi, sallama yayi kawu ya amsa ya fito, yana zuwa ko da suka had'a ido ya d'an dafe cikinshi sakamakon juyawa da yayi, *soja?* Soja a gabanshi? Me yayi zafi haka? Idonshi take suka raina fata jikinshi ya fara rawa, cikin rawar murya yace "Aaaa...bbbb...barka rank...a shi dad'e."

Sake zaro mishi ido yayi bai amsa ba sai muzurai yake, k'ara tsorata yayi ya d'an sunkuya kamar zaiyi ruku'i yace "Ranka shi dad'e lafiya? Allah yasa dai ba lafiya nayi ba."

Mota ce ta zo wucewa ta haskasu
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment