Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

shin me zaka ce a game da hakan?"

Saida yayi murmushi yasa babbar yatsarshi a baki sannan yace "Idan shi wannan mahaukaci ne ai ku da hankalinku, a ina kayan suke? Wurin wa ya gani?"

Kallonshi Jano yayi yace "K'arya zan maka, kai kasan baka isa ba wallahi."

Da k'arfi ya taso daga kwanciyar da yayi kan kujera ya nuna inpecteur d'in yace "Yallab'ai da kai nake magana, ka fad'a mishi karya sake saka min bakinshi, inba haka zan zubar mishi da hak'ora kuma a gabanka wallahi."

Kallon Jano inspecteur d'in yayi da ido ya mishi alamar yayi shiru sannan ya kalli Ammar yace "Malam Ammar, ya fad'a mana ba kawai kakin ne jikinka ba har da bindiga, rik'e bindiga baga jami'in tsaro ko kuma wanda ke son kare kanshi ba shi ma saida lasisi babban barazana ce a cikin al'umma, taka doka ne da idan aka kama mutum za'a hukuntashi, amma idan kana da lasisi da takardar izinin rik'eta saika nuna mana hujja, idan babu zamu iya mik'a al'amarin gurin su sojawan sai suji da kai."

Saida ya d'an buga teburin gabansu yace "Da kyau, haka nake so ai dama, so nake muje wurin manyanku ta yanda za'a bi min hakk'ina na k'azafin daya min, yace wai ina saka kayan soja, to ni mahaukaci ne ko me? Dan ina son zama soja bashi ke nuna zan uya anfani da kayan ba na firgita mutane, dan haka idan har aka tabbatar k'arya ya min ni kuma zan shigar da k'ararshi na cewa da yayi na saka."

Kallonshi inspecteur d'in keyi da mamaki, bala'i da d'umu d'uminshi, Kai ba zan iya ba wannan har ni yasa cikin rigimar, dan haka yace "To shikenan munji, yanzu akan dukan daka mishi a baki har ya fito da jini, anci tararka ta 15 000."

Wata harara ya dalla ma Jano yace "Matsiyaci, ai da bara ka koma."

Kallon insp. d'in yayi yace "Yallab'ai, gaskiya bana da kud'i, kawai muje mataki na gaba."

๐Ÿ˜‚ _Sis a haka kike son shi ko?_

Wani kallo Jano ya mishi ya d'an saci kallon wandonshi daya kama shi sosai har ana ganin shatin wayarshi da alamun kud'i, amma wai baya da kud'i. D'aure fuska insp. yayi yace "Malam Ammar, muna son sulhunta matsalar nan ne ta yanda ran kowa ba zai b'ace ba, ka biya wannan kud'in ku bawa juna hak'uri tare da alk'awarin kiyaye gaba, shikenan kowa ya tafiyarshi."

Zaman farko ya sake yi ba alamar wasa yace "Da gaske na ke fad'a maka banda kud'i, meya kamata nayi?"

"Sai mu rufe ka, idan aka zo belinka sai a biya tarar." Ya fad'a ba alamar wargi, murmushi ya masa yace "Bismillah to, ina so dama na shiga ciki na kwana ko d'aya ne, dan bana so har zamani na ya k'are a tarihi na ace ban shiga gidan maza ba."

Insp. d'in ne yace "To ai idan kana son shiga gidan mazan na k'warai sai kayi babban laifin da zaka shiga hannun mazan."

Kallonshi yayi yana murmushi yace "Indai nine ai zan aikata wata rana, zaka gani a jarida ma."

Wurga ido yayi irin kai ta shafa kafin ya kira wani cop yace ya shiga da shi ciki, saida aka karb'e komai na shi kafin ya iza k'eyarshi gaba, saida ya juyo ya kalli Jano yace "Tsinanne kawai, ai zan fito ne karka bari mu had'u da kai, sakarai mata-maza."

Juyawa yayi ya kalli insp. yace "Kar a kashe min waya ta saboda masoya na zasu iya kira na a kowane lokaci."

Har ya bud'e baki zai mishi magana sai kuma ya zura kai ya tafiyarshi dole ya k'yale shi, yau kam shi ya ga tijaja, shi in ba masu shan k'waya ba bai tab'a had'uwa da irin wannan mutanen ba, kallon Jano yayi ya bashi hak'uri tare da cewa idan anyi belinshi zasu nemeshi dan a musu tsakani, godiya ya mishi ya tafi shi kanshi zuciyarshi ta cika fal da tsoron sake had'uwa dashi d'in, dan yana da tabbacin Ammar da d'an ta'adda ne to ba zaiji wuyar yin k'unar bak'in wake ba, dan shi wani lokacin tsabar bala'i kawai a mutu ko ayi rai ne, ya kashe ko a kashe shi.

Ko da aka shigar dashi aka rufe akwai mutane a ciki, wani saurayin mashayi ne ya matso kusanshi yana mishi kallon raini da wani d'aukar kai, a hankali saiya zauna kusanshi irin yana neman masifar nan (kunsan dai a gidan yari kowa yana so yaga ya cuci na k'asa dashi, kuma kowa yana ma kowa kallon k'aramin d'an iska ne), har yanzu bai daina mishi wannan kallon kad'an nake jira ba, Ammar dake zaune kan bancin ya dafe hannayenshi a gwiwanshi yana ta bubbuga k'afa, Jano Jano Jano Jano, sunan da yake ta fad'a kenan ko tsagaitawa babu, jin wannan saurayin na matse mishi wuri yasa shi d'an kallonshi, ganin wannan kallon rashin mutumcin da yake masa irin shi wai shak'iyi ne yasa shi yin murmushin gefen labb'a ya jinjina kai, saida ya sake kallonshi da kyau yace "Meya shigo da kai nan?"

Cike da gadara yace "K'waya, ni mai siyar da k'waya ne."

Ba tare daya daina kallonshi ba yace "Wa ka tab'a kashewa a harkar taka?"

A d'an tsorace ya kalleshi yace "Kisa kuma? Ban tab'a ba."

Jinjina kai yayi yana d'auke idonshi daga kanshi yace "To karka shiga harkata, inba haka ba a filin wurin nan zan rataye ka."

K'wafa yayi tare da mayar da kallonshi gabanshi, matsawa nesa dashi yayi yana kallonshi yace "Kai ka tab'a kashe mutum ne?"

"Sosai ma." Ya fad'a ba tare daya kalleshi ba, da mamakinshi yace "Wa ka tab'a kashewa? Kuma meye sana'arka?"

A hassale ya kalleshi yace "Kai, kai zan fara kashewa yanzu idan ka sake min magana, shege kai jarababbe." Saida ya zabura saboda d'aga muryar da yayi, tashi yayi daga wurin gaba d'aya yana kallonshi.


A tare suka shiga yau dan gaishe da iyayensu, sai dai yau babu Hajia zaune a kujerar mulki, kai tsaye d'akin mahaifiyarshi suka nufa da sallama, daga ciki ta amsa tare da musu izinin shiga, suna danna kai cikin d'akin ko da ta gansu tare da Huda saita b'ata rai tana musu wani kallo, durk'usawa sukayi dukansu suna gaishe ta, a wani basarwa ta amsa kafin ta kalli Huda data sha shirinta tsaf tace "Yaushe kika zo? Da safen nan?"

Junaid ne yace "A'a Mama, tun jiya ta zo ai, yarinyar bata da hayaniya ne shiyasa baki san ta zo ba."

Cike da dakiya tace "Uhum! Ta zo ta kwana biyu ne kenan?"

Kallon kallo sukayi sai Maryama ce tace "A'a Mama, na sa a kawo min ita ne ta zauna tare dani."

"Ban gane ba? Kina so ki ce zata zauna a gidan nan din-din-din?"

Saida ta kalleta dan son gano yanayinta tace "Eh."

Fuska a d'aure tace "To naji, ki bamu wuri zanyi magana da d'ana."

Murmushi Maryama tayi ta mik'e rik'e da hannun Huda suka fita, suna bada baya ta balbale shi da masifa akan me zai yarda ta zo da yarta, ai ba haka akayi da ita ba, a k'arshe ma cewa tayi "Wai kai baka da zuciya ne? Matarka ta zo da 'yar da ba kai ka haifeta ba a gidanka, me zai hana ta kaita wajen dangin ubanta? Ko kuma a cikin karuwan nata bata san waya mata cikin 'yar ba?"

A d'an k'ufule yace "Mama, haba Mama, wannan wace irin magana ce? Ni na amince ta zauna damu, wacece Huda? Duk hidimar da zan mata ba zata kai wacce zan yi wa 'ya'yana ba idan na haifa, kawai ki bar maganar nan bana so."

Mik'ewa tayi tace "To kaji da kyau, wallahi ban yarda da zamanta a gidan nan ba, kuma kasan Hajia ma ba zata yarda ba, dan haka kafin ta muku wankin babban bargo ka gaggauta fitar da ita a gidan nan, idan ba haka ba babu ruwana duk sanda ta zo cin mutumcinka."

"Indai hakane to ni kawai zan koma gida na, dama ban so zama anan ba kawai Alhaji ne yasa na zauna."

Fita yayi daga d'akin ya barta tana bambami, yasan za ayi haka dama shiyasa ya shirya juya, a farfajiyar gidan ya sameta nan ya mata sallama ya fita, gidansu ta koma amma madadin ta shiga wurinta saita wuce b'angaren da bata da masaniya ko na waye, saida ta shiga da sallama a k'ofar d'akin suka ci karo da Amar zai fita, gaisawa sukayi a mutumce ya wuce, saida taga fitarshi saita wuce b'angare na gaba dan ba Umaimah take son gani ba, anan tayi sa'ar samun Jibril ko fita baiyi ba, ganinsu yasa Jamila saka hijabi akan k'ananan kayanta suka gaisa, suna zaune ya fito da alama tashinshi kenan, Huda na ganinshi ta ruga ta rumgume shi tana fad'in "Lahhh Abba, ina kwana."

Rintse ido yayi tare da gumtse baki yace "Shit!" A zahiri kuma bud'a ido yayi ya mata dariya ya rik'e hannunta yace "Yah beby Huda, ya kike? Yaushe kika zo gidanmu? Kin zo wajen mamanki?"

Da fari fad'uwa gabanta yayi jin yarinyar ta kirashi Abba daga ganinshi, amma yanzu tana son sanin dalilin da yasa ta kira shi da haka, kafesu tayi da ido tana kallo, har suka k'araso ya zauna nesa da ita Huda na mishi magana, a kaikaice ya kalleta yace "Madame ya kike?"

Wani shed'anin kallo ne take masa wanda bai dace ba, saida tayi murmushi tace "Lafiya lau Abban Huda, ka tashi lafiya?"

Saida ya d'an rarraba ido yace "Lafiya lau, ina mutumin ko har ya fita?"

"Ya fita." Ta fad'a tana kafeshi da ido, ganin ba zai juri wannan kallon ba yasa shi sakin Huda ya mik'e zai koma ciki, da sauri Maryama tace "Abban Huda nace ko zamu iya magana?"

Yawu ya had'e da k'arfi sannan ya juyo ya kalleta, Jamila ma da baki sake take kallonsu, cikin dai k'warewa ta bariki ta mishi alama da kai da ido cewa su fita waje mana, mik'ewa tayi tana rik'e da hannun Huda ta fita, bayansu ya bi jiki a sab'ule yana kallon yanayin yar matarshi wacce ke jin kamar ta shekara a soyayyar mijinta duk ta fara zufa, suna fita k'ofar d'akin ya tsaya ya rufe yace "Lafiya? Me kikeyi haka Maryama?"

Da yatsa ta nuna shi tace"Dakata malam, dama dan na fad'a maka Huda ta dawo nan da zama ne, ba wai dan mahaifiyarta na aure nan ba, a'a sai dan nan gidan ubanta ne, gidan da ko babu ni a raye nan ne yafi dacewa data rayu, dan haka ka fara shirya nuna mata gata ita ma tasan 'ya ce."

Juyawa tayi zasu wuce sai kuma ta tsaya ta kalleshi tace "Anjima zan bata ta kawo maka takardar haihuwarta, ina buk'atar ka canza mata makaranta ita ma, ya rage naka ka samar mata dreba ko kuma ka kaita da kanka ko ma ta tafi a k'afa duk matsalarka ce."

Wucewa sukayi ta barshi tsaye kamar zai kashe kanshi, wane bala'in ne kuma wannan ke shirin danno mishi kai? A haka ya dawo d'akin Jamila na gyara teburin cin abinci, ta baya ya rumgumeta yana shinshinar wuyanta, ba alamar wasa a amon muryarta tace "Me yasa take kiranka Abban Huda?"

Dakewa yayi duk da fad'uwar da gabanshi yayi yace "Saboda ni da Junaid duk mun ce mata mun zama iyayenta, yarinyar kullum damuwarta ita ce mahaifi, amma yanzu kinga ta daina."

Ba tare daya saketa ba ta juyo ta shafa kumatunshi tace "Je kayi wanka ka fito ka ci abinci."

"To." Kawai yace ya shiga d'akinshi da tunanin k'ananan iskancin da Maryama ta taho mishi dashi kuma, shiryawa yayi ya fito ya sameta suka karya.

Amar na saman hanya lieutenant ya kira shi kan yana so ya tura ma Ammar kud'i ya bashi lambar account d'inshi, dan a ganinshi daya tambayeshi kud'i to baya da su ne shiyasa, ba dan haka ba zai tambaya ba dan rabon da sisin kwabo ta shiga tsakaninsu dashi har ya manta, tun bai fara aikin likita ba ya tsaya da k'afafun, matsala ko wacce ta shafi karatunshi ce shi ke tsaya ma kanshi. Amar dai cewa yayi wallahi baisan komai a game da abinda ya shafi Ammar ba, shi kuma lieutenant yana jin ba zai iya tambayar Ammar d'in ba dan haka yace Amar ya bud'e mishi sabon count a bankinsu, yana zuwa aiki ba b'ata lokaci yayi komai ya ga sai sa hannun Ammar da yake buk'ata, hakanne yasa shi kiranshi dan ya fad'a mishi ya zo, amma mummunan labari sai police ya d'auki wayar ya fad'a mishi abinda ke faruwa, tun saman hanya Amar ke maimaita jikka sha biyar d'in me da Ammar zai yarda a d'aure shi akan ta, da wannan takaicin ya isa ofishin yayi bailinshi.

Ana fitowa dashi ya ga Amar ne sai yaji ba dad'i, tsaye yayi yace "Dama wannan yaron ne ya zo fito dani? To babu inda zanje."

Rai b'ace Amar yace "Ammar kar kayi taurin kai mana, ba wasa na zo yi ba."

"To yi min fad'a ubana." Shiru Amar yayi yana kallonshi, ni yake kamar ya rufe shi da duka, amma yasan ko yayi haka shine zai sha wahala, a kausashe yace "Wuce muje."

"Babu inda zanje, an fad'a maka ni bana da kud'in fitar da kaina ne? Abba nake si ya zo wajen nan, inba haka ba kuma ina nan wallahi."

Juyawa yayi cike da takon isa da k'asaita ya shiga ciki aka rufe shi, harara Amar ya dalla mishi daga nan yace "Kai ka sani ka tabbata anan."

Da kallon zaka gane kurenka ya bishi yace "Zamu had'u ne zaka san ka harare ni yaro."

Da fari Amar shafawa yayi da al'amarin ya shiga harkokin gabanshi, saida ya tuna waye tagwaicinshi kad'ai ya sake kiran lambarshi, yanzu ma police ne suka d'auka, dan haka baiyi k'asa a gwiwa ba ya garzaya douanes ya samu lieutenant, yana fad'a mishi lieutenant ya rufe ido yana zabga masifa ta inda ya shiga bata nan yake fita ba, cewa yayi ya tafi kawai ya barshi can shiya sani amma shi babu inda zaije.

Ummy ya kira a waya da niyyar yace ta lallab'i Abba, amma sai yaga tafi ma d'aukar zafi fiye da Abban, ita ma haka ya rabu da ita ya kira wayar Ammar aka bashi shi a waya, rarrashin duniya yayi dan ya fito amma Ammar sai yaga rayuwarshi ma bata da anfani, kenan babu wanda zai zo? Kashe wayar yayi ya bayar aka aje ya koma ya kishingid'a kamar a gadon sarauta yana ci gaba da tasbihi ga ubangiji yana kuma jiran yaji wa zai zo.


Bayan magriba lieutenant ya dawo gida, a d'aki ne yake fad'a ma Zeituna cewa "Kinji wannan mahaukacin yaron abinda yayi?"

Tasan sarai da wa yake dan haka bata kula shi ba ma dan bata ji dad'i ba, saida ya kalleta yace "Dake fa nake magana kina jina."

Cikin d'an fad'a fad'a tace "To me kake so nace maka?"

"Ban gane ba? Ina fad'a miki Ammar yana ofishin yan sanda kuma d'an uwanshi yaje yayi belinshi amma ya k'i tahowa wai sai naje da kaina, shine zaki fad'i haka."

Cikin gatse tace "Oho ashe sunansa Ammar, ai na d'auka baya da suna ne."

Kallonta yayi yace "...


*Comment ya sani muku typing, ku ci gaba da haka zakuji bayani.*

*Alhamdulillah*
14/10/2020 ร  00:58 - Ummulkhairi: ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ
*BADAK'ALA*
๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ

*Labarin Gaske*

*NA*

_SAMIRA HAROUNA_

*Litattafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._

*SADAUKARWA GA*

๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ _*AHALI NA*_๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

๐Ÿ‡ณ๐Ÿ‡ช *TAURARIN NIGER*
```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)```

โœช{T . N}โœช๐Ÿ“–๐Ÿ–Š๏ธ

https://www.facebook.com/101305508365889/posts/101311008365339/?substory_index=0&app=fbl


_Bismillahir rahamanir rahim_

_43_


"Ke wai ya kike neman b'ata min rai ne? Ya ina miki magana kuma kina magana kan wani abu daban."

Ba alamar farin ciki ita ma tace "Na fad'a maka gaskiyar abinda ke raina shine, bana jin dad'in halin ko in kula da kake nuna mishi, shi ma fa haihuwarshi akayi, yana da rai da zuciya, yana jin zafi haka kuma yasan meye farin ciki, dubi ka gani d'azu kafin fitarka a gabana ka kira d'an uwan haihuwarshi kake tambayar lambar account d'in shi, me yasa shi baka kira shi ba? Kana jin kunya ne saboda shine babba ko kuma saboda baka k'aunarshi ne? Ni ban tab'a ganin iyaye irinku ba wallahi, gaskiya Abban Ammar ba zan yarda na haifi abinda ke cikin nan nawa ba shima kana nuna mishi wannan k'iyayyar, sam ba zan lamunta ba wallahi, gwara ka fad'a min tun yanzu in baka son 'ya'yanka ne saina zubar da cik..."

"Ke." Wannan tsawar daya mata ce tasa tayi shiru tana kallonshi, baya k'aunarshi? Baya k'aunar 'ya'yanshi? K'iyayya? To wai duk meye na fad'in haka? Me na aikata da yasa ta tunzura haka har take fad'in maganganun nan? Kallonta yayi sai dai ya kasa cewa komai yana son sanin abinda take nufi, ganin bai ce komai ba sai kallonta yake yasa ta matso kusanshi ta rik'o hannunshi tana mai tausasa muryarta tace "Abban Ammar, kayi hak'uri da d'aga muryar da nayi a gabanka, amma ka sani wallahi abunne baya min dad'i ko kad'an, bansan ko har yanzu baku fahimta bane, ni marainiya ce babu uwa babu uba, nayi wayo a tare dasu amma ban girma dasu, sai dai duk da haka nasan soyayyarsu da yanda suka jani a jikinsu, hakan yasa har yanzu ina kewarsu kewar kulawarsu gare ni, duk sanda na tuna saina zubar da k'walla, haka duk sanda na ga maraya irina saina tausaya masa, karo na farko da naga wanda iyayensa ke raye kuma nake jin tausayinsa, shine Ammar, yana rayuwa tare daku a gida d'aya, amma hakan baisa kun iya fahimtarshi ba, a d'an zaman da nayi tare da ku da bai haura wata d'aya ba na lura da abubuwa da dama."

Saida ta share hawayen da suka taho mata sannan ta ci gaba da cewa "Ban tab'a ganin Ummy ta amsa sallamarsa ba, ban tab'a ganin ta amsa gaisuwa ko maganar da zai mata cikin dad'in rai ba, hasalima yana shigowa inda take zaka ga ta canza fuska daga murmushi zuwa had'e rai, haka zai juya ya fita ba tare data bishi da kallo ba, bata damu ya ci abinci ko bai ci ba, ya ya kwana ya kuma ya tashi? Amma Amar, haba-haba take dashi da nuna masa kulawa, bayan ta amsa gaisuwarshi zata zata tambaye shi abinci fa? Idan yana buk'ata da kanta take bashi ya ci, to me yasa shi d'ayan bata mishi haka, ka duba kaga lokacin bikinsu, Amar na ta kai da kawowa tsakanin waje da d'akinta suna ta shawara, amma shi Ammar shi kad'ai yake harkokinshi babu mai kula shi a gidan nan, kowa d'ansa ya sani kowa ya kama wanda yake k'auna ya rumgume, to me yasa? Shi ba d'an gidan nan bane? Ko kuma wani abu ya muku wanda kuke hushi dashi har haka?"

Kuka ne ya ci k'arfinta ta sunkuyar da kanta, saida ta saita nutsuwarta kafin ta d'ago tana kallonshi tace "Wallahi idan nice ake nuna wa wannan bambamcin na tabbata zan iya cutar da kaina, dan zanga kamar babu mai so na ne kawai gwara ma na mutu, Abban Ammar dan Allah ko sau d'aya ne ka zauna da yaronka ka fahimci matsalarshi kasan me yake ciki, ina tabbatar maka cikin sauk'i zaka fuskance shi, misali ni mana, wa zaiyi zaton zan samu wata girmamawa daga wajenshi? Amma sai gashi na ci darajar samun sunan uwa daga bakinshi, dan Allah kayi tunani akan abinda na fad'a maka, idan har kayi tunanin abinda ya dace nasan Ammar zai kwana gidan ubanshi yau, idan kuma kayi tunanin daka saba yi kullum to zai kwana a magark'ama, amma ka sani kar kuyi kuka da kowa duk ranar da kuka kaishi mak'ura har yayi abinda sunanku zai bazu a cikin gari."

Sakin hannunshi tayi ta shiga ban d'aki, gaba d'aya lieutenant rasa jijiyoyinshi yayi kamar an tsinkasu, yana so ya gyara ko da tsayuwarsa amma ya gagara, sai dunk'ule hannunshi da yayi sosai kamar zai naushi wani, yafi minti ashirin a wurin nan kafin ya samu da k'yar ya d'aga k'afarshi ya juya ya fita, lambu yaje ya samu kujera ya zauna, durmiya yayi tunanin abinda ta fad'a mishi, babu komai a ciki face zallar tsagwaron gaskiya, to amma inda matsalar take shi bai tab'a tunanin hakan rashin kyautawa ne ba, bai tab'a tunanin hakan zai iya zama wani abu ba duba dashi ba yaron goye ne ba da sai an kula dashi, da wannan tunanin ya kasa katab'us sai tubka da warwara yake. Ko da ta fito bata ganshi ta fito da niyyar zuwa wajen Amna, acan ta hangeshi zaune cikin lambu yayi shiru, girgiza kai kawai tayi ta wuce inda zata je, saidai a tunaninta ba zai je ya dawo da shi ba, dan haka ta tafi da sake wani shirin da zaisa dole yaje.

K'wank'wasa k'ofar tayi hakan yasa Amna tahowa da sauri, tana bud'a k'ofar ta ga Zeituna take ta bayyanar da damuwarta tare da fuszar da iska, kaucewa tayi a hanya ta shiga ciki sannan ta mayar da k'ofar ta rufe, juyowa Zeituna tayi ta kalleta tace "Amna lafiya kike?"

Cike da damuwa tace "Aunty Zeituna ina lafiya, yah Ammar tun safe ya fita har yanzu bai dawo ba, ya fad'a min zai jima amma ban d'auka zai jima haka ba, wallahi gabana sai fad'uwa yake ina jin tsoron abinda ya same shi."

Kallonta tayi da tausayawa tace "Kenan baki san mijinki na ofishin 'yan sanda ba?"

Zaro ido tayi tsoro da tashin hankali ya ziyarce ta tace "Ofishin yan sanda? Meya faru dashi? Wane laifi yayi?"

Dafata tayi tace "Kwantar da hankali Amna, ba wani babban laifi bane."

"Amma kuma yake hannun yan sanda? Me yake faruwa aunty Zeituna?"

Nan ta kwashe komai ta fad'a mata, cikin kuka wanda yafi kama dana shagwab'a tace "Yanzu aunty Zeituna Abba ba zai je ba kenan? A can zasu barshi ya kwana? Allah ba zai yiwu ba."

Murmushi ta mata tace "Nima na zo fad'a miki abinda in ki kayi ne mijinki zai kwana tare dake yau."

Da sauri ta rik'e hannunta tace "Fad'a min aunty Zeituna, me zanyi?"

Cikin murmushi tace "Kawo kunnenki kiji." Wani abu ta fad'a mata wanda nima an fad'a min abinda ta fad'a mata amma ni zan fad'a muku a rubuce, kallonta tayi tace "Kin tabbatar zaiyi aiki?"

Cike da son tabbatar mata tace "Amna dole zai fito miki da mijinki ko baya so, kawai ke dai ki jajirce ki zama mai naci kan hallayar mijinki."

Duk da tana jin ciwo a k'afafunta na bak'ar wahalar da tasha amma saboda k'arfin hali da gudu ta nufi d'aki tana fad'in "Nagode aunty Zeituna."

Jim kad'an ta fito da mayafi ta yafa a kafad'a ta shiga madafa, kwandon saka kwanukan abinci ta dauko ta fito, kan teburin cin abinci ta nufa ta jera kwanonin abincin tare da robar ruwa da lemu da kuma lemu orange da ayaba, saida ta zo gaban Zeituna dake ta binta da kallo tace "Aunty haka yayi?"

"Sosai ma, ai kawai ki basu mamaki." Ta fad'a tana kanne mata ido, tare suka fita inda Zeituna ta koma b'angarensu ita kuma ta fita, saida ta kai bakin titi kad'ai ta samu adaidaita sahu ta shiga, ba jimawa sosai mai adaidaitar ya sadata da inda zataje dan babu nisa sosai, bayan ta shiga ta fad'i wanda ta zo gani da cewa abinci ta kawo masa, abunka ga idan mutum wani babbu ne ko mai alak'a da babba, izinin ganinshi aka mata ta zauna inda aka nuna mata gabanta na ta fad'uwa dan bata tab'a zuwa ba sai yau dalilin mijinta. Da wani tako ne ya fito wanda yafi kama da fitowar sarki daga cikin gida zuwa kan karagar mulkinshi, kallonshi take a hankali soyayyarshi tana narkewa a zuciyarta, k'arfin halinshi da sababinshi yasa ta sakin murmushi, sab'anin shi da yana ganinta ranshi ya b'ace ya k'ara sauri a tafiyarshi ya k'araso wajenta, yana zuwa ba tare daya zauna ba ya zaro mata ido yace "Ke kuma meya kawo ki nan?"

Saida ta daure sosai kafin ta samu k'warin gwiwar cewa "Wajenka na zo mana."

Fizgo hannunta yayi ya mik'ar da ita tsaye yana fad'in
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment