Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

naga zaki fita k'asa?"

Cikin damuwa tace "Saida na gama shiri zan fita kuma sai Ayuba yake fad'a min motar na wurin gyara, kawai zan hau taxi ne."

Girgiza kai yayi yace "Haba uwata, idan ma baki kira Abbanmu ya zo ya kaiki ba, to mu miye anfaninmu? Muje na sauke ki kawai dama bacci na zo yi."

Murmushi tayi tace "Nagode." Zagayawa tayi ta sauke goyon ta bud'a ta shiga, suna tafe suna d'an tab'a hira tana nuna mishi gidan har ya sauke ta, juyawa yayi ya koma ita ta shige ciki. Hanyarshi ta dawowa ne ya hangi Amie kan moto, duniyanci sai abinda ya ci gaba bawai ya rage ba, tsayar da ita yayi suka tsallaka titi suka tsaya, kallon juna sukayi sosai har yau yana tuna Ummy ta fad'a mishi wai Amie ce ta fad'awa marigayiya Shureim d'ansa ne, saida ya fito daga motar ya tsaya gabanta tana fad'in "Mai kyau ya kake? Kwana biyu?"

Kallon fuskarta yake da tasha kujera kamar an watsa takin gona yace "Da dama? Ya harkokin?"

"Da dama." Ita ma ta fad'a tana d'an sakin kan moton, ba tare daya daina kallonta ba yace "Me ya had'aki da k'awarki?"

Kallonshi tayi ita ma tace "Wace k'awar tawa?"

"Matata mana, kankana."

Wani kallon rashin mutumci ta masa tace "Ba komai, me ka gani?"

Murmushi yayi yace "Ko yaron yasan da komai, yaushe rabon dana ganku tare? Sannan har akayi bikinta aka gama ban ganki ba."

Cikin rashin damuwa tace "Hakane, kasan duniya juyi juyi ce, k'awance ma yana da tsuntsun soyayya, yau ya hau kanka gobe ya tashi ya koma kan wata."

Murmushi ya sake yi yace "Hakane, amma haka yafi faruwa kan k'awancen da ba'a gina dan Allah ba."

Tab'e baki tayi tace "Ok, ni zan tafi dan ina da abunyi sosai a gabana."

Wani kallo ya mata yace "Ba damuwa, amma idan kin samu dama kije ki ci abincin amaryata."

Saida ta kashe masa ido tace "Zan zo, amma ka fara saka min lambarka ta yanda zan sanar da kai zuwan nawa idan na tashi zuwa."

Ta k'arashe da mik'o masa wayarta, saida ya kalleta kallo na fahimta sannan ya karb'i wayar, saka mata lambar yayi ya mik'a mata, karb'a tayi tana tana kallon lambar tace "Kai babba ne, lambarka sauk'in hardacewa gareta kamar shan ruwa."

Murmushi ya mata yace "Amma ai kinsan ruwa kala kala ne ko, sannan idan ka shanye ruwanka a duniya ko a cikin tekun maliya kake ba zaka iya had'a ko d'igo d'aya ba."

Ko da ya fad'a ya wuce abinshi ya barta nan, kai tsaye gidan ya koma ya nufi b'angaren amaryarshi, amma daya shiga k'ofar rufe bai same ta ba, kuma gashi ba zai iya baccin ba idan bata kusa dashi, a hankali ya fito ya nufi b'angarensu Ummy.

*Da* sallama a bakinshi ya shiga wanda yayi daidai da fitowar Hamna daga madafa da plate a hannunta da Ummy da Soueiba bayanta da alama aiki suka gama, tana ganinshi ita tasan meya kawoshi gida wannan lokacin, da sauri ta ratsa tsakanin Ummy da Soueiba zata koma madafa ta b'uya, da sauri yace "Algunguma na ganki, maza zo wuce mu tafi to."

Juyowa tayi tana turo baki tace "Ba zan je ba ka tafiyarka."

Nuna kanshi yayi da yatsa yace "Ni ne kike fad'a ma ba zaki zo ba? Ni kankana?"

Lab'ewa tayi bayan Ummy ta rik'eta da hannun d'ayan tana lek'enshi, tunkarowa ya fara yi yana fad'in "Zaki san wa kika fad'awa ba zaki zo ba kankana, ba dai ni ne kika ce ma ba zaki zo ba? Ni ga sakarai ko?"

Sake rirrik'e Ummy tayi tana ihu tana fad'in "Ummy ki ce masa ya tafiyarsa, dukana zaiyi."

A hankali Ummy tace "Hamna, ke dai kinsan halin kayanki, dan Allah rufa masa asiri ki jashi ku tafi, ke kinsan yanda zaki bashi hak'uri."

Kamar zatayi kuka tace "Ummy ni ba zan je gaskiya na gaji."

Rik'e baki Soueiba tayi tana kallonta Ummy ma kallonta tayi, takowa yayi da sauri hakan yasa ta dakawa da gudu madafar ta shige, kafin ta mayar da k'ofar ta rufe ya shige ciki, kallon juna sukayi inda Ummy ta girgiza kai tace "Muje Soueiba, ta fito da kuka yanzun, anjima kuma sun shigo nan suna dariya."

Dariya Soueiba tayi ta juya zata wuce d'akinta, ihunta sukaji yasa duk suka juya dan ganin me ye? Abun mamaki ganinshi sukayi ya mata dokin wuya ya d'aukota, wutsil wutsil ta shiga yi da k'afafu tana ihu da kwaroroton kiran Ummy tasa ya sauke ta, Ummy ita dariya ma ta shiga yi har da rik'e ciki, ita kam da take ganin kamar zata fad'o ihun ta ci gaba da yi iya k'arfinta, mai gadi da yaji kuwar saida ya d'an lek'o, ko da ya ga soyayya ce saiya koma yayi gum, daya shiga b'angarensu ma saida su Jamila da Farisa suka lek'o, Umaimah ko ko a jikinta dan ba sabon abu bane, tunda akayi aurensu abinda ke faruwa kenan, wani abun ya baka takaici wani ya baka haushi, wani kuma saiya baka dariya har cikinka ya k'ulle, wani kuma in sukayi shi sai su matuk'ar birgeka ka gane cewa akwai fahimta sosai a tsakaninsu, kowa yasan kowa babu mai bawa wani wahala.

Sai kan gado ya direta yana b'alle mab'allan rigarshi yana fad'in "Hamna ba ni ne na ce ki zo kika ce k'in ki ba? Zaki ga ikon Allah yau wallahi sai kin haifi yan uku ko na barki."

Cikin kuka tace "Kayi na ce to ba zan sake ba, Allah na maka alk'awari."

Dungurar mata kai yayi yace "Ke tafi can alk'awarinki na banza, kullum ba haka kike ba."

Kallonshi tayi idonshi sunyi launin ja alamar fitina, gashi ta jawa kanta zai murk'esheta da rana patsal patsal, in tayi wasa yau ma sai an mata sabon d'inki, dan yanzu indai ta mishi iskanci to tana nan yake horonta, dan ta samu lafiyarshi sai kawai ta tashi zaune ta shiga cire d'amararshi, yana kallonta ya ga me zatayi sai gani yayi ta fito da...bata tsaya komai ta ba mata masauki a bakinta.

Da sauri ya rintse ido ya k'amk'ameta tare da danna kanta yana sauke wani wahalallen numfashi...๐Ÿ˜Ž

*Bayan awa biyu* kanshi na kwance tsakanin mamanta biyu, shafa kanshi take a hankali idonta rufe tana ji kamar ita ma tayi k'undubala tace tana son shi, yanda hannunshi ke mammatsa mazaunanta yasa take ta sauke numfashi, dukansu babu mai magana sunyi shiru suna jin dad'in yanayin, wayarshi ce tayi k'ara dake kusa da Hamna kan gadon a cikin aljihunshi, ba tare daya d'ago ba yace "Duba kiga."

Hannu tasa ta fito da ita ta duba tace "Babu suna."

Hannu ya zura ya karb'a ya danna ya sata a speaker ya d'ora wayar kan cikinta yana saurare, cikin wata irin muryar bariki ta d'aukar hankali aka ce "Hello mai kyau."

Ba tare da damuwa ko tunanin komai ba a kasalance ya amsa da "Ya kike? Har kin shirya zuwa ne?"

A hankali ta amsa da "Eh, zan zo anjima, me zaka tanadar min?"

"Me kike?" Ya fad'a idonshi rufe, cikin kashe murya tace "Kai, kai kad'ai ma ka ishe ni."

Ido rufe yace "Na miki yawa, ki dai canza wani abun."

Saida ta sake kashe murya tace "Ni kai d'in kawai nake so, in kuma ba zan samu ba nayi zamana."

Yana shirin cewa eh tayi zamanta kawai yaji Hamna ta mishi wata hankad'ar tsiya wacce baisan da zatayi hakan ba ya fad'i k'asa kwance, tashi tayi da k'arfi tare da rik'e wayar a hannunta, saida ta sauka daga kan gadon ta d'aga wayar iya k'arfinta ta b'arsata k'asa, fashewa tayi inda ta kalleshi rai a b'ace cikin fitar hayyaci tace "Ni zaka raina Ammar? Me ka d'auke ni nima? Karuwar kamar ta? To baka isa ba wallahi, banyi wannan lalacewar ba."

Da sauri ta bud'a kayanta ta zago doguwar riga ta zura ta d'auki hijabi ta saka, ta juyo zata fita ta ganshi yana mayar da kayanshi shima, saida ta harare shi sama da k'asa taja tsaki tace "Na bar maka gidanka ka d'auko duk wacce kake so ku zauna tare."

Da sauri ta fita inda ya bita da gudu yana kiran "Hamna, Hamna tsaya ki saurare ni, Hamna dake nake magana."

Juyowa tayi a hassale tace "Je veux te tuรฉ."

Wucewa tayi ta bar d'akin sai b'angarensu Ummy, kai tsaye d'akin Ummy ta shige ta same ta zaune ta idar da sallah la'asar, fad'awa tayi kan k'afafunta ta fashe da kuka, Ummy da gabanta ya shiga fad'uwa da sauri ta aje carbin hannunta tace "Hamna lafiya? Me ya faru kike kuka? Dukanki yayi?"

D'agowa tayi abun tausayi tace "Ummy ba gwara ma ace dukana ne yayi ba da abinda ya min, da dukana Ummy ko ji ba zakiyi bare har na zo na d'aga miki hankali."

"To meya faru?" Ummy ta fad'a hankalinta a tashe, cikin kukan tace "Ummy yah Ammar baya k'aunata baya so na ko kad'an, Ummy a gabana yake hira da K'awata yar iskan nan Amie, wallahi Ummy ita ce na gane muryarta kuma ita kad'ai ke kiranshi da mai kyau, Ummy yah Ammar ya gama dani a rayuwa."

Ajiyar zuciya Ummy ta sauke, sai yanzu ta fahimci al'amarin wato na kishi ne, d'an jinjina kai tayi ta juyo da fuskarta suna kallon juna cikin nutsuwa tace "Me ye tsakaninshi da Amien?"

Cikin hushi tace "To ni ina na sani, kawai suna son tozartani ne, Ummy yarinyar fa yar iska ce wallahi ta sawa a gaba, baki ga nima na daina kulata ba saboda ba mutuniyar kirki bace."

Kallon fahimta ta mata tace "To yanzu yana ina shi?"

Saida ta turo baki tace "Yana can na baro mishi gidanshi."

Zaro ido Ummy tayi tace "Kin baro masa gidansa? Hamna me kike nufi?"

Saida tayi k'asa da kanta tace "Ni ba zan koma ba."

Lallai ta yarda tana son Hamna fiye da yanda take son 'ya'yan data haifa a cikinta, musamman da yar uwarta ma ta mutu saita k'ara ninka soyayyar, amma a yanzu da ake magana kan gidan aurenta, dokenta ta nusar da ita ta kuma nuna mata ita uwa ce, wannan karan ba zata goyi bayanta ba kamar yanda take yi kullum, dan haka ta kalleta tace "Kenan ki ce yaji ne kikayi?"

Cikin zumud'i tace "Eh Ummy."

Wata tsawa Ummy ta mata da bata tab'a mata ko kamar ta ba tace "Dallah malama tashi anan."

Saida ta zabura ta kalli Ummy da mamaki, mik'ewa tayi jiki na rawa tana kallon Ummyn da ita ma take tashi tsaye, kallonta tayi ita ma tace "Kina nufin yaji ne kika min nan? Hamna mahaukaciyar ina ce ke? Auren naki duka yau kwana ashirin da uku ki ce min wai yaji kikayi? To maza wuce koma gidanki."

Hannu tasa ta shiga murza ido tana kuka tace "Ummy yanzu ko kiranshi ba zakayi ki tambaye shi me ye tsakaninshi da ita ba? Ni wallahi ba zan iya zama dashi ba indai yana tare da wannan tsinanniyar, haka kawai yaje ya jawo min jarfa."

Ita kam dariya ma ta so bata amma saita gimtse fuska, inta fahimta ita ma kamar ta fara son shi kenan, sai dai kuma tana da gaskiya tunda tafi kowa sanin wacece k'awarta ta, dan haka tace "Zo nan."

Saida ta tsaya gabanta tana ta share ido ko hawayen babu Ummy tace "Zan kira shi naji me ya faru, amma idan ya fiki gaskiya Hamna dole zaki koma d'akinki, ba zan yarda kullum ana cewa ni ke d'aure miki gindi kina abinda kika ga dama ba, kin yarda?"

Turo baki tayi tace "Na yarda."

Jinjina kai tayi tace "Shikenan to, mik'o min wayata."

Kan gadon ta nufa inda ta nuna mata ta d'auko wayar ta bata, ban d'aki ta shiga dan tsarkake kanta ta samu tayi sallah. Bata kai ga danna kiran ba ya shigo d'akin kamar wani ne ya turo shi daga baya, d'aga kai tayi tana kallonshi kallo na fahimta, duk a hargitse yake hatta kayan jikinshi ma.

Shi kanshi tunda tace wai na bar maka gidanka tasa yaji kamar ta soka mishi mashi, kai shi fa wallahi tallahi idan ta sake maganar zata rabu dashi saiya zaro harshenta ya datsashi biyu, ta yanda gobe ba zata sake fad'in haka ba, yo inba ta raina shi ba kan wata yar iska da bata san ma akan me ake magana ba zata fad'a masa hakanen, da marinshi tayi duk da yafi mishi sauk'i kan tahowarta, yanzun haka ya zo ne da niyyar indai zata koma tare dashi to zai durk'usa har gabanta ma ya bata hak'uri, abune da bai tab'a jin ko tsammanin zai ji shi akan wata hallita ba, zuciyarshi ma saida yaji wani zazzab'i ya kamata.

Da sauri ya matso kusan Ummy da nufin tambayarta ina take? Rik'e hannayenta yayi zaiyi magana Hamna ta fito da towel d'in Ummy d'aure da kuma d'an k'arami ta d'aure kanta dashi, tana ganin ta juya zata koma da wani saurin bala'i yasha gabanta, kallonshi tayi fuskarta a had'e shi ma kuma haka.

Saida ya furzar da iska ya saisaita numfashin shi dake jin kamar zai bar gangar jikinshi kafin yace "...


*Alhamdulillah*
04/11/2020 ร  14:39 - Ummulkhairi: ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ
*BADAK'ALA*
๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ

*Labarin Gaske*

*NA*

_SAMIRA HAROUNA_

*Litattafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._

*SADAUKARWA GA*

๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ _*AHALI NA*_๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

๐Ÿ’ซโœจ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*๐ŸŒŸ
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_๐Ÿค

โ˜† *[ T.M.N.A]* โ˜† ๐Ÿ“–๐Ÿ–Š๏ธ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_

_74_


"Uban waye yace ki fasa min waya?"

Wani kallon mamaki ta mishi, wayar shi ma yake magana akai? Sake had'e fuska tayi tace "An fasa d'in, me zakayi?"

Rik'e k'ugu yayi yace "Biya na zakiyi ko kuma jikinki ya fad'a miki."

Tab'e baki tayi ta rab'ashi zata wuce ya sake tare ta yace "Sai fa kin biya ni yarinya."

A hassale tace "Kai kasan ni ba matsiyaciya bace, amma ba zan biyaka ba dan kaji dad'in kiran wasu yan iska kana hira dasu."

Da wani mamaki a fuskarshi yace "Iyeee Hamna, ni ne d'an iskan ko yan matan?"

Sama da k'asa ta harare shi ta juyo ta tsaya gaban gadon Ummy, bayanta ya tsaya yace "Allah sai kin biya ni kud'in wayata, na yafe miki sauran ma ki ban d'ari biyu, sauran babanki zai cika min."

Juyowa tayi tace "Saboda shine ya fasa wayar? To ko ni dana fasa ba zan biya ba."

Gashinta dake jik'e da ruwa ya fizgo da k'arfi ya matso da ita kusanshi, k'ara ta saki sanda ya rik'e gashin nata, rik'e hannunshi tayi tana kallon fuskarshi da ido jawur tana shirin yin kuka tace "Sake ni Ammar."

Jinjiga kan yayi yace "Waye Ammar d'in?"

Da k'arfinta tace "Kai, kai ne Ammar, Ammar Ammar Ammar! Na fad'a sunanka ne ai."

Sakin gashinta yayi ya jawo k'ugunta ya had'e da na shi yana mata wani kallo mai ma'anoni yace "Naji zan yafe miki kud'in, amma sai munje b'angarenmu."

Hannu biyu tasa ta ture shi tace "Da wa? Ni? Har abada Ammar, wallahi sai ka..."

Leb'enta na k'asa yayi saurin cab'owa da yatsunshi biyu cikin tsananin tashin hankali yace "Karki yarda bakinki ya sake fad'in ba zaki koma gida na ba, tawa ce ke har abada, kin gane?"

Idonshi ta kalla tana sako da hawaye masu zafi tana fad'in "In dai har kana kula irinsu Amie, to ba gidanka ba kad'ai har da tsanarka saina koyawa kaina, zan tsaneka Ammar tsana ta har abada."

Da sauri ya saketa yana sunkuyar da kanshi, hannu d'aya yasa yana murza fuskarshi yana sauke huci mai zafin gaske, kallonta yayi kallo na basira yace "Babu komai tsakani na da ita Hamna, yau na had'u da ita kuma a yau na bata lambata, amma sam ba abinda kike tunani bane."

Da k'arfi ta tureshi baya tana fad'in "To miye inba haka ba? Akan me zaka bata lambarka? Me take da shi a jiki dani bana da shi?"

Da sauri ya rik'e hannayenta yace "Babu Hamna, bata da komai da yake birge ni ma, ke kad'ai ce ke birge ni a yanzu, bayan ke wallahi babu kowa a gabana."

"Amm.." Da sauri Ummy dake tsaye ta zuba tagumi tana kallonsu, kanta har ya fara ciwo saboda cacar bakin nan (ni ma yanzu haka nawa kan ciwo yake Ummy, tunanin yaranki kad'ai nasa gabana ya fad'i), mamakin yanda suka manta da ita a d'akin suke ta maganarsu ma take, wani na fad'a wani ke d'auka shi ma ya fad'a, ita sun hanata damar fad'an wani abu ma, nuna musu k'asan gadon tayi tace "Ku zauna."

Kallon Hamna yayi saida ta zauna k'asan tana rufe kafad'unta da k'aramin towel d'in kafin shi ma ya zauna yana ta kallon fuskarta, kan gadon Ummy ta zauna ta kalle shi a nutse tace "Me ya had'aka da k'awarta har ka bata lambarka?"

Zunbur ya sake gyara zama kamar mai zaman tahiya yana fad'in "Ummy yarinyar nan bata da hankali karki saurare ta, na kai uwa Zeituna wajen bikin Jumare, na dawo shine na ganta na tsaya muka gaisa..."

Duk abinda ya faru ya fad'awa Ummy kafin ya kalli Hamna yace "Shine dan ubanta ta fasa min wayata sabuwa, Allah sai kin biyani ko kuma na siyar da motarki."

Nuna shi tayi da yatsa tace "Kar sake zagar min uba malam, ya isheka haka fa."

Dafe k'irji yayi da hannu ya zaro ido yace "Lah na shiga uku, Hamna ni kike nunawa da yatsa? Mijinki ne ni fa."

Hararanshi tayi tace "Ka sake zagina ma sai kaji tafi a fuskarka Allah."

Ummy ya kalla yace "Shikenan Ummy 'yarki wuta zata shiga."

Cikin juya baki tace "Sai ka kaini ai tunda kai ke da wutar."

Kallonshi Ummy tayi, wai fa so yake ta koma a hakan har ya fara jigata shi, amma dai nuna tsananin damuwar da kuma lallab'ata shine baisan ya zaiyi ba, har da zagi yake had'awa, to a hakan zata koma ko me yake nufi? Had'e fuska tayi ita ma tace "Taje ta fasa wayar, to bari kaji ba ita ba ko ni naga ubanka na waya da wata Allah bayan na fasa wayar ma saina fasa mishi kai, ai kai ta maka mai sauk'i ma, malam fitar min a d'aki."

Galala ya kalli Ummy, me take nufi? Ganin baiyi niyar mik'ewa ba yasa Ummy kallon Hamna tace "Yar albarka tashi canza kayanki, zanje da kaina na d'auko miki kayanki adadin da kike buk'ata."

Wata dariya ya shek'e da ita yana mik'ewa tsaye yace "Eh lallai Ummy ba zaki iya zama alk'aliya ba, kuma da nasan wariyar da zaki min kenan da ban kai uwata wajen bikin nan ba har sai an gama wannan yak'in."

Mik'ewa tayi ita ma ta ja rigarshi tana fad'in "Muje waje a barta ta huta, saina bata maganin ciwon kai tasha saboda damuwar nan daka saka mata."

Juyowa yayi ya kalleta yace "Ke yanzu zaki iya zama babu ni a kusa dake? Kinfa san abinda nake baki kina ci cikin dare."

Ita kanta Hamna saida ta dara tace "Bana so, ka ci kayanka kai kad'ai."

Tsaye yayi ya rik'e k'ugu yace "Ummy kin kassara min zuciyata wallahi, zan fita yanzu amma ba zan sake dawowa nemanta ba, amma Ummy ki tabbatar kin ware mata gadonta, dan zan dinga kawo mata ziyara."

Kallonshi tayi tace "To bismillah kaga yanda zanyi da kai."

Saida ya kai k'ofa ya juyo ya kalleta yace "An dake ni kuma an hanani kuma, ke dai baki da imani wallahi ko kad'an."

Ummy ce tace "Zama da kai ne yasa ta rasa nata ita ma."

Ko da ya shigo da dare da sabuwar waya ya saka layikan nashi a ciki, yana zaune yana duba sak'onnin dake shigo mishi ta WhatsApp yaga bak'uwar lamba ta turo mishi hotuna, shiga yayi dan ganin wanene, tashin hankali sanda ya bud'a hotunan, Amie ta turo mishi hotunan ta tsirara, wanda ke da kayan ma kamar ba'a saka ba na d'aukar hankali ne, da sauri ya lik'e idonshi yana fad'in "Ya salam."

Bud'ewa yayi ya shiga ya goge su duka tare da bloquรฉn d'in lambar, kiran lambar yayi ko da ta gani ta d'auka jiki na rawa, na yan Maradi ya mata ta hanyar cewa "Ke dan mai... me kike nufi da ni? Na miki kama da d'an iska irinki? To saurare ni da kyau kiji."

Saida ya gyara zama yace "In kika k'ara kula ni ma ko a hanya wallahi daga ubanki har kakanki na ashirin sai sun zubar da hawaye, in kika k'ara tuna ko sunan matata ma sai yan uwanki sunyi nadamar kasancewarsu yan uwanki, In kuma kika sake aiko min hoton rub'abb'ar fuskar nan taki mai kama da gurb'ataccen tumatir Allah saina watsa miki asid kin k'arasa dahuwa, shegiya b'abb'akar banza ke ba kyau ba ba kyan jiki ba har ki tsaya kina bariki, to ki kiyaye ni kafin ki fara nadamar sani na da kikayi, yanzu ma wallahi na raga miki ne dan ni dan ni fad'a da mace ba aikina bane, amma da namiji ce ke da tuni na nemi inda kike na cire miki k'ashin baya, 'yar banza mai kama da agwaluma."

*Kuyi hak'uri da jaruminku, bakin ya saba da...*

Amie da tunda ya fara magana tayi shiru take saurarenshi, saida taji ya kashe wayar ta bi wayar da kallo, ya ci mutumcinta sosai fa ta yanda ba zata iya mantawa ba, amma ya zatayi daya wuce tayi wuri ta aje shi, dan tasha jin labarinshi wurin Hamna tun kafin su b'ata, tasan in tace ma tayi dashi ita ce a kasa da cizon yatsa.

Ko da ya gama fad'a shima ya aje wayar ya mik'e ya shiga wanka, daya fito shiryawa yayi cikin kayan bacci ya fesa turare ya fice wajen matarshi. Da sallama ya shiga ya same su duk zaune a falon, kusan Hajia ya zauna yana kallon Nazifa dake kusa da Hamna suna kallon waya yace "Ke tashi samo min abinci."

Mik'ewa tayi a ladabce ta shiga madafa, kallon Hajia yayi yace "Hajia jikar nan taki bata san meye miji ba, kiga fa babu ruwanta da na ci abinci ko ban ci ba, ita dai data samu ta cika tunbi shikenan ni na mutu dan yunwa."

Ko kallonshi ba bare ta tanka masa, haka ma Hajia bakinta taja tayi gum, jin babu wanda ya kula shi yasa yace "Hajia yau wace rana?"

Kallonshi tayi tace "Yau talata."

"To juma'a insha Allahu zamu koma sabon gidanmu."

Duk yayi maganar ne yana kallon Hamna, duk da bata kalleshi ba shiru tayi daga danna wayarta, sanda tayi k'ok'arin kallonshi kuma saita lura da wajenta yake kallo, dan haka bata yarda ta kalleshi ba, Ummy ma kallonshi tayi ba tace komai ba sai Hajia da tace "Ammar da gaske kake?"

A lokacin Nazifa ta fito ta sunkuya ta mik'o mishi abincin, saida ya karb'a ya fara ci yace"Allah kuwa Hajiata, tafiya zanyi daga nan mu barku ku sarara kuma."

Cike da rashin jin dad'i tace "Ammar bana so ku bar nan wallahi, in na bari kuka tafi kamar ban cika burin marigayi ba na son zama a waje d'aya, kuma kaga yanzu kana tashi daga nan sauran ma zasu ce zasu tashi."

Gyara zama yayi yana kallonta yace "Hajia kiyi hak'uri dan Allah ku ba kowa dama ya d'an matsa, ni na miki alk'awari zumuncinmu ba zai lalace ba sanadiyar tashinmu, na kuma miki alk'awarin ko da na tashi daga nan kullum zan dinga zuwa kowace safiya ina gaishe ki, haka ma kafin na kwanta saina tabbatar da na zo kin ganni na ganki sannan."

D'an lab'e baki tayi tace "Shikenan, Allah yasa alkairi."

Su Ameer ya kalla dake kewaye da Husseina tana musu tatsuniya ya kalla yace "Heyy, duk wani wanda yasan mallaki na ne shi ya had'a kwomantsanshi, dan babu wanda zan bari."

Murmushi ta saki daga nan zaune dan ta fahimci ina zancen ina ya nufa, har ya gama cin abinci suna ta hira dasu Husseina da Hajia, bayin Allah dariya har rik'e ciki sukeyi, sun daddage sai biye mishi suke yi kam, idan ya fad'i wani abu ita kanta Hamna da Ummy sai sun murmusa ko har ma su dara, amma duk da haka bata kalleshi ba bare ta mishi magana. Saida dare yayi sosai kowa yayi haramar nufa inda zai kwantar da hak'ark'arinshi, ta mik'e ta nufi d'akinta na yan mata wanda Nazifa ce a ciki yanzu da Huda shima ya bi bayanta, tsayawa
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment