Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

irin rayuwa ce, haba."

Juyowa yayi ya kalleshi ya had'e girar sama da k'asa yace "Kar ka fad'a min maganar banza, yan daudu ne ku ko mata da zaku ce shirinku na buk'atar b'ata lokaci?"

Cikin jin zafi Amar yace "Yan daudun ne kamar kai ba, ai kai gashi nan ka shirya a tsanake babu wanda ya takuraka, sai mu daka raina, wallahi ba dan ance Abba ne yace mu tafi tare ba da babu tsiyar da zata sanya na tafi da kai, tunda ai motarka ba fin tawa motar tayi ba."

Idon Ammar ne sukayi launin ja ya fito daga motar da k'arfi tare da zagayowa inda Amar yake a baya yana fad'in "Amar ni kake kira d'an daudu? Ni? Ni sa'anka da zaka kirani da d'an d...?"

Junaid ne yayi saurin rik'e Ammar d'in saboda bud'e murfin motar da yayi zai daki Amar da shima ke shirin fitowa, fitowa yayi a hassale shima yace "An kiraka d'an daudu, mu daka kamalta mu dasu bamu da zuciyar jin zafi ne ko me? Sai kai daka fi mu sanin ciwon kanka kenan, uban son girman tsiya, tsakani na da kai ko minti biyu babu, amma kullum kai ganinka ka girmeni da wata tazara mai tsayi."

Junaid dake ta rik'on Ammar yana bashi hak'uri cikin b'acin rai ya sa gwiwar hannunshi ya buge shi a baki yana fad'in "Dallah sakeni malam, kana ji yaro yana fad'a min magana son ranshi."

Junaid daya ji hanb'ara a baki baisan sanda ma ya sake shin ba, tuni jini ya gabce mishi harda hanci ma, sai kuwa Ammar ya cakumi wuyan Amar da hannu biyu ya shak'e shi sosai yana fad'in "Ni kake wa iskanci, ko sakan d'aya na baka ince dai ni na fara shan iskan duniyar? Shine zaka tsaya kana raina min wayo dan kawai kunga ina k'yale ku."

😔 'Yan biyu a madadin had'in kai sai gashi Ammar da Amar suna dakuwa kamar yara k'anana, amma Amar yafi galabaita saboda har yanzu Ammar bai sake shi ba daga shak'ewar daya mi shi, duk da haka kuma sai kai yake buga mishi a nashi kan, a d'aya b'angaren kuma yasa gwiwar k'afar shi sai tokara mishi yake a ciki, shi kuma duk dukan da yake ma Ammar d'in ma ba ji yake ba, ai kuwa gani Ammar zaiyi kisan kai yasa Junaid dake jinyar kanshi da Jamil suka fara k'ok'arin b'anb'are shi, dan tuni fuskar Amar ta fara had'a jini daga baki da hanci, amma saboda bak'ar zuciya ta Ammar sai ya dinga kai musu haura suma, ana cikin haka Ummy da ta ga mutuwar Hajia Fatime a kafar sada zumunta na alahlin Gaga ta taho gida suka ji muryar ta tace "Junaid, Jamil, ku barshi ya kashe shi."

Tana fad'a ta wuce b'angaren su ko kallonsu batayi ba, su Junaid kuma basu bar raba su ba saida Junaid ya tattara k'arfin shi ya fizgo Ammar daga jikin Amar yana fad'in "Dallah malam sake shi ko."

Amar na jin ya samu numfashi ya durk'ushe a wurin yana mayar da numfashin wahala, Jamil ne ya taimaka mishi ya mik'e suka nufi b'angaren iyayen sai Junaid daya bi bayansu bayan ya k'arewa Ammar kallo wanda ya buga murfin mota da k'arfi ya juya ya koma b'angaren su, suna shiga ciki suka ci karo da Zeinabu da faranti a hannu, tana ganin Amar a yamutse tace "Jamil lafiya? Meya same shi haka? Allah yasa dai ba hatsari yayi ba."

Kafin ya bata amsa Junaid ya shigo bakinshi har ya fara kumbura kuma har yanzu yana fitar da jini kad'an kad'an, da sauri ta saki farantin ta k'arasa ga Junaid tana fad'in "Kai wai lafiya? Meya sameku ne haka?"

Cike da k'aguwa Junaid ya d'an janye hannunta data tab'a shi yace "Umma ba komai, ba had'ari mukayi ba."

A lokacin Jamil harya zaunar da Amar kan kujera ya nufi d'akin Ummy dan ta fito ta duba shi, Zeinabu ce ta kalli Junaid tace "In ba had'ari kukayi ba to me kukayi? Dubeku fa."

Shima zama yayi a kujera ranshi a b'ace yana murza bakinshi, Soueba ba ta fito yayi daidai da fitowar Jamil dan Ummy tace babu inda zataje can su suka sani, Soueba ce ta kalli Jamil tace "Kai wai lafiya; meya faru ne haka? Meya samu Amar d'in."

Cike da damuwa yace " Mama ba komai, dan Allah kije ki samu Ummy ki fad'a mata Amar na zubar da jini ta zo ta duba shi, ni na mata magana amma ta k'i fitowa."

Amar na jin haka ya mik'e ya nufi d'akin Ummy duk da jirin dake son kwasar sa, cikin fad'a da hushi Zeinabu tace "Wai duk uban da aka tambaya sai yace ba komai bayan ga komai d'in, to koma menene ya faru ba sai ku fad'a ba, idan har kunsan ba zaku fad'a ba meye na shigo mana d'in? Wato inda iyayenku ne maza suka k'ura muku ido da tuni kun sakar musu zance, amma dake mune marainanku da muke wasa da ku kowane na hancin uwa sai dai yace ba komai, to kuje da ku da ba komai d'in duk kun ci uwarku."

Cikin b'acin rai Junaid yace "Dan Allah Umma meye haka? Mun fad'a miki ba komai ba shikenan maganar ta wuce ba, zaunawa zamuyi mu fad'a muku Amar da Ammar ne suka samu sab'ani har ta kaisu ga doke doke."

Mik'ewa yayi zai bar d'akin dan yana jin haushin surutun uwarshi da tseguminta, abun magana da ba na magana ba ita duk d'aya ne a gurinta, da gudu gudu ta tare gabanshi tana kallon bakinshi tace "Ammar fa ka ce? Halan kai kuma tsakaninsu ka shiga shiyasa ya maka wannan dukan?"

Rab'ata kawai yayi ya bar d'akin hakan ya k'ara hassalata ta fara d'aga murya tana fad'in "Ni na sani mana wani abu ai sai wannan mugun, wai shi Ammar meya d'auki kanshi a cikin gidan nan ne? Haka kawai ka addabar mana yara basu da damar da zasu wataya a gidan ubansu, kai ne kullum zuciya da cin zalin yan uwan ka, duba kiga yanda ya fasawa d'an uwanshi fuska, shi kuma wannan daga rabo ya fasa mishi baki, meye anfanin haka dan Allah? To wallahi na daina yarda daga yau, yanda yake jin haihuwarshi akayi a gidan nan haka suma yaranmu haihuwarsu mukayi, kuma nak'uda bata fi nakudaba bare yace uwarshi ta fi mu shan wahala, dan haka wallahi daga yanzu ni zan dinga tarewa kai na fad'an tunda dai shi mugu ne na gidan gaba."

Wannan b'ab'atun ne yasa Hajia Husseina fitowa daga d'akin ta, Soueba ce tace "Dan Allah Zeinabu kiyi hak'uri, da Ammar da Junaid ai duk d'aya ne a gurinki kamar 'ya'ya suke a wajenki, dan sun samu sab'ani bai kamata ace muna jin zafi haka ba, yan uwane su kuma mabiyi da mabiyi, dole dama ana samun haka saboda zaman tare, amma bai kamata ki dinga fad'in haka a kan shi ba."

Hajia Husseina ce tace "Lafiya ku kuma meke faruwa ne?"

Zeinabu ce tace "Hajia, Ammar ne ke fad'a da Amar, Junaid daga zai raba kawai ya samu shima ya bubbuge shi saboda fin k'arfi, shine yanzu nake magana Soueba take nuna min ba hakanan ba, to dan Allah yanzu su Ammar yara ne da za ace har yanzu suna fad'a? Sanda sukayi fad'an k'uruciyar wa ya tab'a cewa wani abu, ko da suna yara ma kullum shine ke saka mana yara kuka, kuma yanzu ace sun girma ma ba zasu huta daga kaidin shi ba saboda shi ya zama wani shaid'an."

Murmushi Husseina tayi tace "Ai gaskiya Soueba ta fad'a, ba kina kwaroronton sun samu sab'ani yanzu ba? To zuwa gobe ko jibi a falon nan zaki tarar da su kuma suna wasa tare kamar lokacin da suke yaran, kuma kema kin sani ko wasa suke sunfi tsokanar Ammar d'in, amma shi ko magana bai cika son yi ba, kenan meye abun wannan fad'an?"

Amar da yana shiga d'akin ya samu Ummy zaune kan kujerar coiffeuse (dressing miror) zunbur ta mik'e tana kallonshi ta nuna mishi k'ofar fita tana fad'in "Fitar min a d'aki Amar, fita."

Cikin muryarshi ta shan wahala ga dishi-dishin da yake gani yace "Ummy kiyi hak'uri na fad'a miki ab..."

Cikin tsawa tace "Ka fad'a min me Amar? Me zaka fad'a min? Shin Amar tun yaushe nake fad'a maka ka dinga hak'uri da halin d'an uwanka? Sau nawa ina fad'a maka kai da shi akwai banbanci na hallaya ka dinga kiyaye b'acin ranshi? Amar na fad'a maka kai ne d'an uwanshi wanda ko bayan ba ranmu zaka iya tsaya mishi duk da shine babba, me ya sa ba zaka dinga hak'uri ba da duk maganar da zata fito daga bakinshi? Tunda kafi kowa sanin halinshi magana indai har ta zo bakinshi ko ni uwarshi fad'a min yake bare kuma wani, amma ku tsaya kamar yara yan shekara biyar wai kuna fad'a, fad'a Amar da girmanku da komai? Amar so kuke duk gidan nan na zama mujiya ko kuma kamar wacce ta haifi annoba?"

Komawa tayi ta zauna cike da damuwa kamar zata fashe da kuka, cikin sanyin jiki da rashin jin dad'i ya durk'usa kusanta ya rik'e k'afar ta yace "Dan Allah Ummy kiyi hak'uri ki yafe mana, wallahi har cikin raina bana jin dad'i na ga kina damuwa akan halin Ammar, Ummy in kina damuwa da halinshi hakan zai iya janyo mishi fushin ubangiji, kiyi hak'uri dan Allah ki daina Ummy, nayi kuskure dana kula shi, amma na miki alk'awari hakan ba zata sake faruwa insha Allahu."

Hawaye ne suka taho mata ta d'ora kanshi a saman cinyarta ta kasa cewa komai, ita yanzu babban tashin hankalinta idan Hajia ta zo ta ga Amar da wannan ciwon a fuska, tashin hankalin zai fara ne idan aka ce Ammar ne ya dake shi, _kowane d'an adam da wanda Allah yake jarabtarshi da son shi, Hajia ita ta ta jarabta Amar ce, duk cikin 'ya'ya da jikoki babu wanda Hajia ke nunawa k'auna kamar Amar, babu wanda take nuna damuwarta a kanshi kamar Amar, takai ta kawo Amar na iya mata magana kan wani hukunci data yanke kuma ta janye shi, tun yana yaro yake samun kulawarta da soyayyarta, hatta yayesu da za ayi ita ta amshi Amar hannunta, kuma sun fara samun rashin jituwa ne da Ammar saboda kullum shi ke nasara akan Amar in dai ana fad'a, da kaji Amar na kuka to Ammar ne ba makawa, ita kuma saita dinga wa Ammar fad'a tana nuna mishi tsana a fili, hakan yasa shima baya wani k'aunar ta bare al'amuranta,_ to wannan ne yanzu damuwarta dan tasan sai rai ya b'ace fiye da yau, tana cikin wannan tunanin suka ji muryar Zeinabu na wannan fad'a, cikin sanyin murya tace wa Amar "Ka ji ko, na tabbata suna magana ne akan abinda ya faru."

Mik'ewa Amar yayi yace "Ummy ni fa bana jin dad'i na ji ana fad'an maganganun marasa dad'i akan d'an uwa na, zanje na fad'a musu kar wanda ya damu da abinda ya faru yanzu, tsakaninmu ne wannan kuma zuwa anjima zamu shirya."

Rik'e hannunshi tayi tace "Bara na duba maka ciwonka tukuna."

Zage hannunshi yayi yace "A'a Ummy zan dawo yanzu, kinsan tanti (Zeinabu)da ji-nini."

Mik'ewa tayi ita ma ta bi bayanshi, suna tsaye lokacin Husseina ke tambayar lafiya? Duk abinda ta fad'a akan kunnensu, Amar zai tafi wajenta Ummy ta rik'e shi, tana cikin wannan fad'an kuma sai ga Ammar ya shigo falon da takonshi na k'arfi kamar zai tashi k'asa.

Tunda ya koma b'angaren su tunanin Ummy ya dameshi yasan yanzu tana can tana kuka, shiyasa ya tashi yayi wanka ya canza kayan jikinshi zuwa wata shadda ruwan k'asa ya fito, tunda ya doso falon ya ji wannan hayaniyar ya sake tamke fuska kar ma aga damarshi, Zeinabu na fad'in "Ai dan ya ga wuri ne shiyasa yake mana iskancin son ranshi, suma ba dan suna wasu sakarkaru ragwaye ba har yaushe mutum kamarku wanda duk cikinsu babu wanda ya bawa wata biyu da haihuwa amma ku tsaya yana lallasaku son ranshi."

Husseina dai murmushi ne nata tace "Zeinabu ai abun a jini yake, tun daga yanayin tafiyarsu zaki duba, zaki fahimci ko a tafiya shi da k'arfi yake tashi sab'anin su."

Tsaki tayi tace "Ala wadaran naka ya lalace, to badan basu da wayo ba ai ko taron dangi ne su mishi wata rana su jijjiga shi shima ya ji jikinshi, wallahi sai kiga an zaunnnn..."

Gimtse bakinta tayi dan har ga Allah ta tsorata kuma gabanta ya fad'i lokacin data d'ora idonta akan Ammar daya had'e fuska yake kallonta ido jawur kamar kullum, Ummy da suke k'ofar d'aki tsaye tasan sai yayi magana, dan haka daga can tace "Ka wuce ka tafi inda za ka."

Amma ko kallon Ummy baiyi ba kuma har yanzu bai daina kallon Zeinabu ba yace "Idan kina ganin zasu iya ki basu shawara mana tunda kun shirya rasa 'ya'yanku."

Saida Ummy ta lumshe ido, dan tasan dama sai anyi haka, shi fa in dai maganar zata zo to sai ya fad'a ko za'a yanka shi, babbar matsalar kuma shine bai damu da girman wanda zai fad'awa ba ko kuma d'acin maganar ko rashin dacewarta, zai fad'a ne in ya so kai kayi kuka dan bak'in ciki, ko kuma ka zage shi kayi tir da halinshi shi duk d'aya ne a gun shi, takawa yayi ya nufi wajen Ummy tana ganin haka ta shige d'aki ta rufe k'ofar da makulli tana wani sabon kukan, k'ofar d'akin ya tsaya yana kallon fuskar Amar da tayi jina-jina, wani irin buga k'ofa ne yayi d'aya biyu baiyi na uku ba sannan yace "Kiyi hak'uri fa ki daina kuka, kinsan zai iya ja miki ciwon kai, daga haka kuma ake kamuwa da hawan jini ko ciwon zuciya, kina so ne ace zan nuna k'warewata na zama likitan zuciya a kan ki?"

Yana fad'in haka ya juya zai bar d'akin, cak kuma ya tsaya saboda duk baya jin dad'in ganin Ummynshi na kuka saboda shi, d'an uwan shi kuma na fitar da jini a dalilinshi, juyowa yayi ya kalli Amar dake shirin bubbuga k'ofar d'akin, sake d'auke kai yayi kuma wata zuciyar na fad'a mishi ai sai ya d'auka ka damu da shi ne, a hankali ya lumshe ido ya sauke numfashi a zuciyarshi yace "Ka damu da shi mana Ammar, ku fa ko a cikin ciki tare kuka rayu, ka d'auka kai da shi kamar kuna rayuwa ne da rai d'aya."

Bud'a ido yayi ya sake kallon Amar wanda shi ma yake so ya ga sun shirya ko dan mahaifiyarsu ta ji dad'i, kamar baya son maganar haka ya motsa bakinshi yace "Muje na wanke maka ciwonka."

Da sauri ya k'araso kusanshi ya rumgumeshi dan sam bai d'auka Ammar zai fara mishi magana ba, sosai yake ta k'ara cakume shi saboda k'auna, amma me Ammar zaiyi sai kawai ya raba kanshi da shi ya had'e rai yace "Miye haka malam sai ka b'ata min kaya da jini, muje ni dallah."

Da k'arfi ya juya ya fita Amar ya bi bayan shi yana girgiza kai, lallai a duniyar nan in har shi ya kasa fahimtar d'an uwanshi to babu mahalukin da zai iya fahimtarshi bayan wanda ya halluce shi, Husseina da Soueba da dariya suka bisu har Husseina na fad'in "Kin gani ko Zeinabu, shiyasa shiga fad'an yara ke da kunya wallahi, dan Allah ki daina damuwa da rayuwarsu, mu yarda cewa haka Allah ya hallici Ammar."

Tab'e baki tayi tace "Hum! Ni bana so na ji kuna cewa wai yara, yaran nan fa ba dan dogon karatu da sukayi ba wallahi da yanzu sun aje mana jikoki bibbiyu ko sama da haka."

Dariya Zeinabu tayi tace "Gashi kema kin fad'a kince yara."

Shigowar Junaid cikin sabon shiri yasa suka kalleshi a tare, shima dai fuskar nan a had'e take dan ranshi ya b'ace sosai, Jamil ya kalla wanda ke zaune yana latsa wayarshi yace "Kai in za ka je ka taso mu tafi."

Mik'ewa ya yi yace "Mu tafi kawai."

"Ina kuma zaku je?" Cewar Husseina, a tak'aice Jamil yace "Gidan roumji."

Zeinabu ce tace "Inda ubanninsu suka tafi zasu je, amma babu wanda zai iya fad'a mana dalilin zuwa."

A motar Junaid suka d'auki hanya ba ko waiwaiye saboda su isa da wuri, Ammar ma wani d'aki suka shiga wanda ya ware yake zuba duk wasu kaya da suka shafi na jinya, sannan har magunguna ke akwai da kayan aiki masu mahimmanci wanda babu su a ma k'asar baki d'aya, hakan yasa baya wasa wajen kula da su, zaune Amar yayi kan gado Ammar yasa k'aramin almakashi da k'ada da yan ruwan kashe ciwo yana goge masa, babu mai kallon idon wani bare magana, saida ya gama ya duba inda ke buk'atar a rufe yasa k'aramin bandeji ya rufe mishi, ba tare daya kalleshi a yace "Kana jin jiri?"

Saida ya d'an dafe kai yace "Eh, dan da k'yar ma na kawo kaina nan, na so na ce ka goye ni amma kuma..."

Kallonshi yayi yace "Amma kuma me?"

"Kana hushi da k'aninka, d'an uwanka, shak'ik'inka, sannan abokin rayuwarka." Duk yayi maganar ne cikin marairaicewa, k'ala bai ce masa ba sai ma wasu kwalaye dayake fito da su yana son d'auko wani magani, ya sha wahala kafin ya d'auko ya bud'e ya d'auki wanda yake buk'ata ya mayar da sauran, fitowa yayi daga d'akin jim kad'an ya dawo, ruwa ya bashi a roba tare da maganin yasha, d'aya maganin kuma ya sa a cikin kofi da ruwa, saida ya gama tafasa ya mik'a mishi ya shanye ya aje kofin, ba tare daya kalli fuskarshi ba yace "Ka kwanta kan gadon nan."

Ganin ya juya zai fita yasa Amar cewa "Har zuwa wane lokaci?"

Ba tare daya juyo ba yace "Har a busa k'aho."

Murmushi kawai Amar yayi shi kuma ya fice, yana fita kuma motar shi ya fad'a ya tayar, mai gadi na bud'e k'ofa ya suri motar yayi waje, hanya ya d'auka shima kamar zai tashi sama, shi ma dai kamar su Junaid hanyar gidan roumji ya nufa, sai dai duk gudunshi bai iya riskar su Junaid ba dan sun rigashi d'aukar hanya kuma suma gudu suke sosai.

*K'arfe* 06:20 na yamma Amar ya fito cikin shiri ya samu Ummy ya mata sallama yace zai tafi shima k'auye saboda kar ran Abba ya b'ace, cike da damuwa tace "Amar kayi hak'uri mana zuwa gobe sai mu tafi tare, tunda kaga ba lafiya ne da kai ba."

Dariyar gefen labb'a yayi yace "Haba Ummy lafiya ta lau fa, ki bari naje kawai kar Abba ya ga kamar bamu ji maganar sa bane, kuma kinga dukansu fa ina kyautata zaton can suka tafi, kinga gwara nima na hanzarta na tafi ko da ana sallah magriba ne saina isa."

Cikin sanyi tace "Shikenan Amar, Allah ya tsare ka ya kare gabanka da bayanka."

Murmushi yayi sosai yace "Ameen Ummy, sai mun dawo."

"A dawo lafiya." Ta fad'a tana binshi da kallo harya fita.

Yana fita su Hamna na shigowa da motonsu dan saida suka kai d'inki sannan suka dawo gida, haka ma ba jimawa Umaima ta shigo gidan tare da drebanta, sai Jamila da ta shigo gaf da magrib daga école.

*Gidan roumji*

Rana ta fad'i sosai su Junaid suka iso, tunda suka fito daga mota lieutenant da colonel ke kallonsu da mamaki, k'arasowa sukayi cikin mutane suka gaishesu da girmamawa tare da musu ta'aziya, sun shiga cikin gidan dan yiwa na cikin gida suma sai ga motar boss ta karyo kwana, da k'arfi ya ci burki ya kashe motar ya fito makulli da waya a hanu, ga kyau ga kyan tsari da hallita sai dai a wurina babu kyan hali, da k'akk'arfar tafiyar nan tashi ya k'araso yana sallama amma fa wanda yayi sa'a ne kad'ai ke ya ji sallamar dan kamar bai so yayi ba, saida yayi zaune ya tank'washe k'afafun shi kafin ya fara bawa na kusa da shi hannu, colonel kam daya tsura mishi ido a ranshi cewa yayi "Lallai yaro na, wannan da ace kai général ne na soja da anshiga uku, ko mu dake iyayanka dai saida muka gaishe da mutane kafin muka zauna saboda wurin mutuwa ne, amma kai sai bayan ka zauna kake gaishe da wanda ke kusa da kai, humm."

Lieutenant kuma haushin Ammar ne d'in ya kusa kashe shi shiyasa ma ya d'auke kallonshi daga kan Ammar d'in dan kar zuciya ta kwashe shi ya mareshi, yana gama tashi ta'aziyar ya fara danna waya, da sauri Labaran ya kalleshi yace "Ammar ka shiga ciki mana ku gaisa da matan."

Kallonshi yayi lokaci d'aya kuma ya mayar da kallonshi kan wayar, yana kallon wayar tashi ya mik'e yasa takalminshi ya nufi cikin gidan a ranshi yana fad'in "Yanzu mutum na shiga zasu saka maka ido suna kallo, kowace burinta ka mata magana ta ji dad'i, mtssss, shiyasa na tsani shiga irin taron nan."

*Ikon Allah sai kallo, to Ammar me ka d'auki matan? Sai kace wasu tsofaffin...*😏

Yana kallonsu su Junaid suma suna kallonshi haka kowa ya gama ya fito, suna zuwa kuma wasu har sun nufi masallaci wasu kuma na alwala, suma alwala sukayi suka nufi masallacin, tare sukayi sallah suka fito, fitowar lieutenant da colonel yayi daidai da shigowar Amar cikin kwanar, lieutenant a ranshi yace "Wato yaran nan sun raina mutane ko? Amma laifin duk na waccen babban kwabon ne."

Tsaye yayi hakan yasa colonel ma tsayawa, su Junaid da Ammar na fitowa lieutenant yace su zo, Amar na ganinsu saboda ya hasko fitilar motarshi ya tsaya wajensu ya fito, cikin girmamawa yace "Abba ina wuninku, har kunyi sallah ko? Bara nima na yi alwala."

Zai wuce lieutenant ya dawo da shi baya ya kallesu dukansu yace "Wato da na ce ku taho gaba d'aya shine kowa yayi gaban kanshi, yanzu ribar me kuka ci da kuka nunawa mutane ku kanku ba had'e yake ba?"

Shiru sukayi dukansu suna kallon k'asa sai boss da idonshi ke kan wayarshi yana latsawa ya rumgume hannu d'aya, juyawa lieutenant yayi ya kalli Ammar d'in da ya ga ya mayar dashi wani d'an iska ma, wani haushi ne ya kashe shi sai kawai yasa tafin hannu ya bangaji k'eyar Ammar, bai ankara ba yaji bugun dan haka ya juyo ya kalli mahaifin nashi, had'e fuska yayi ba alamar wasa yace "Abba meye haka? Kai baka san cewa kai shine mutum ba? Duk wani abu mai mahimmanci a cikin k'wak'walwa yake, so kake kasa na rasa komai nawa?"

Hannu ya d'aga da nufin sake mazgeshi colonel yayi saurin rik'e hannunshi yace "Ba kamata yayi ace ka fara tambayar meya faru ba kafin duk wannan b'acin ran, ko baka kula da fuskar Amar bane, sannan ka dubi Junaid ma, baka tunanin ko wani abu ya samesu a hanyar?"

Fizge hannunshi yayi yana kallon Ammar yayi k'wafa kafin ya kallesu yace "To naji, wa zai fad'a mana meya faru?"

Shiru sukayi sai wuk'i-wuk'i da ido da sukeyi, Labaran ne ya kalli Jamil yace "Kai ba tambayarku ake ba kuka mana shiru?"

Jamil kam kallon Ammar yayi wanda ya ga ya kalleshi, idonshi kad'ai suka fassara mishi manufar kallonshi, dan haka ya ja baki yayi gum saboda tsoro, sai dai ya manta gaba da gabanta, colonel ne cikin tsawa yace " Wai ya ana muku magana kuka mana shiru? Shin ku yan mata ne bare ku d'auka son ku muke."

Wani kallo Ammar ya mishi yace "Idan ma yan mata ne mu sai mu tsaya muna sauraron tsofaffi irinku."

Labaran kam bushewa yayi da dariya inda lieutenant ya zabura zai bugeshi Labaran d'in ya rik'e shi, cikin dariyarshi yace "To ai gaskiya ya fad'a, tsofaffin ne mu mana."

Kamar daga sama suka ji saukar mari ji kake "Tauuuuuu."

Da sauri Junaid ya dafe kunci saboda wani mahaukacin mari da colonel ya watsa mishi yana fad'in "Iskanci kai, ana muku magana zaku d'auke mu wasu shashashu."

Lieutenant ne yace "Meye haka saboda Allah? Yanzu shine kenan yayi laifi a wurin nan? Me ya sa ba zaka mari wannan ba dake kusa da kai yana mana shak'iyanci sai wannan? Saboda a ganinka wannan ne ka haifa su kuma wad'annan duk 'ya'yan yan uwanka ne, mtsss."

Lieutenant Jamil ya kalla ya zaro ido yace "Yanzu zaku fad'a mana meya faru da har yasa ku ka k'i bin umarnin dana baku na a taho tare?"

Cikin rawar murya Jamil yace " Dama da zamu..."

Karaf Amar ya karb'a da cewa "Ni ne fa na samu
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment