Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

son fad'a ma Hajia, matsalar d'aya ita ce ta yanda zan fara fad'a, amma nasan ko da na fad'a rai ba zai b'ace ba kamar zamanin baya."

Cike da damuwa Hamna ta kalleta tace "Ummy ni kaina tsoro nake ji, wallahi kullum tunanin al'amarin gigita k'walwata yake, duk da yanzu dai abubuwa sun canza, amma muyi kallon abun ta b'angaren yer uwata da kuma Abba, Ummy ya zasu ji idan suka ji maganar nan, ya yer uwata zata kalleni taji wai Shureim d'ana ne, d'an nawa ma wanda na haifa tare da mijinta, duk da dai kafin aurensu ne amma abun akwai gigitarwa, sannan Abba da yake mishi kallon d'an shi shima ya zaiji Ummy?"

Jinjina kai Ummy tayi tace "Wallahi Hamna karki so ki tona raina kiji yanda a kowace rana nake bacci da fargaban nan, ni kaina nasan wannan abune mai matuk'ar d'aure ne, abune da ko da ya tab'a faruwa to ba dai a k'asar hausa ko kuma anan kusa ba, k'anwata Gaishata da bana b'oye ma komai, amma sai gashi wannan karan har alk'awarin fad'a mata da nayi bai cika ba, Hamna tun tana tambayata na fad'a mata har ta kai ta gaji ta daina, ni kaina bansan ta inda zan fara kawo k'arshen labarin nan da nine na fara shi ba tun farko."

Cikin jimami tace "Kawai Ummy mu jira Amna ta samu lafiya a gama sabgar nan, kukan kura kawai zamuyi mu fad'a, in ya so ayita ta k'are kawai ko mun huta mu ma."

Jinjina kai tayi tace "Allah ya shige mana gaba."

Jin motsin zasu fito yasa *Amie* barin wurin da sauri wacce data mik'e zata tafi Zeituna ta fad'a mata ai Hamnar ta dawo tana wajen Ummy, tana zuwa yayi daidai da jin wannan babban sirri da ake ta b'oyo, da sauri ta koma b'angaren Amna ta zauna sai ga Hamna sun shigo, kallonsu take tana ta sak'a da warwara, sai dai ta girgiza kai kawai tayi murmushi, sai taji ma ta kasa tashi ta bar gidan, Amna da Hamna take kallo tana hasaso Ammar a idonta, lallai duk cikin lamarin Amna aka rainwa hankali, to miye abun b'oye mata ana zalintarta, kai ba zai yiwu ba wallahi, *gwara komai ya fito uban kowa yaji duk a k'one tare*, haka ta ci gaba da zama har k'arfe *09:00* dare yayi.

Mutanen d'akin sun rage daga Amna da Hamna sai Amie, sai kuma Husseina wacce suke kwana tare amma tana nesa dasu sai gyangyad'i take, Hamna ce ta tashi ita ma tace "Besty bari na fad'awa Ummy saina aje ki gida."

"Ok besty." Ta fad'a tana binta da kallon yar rainin hankali, saida ta ga fitarta ta gyara zama ta kalli Amna da kyau tace "Amna ke fa yanzu nan baki san komai ba ko?"

Kallonta tayi tace "Komai kamar me fa?"

Girgiza kai tayi tace "Allah sarki, gaskiya Amna ana cutarki a gidan nan, mijinki, yar uwarki da kuka fito ciki d'aya, da kuma Ummy, sun taru suna raina miki hankali."

Duk mutanen da Amie ta ambata mutane ne da suka zama dunk'ulen rayuwarta, mutane ne masu matuk'ar mahimmanci a tattare da ita, dukansu zata iya sadaukar da rayuwarta akan su, dan haka a take taji wani haushinta da tsanarta sun dira a zuciyarta, sama da k'asa ta kalleta tace "Ni dai a sanin dana miki ban sanki da gulma da yarfe ba, bansan kuma yaushe kika koyesu ba?"

Murya k'asa k'asa tace "Amna wallahi maganar gaskiya nale fad'a miki, idan ma baki yarda ba to ki tambayesu kiji."

A kausashe tace "Na tambaye su me Amie? Wai dama gulma kika zo ba dubiya ba? To tashi ki fita."

Tab'e baki tayi ta mik'e tsaye ta kalleta tace "Dama ko a yan biyu akwai baud'add'e, ke kam ba zaki tab'a gane irin cutar da ake miki ba, amma idan mijin naki ya shigo ki tambayeshi waya
haifi Shureim? *Shi ko mahaifinshi*, inhar gaskiya zai fad'a zai ce miki shine, in kuma k'arya zai fad'a zai fad'a miki mahaifinshi ne."

Juyawa tayi tana fad'in "Sai anjima."

Zata fita Hamna ta shigo, juyawa tayi ita ma tace "Yawwa to yi sauri muje Hajia tace kar na jima."

Cikin wata irin murya Amna tace "Dakata."

Tsayawa sukayi suka juya suna kallonta, ba tare data tashi daga inda take ba ta kalli Hamna ido cikin ido babu yanayin wasa tace "Ki koma ciki babu inda zaki kaita."

Da mamaki Hamna tace "Me yasa?"

"Saboda munafuka ce." Ta fad'a kai tsaye, murmushi Hamna tayi a tunaninta jikin ne ya motsa tace "Kiyi hak'uri kinji yer uwa, ba jimawa zanyi ba yanzu zan dawo."

Da k'arfi tace "Hamna babu inda zaki kaita, in kuma baki yarda ba to kuje ga hanyar nan."

Kallon Amie Hamna tayi ta k'yabta mata ido alamar su mata wayo sai a zahiri da tace "Besty kawai ki tafi tunda yer uwata bata so ba zanje ba."

Jinjina kai Amie tayi ta fita, Hamna na ganin haka ta kalli Amna tace "Akwai abinda kike so na miki ne ko ka naje na kwanta? Bacci nale ji sosai."

Kallonta tayi tace "Kije ki kwanta saida safe."

Juyawa tayi ta fita tana zuwa ta ja mota ta fita ta d'auki Amie, hak'uri ta bata kan abinda ya faru tace ba komai. Tana fita Amna ta bita da kallo, murmushi tayi tace "Ko yaushe Amie ta haukace kuma? Su yanzu nan mutane kallon mai hankali suke mata? Lallai ma Allah ya bata lafiya."

Daga nan zaune ta saki wannan maganar kamar anyi rubutu a saman ruwa, jikinta ya bata Hamna ta tafi ta kai Amie gida ne, k'wafa tayi tace "Haba, kuje d'in mu gani."

Saida sukayi nisa da gida kuma basu kai ko rabin gidansu Amie ba mota ta tsaya cak, ko da Hamna ta duba wajen dake bayyana idan mai ne babu taga tanki cike yake, nan ta shiga tayar wa amma mota shiru, tsayawa tayi tana girgiza kai tana murmushi a hankali take fad'in "Amna, Amna, amma zan ci uwarki, ni zaki wa iskanci."

K'wafa tayi ta kalli Amie tace "K'awata, hak'uri zakiyi ki samu adaidaita ki hau, in dai ina tare dake to babu inda zan gusa."

Da mamaki ta kalleta tace "Me yasa? Wani abun ne ya faru?"

Murmushi ta mata tace "Ba zaki gane ba, kawai ki samu adaidaita."

Bud'e motar tayi ta fita ta kalleta tace "To ke ya zakiyi?"

Saida ta kalli titi tace "Karki damu, idan ma bata tashi ba zan kira a zo a d'auke ni."

"Ok, ki kula da kanki."

Jinjina kai tayi tace "Ok, saida safe."

Nan ta samu adaidaita ta tafi, tun a hanya data shiga WhatsApp d'inta ta kasa hak'uri ta tab'o sauran k'awayenta su biyu, gulma ajali inji yan magana, haka suka jima suna tattaunawa suna fad'in ashe ta ma fisu iskanci, shine in taga suna rayuwarsu saita dinga nuna tana k'yamar abun, ashe ita har shege ma gare ta kuma da mijin yar uwarta.

Saida ta ga tafiyar Amie ta kira Amna a waya, har ta kusa tsinkewa sannan ta d'auka tace "Lafiya? Har kin kaita d'in?"

Dariya Hamna tayi dan su rabu lafiya kar ta jawa motarta kwana akan titi, cikin muryar rarrashi tace "Dan Allah yar k'anwata taimaka min ina so na koma gida kinji, dare kayi kar Abba ya min fad'a."

Cikin kumburo baki Amna tace "Na k'i d'in, bani kika rainawa hankali ba?"

Sake mak'ale murya tayi tace "Dan Allah fa nace."

"To shinenan, ki bani hak'uri yanzu." Cewar Amna.

Saida ta gyara murya tace "To aunty Amna kiyi hak'uri."

Murmushi Amna tayi tace "Shikenan to kiyi sauri ki dawo gida kar wani ya sace min ke."

Dariya tayi tana wa motar key tace "An gama zuciyata."

Ko da ta kunna ta kama tana murmushi tayi baya baya ta d'auki hanyar komawa gida.

*Da safe* Hamna na ta kai da kawon gyara falon an gama ma bรฉbรฉ wanka, duk inda tayi sai Amna tabi ta da kallo, tun bata lura ba har ta ankare, tun abun bai tsaya mata akai ba har ta fara tsarguwa da kallon, tsayawa tayi tana kallonta tace"Wai ke lafiya?"

Sai kawai ta bushe da dariya kamar mahaukaciya, kallon mamaki Hamna ta bita dashi ta girgiza kai ta ci gaba da aikinta, Ummy na shigowa cikin shirin tafiya aiki da Shureim a hannunta, hannu ta tarawa Shureim tace "Zo nan."

Takawa yayi ya je wurinta ya tsaya, rik'e hannunshi tayi tana mishi wani kallo kamar yau ta fara ganinshi, sai kawai ta matso dashi kusanta ta sumbaci goshinshi, saida ta d'auke bakinta ta sake kallon fuskarshi sai tace "Kai ni fa sai naji na fi sonka da aka ce yar uwata ma ta haifeka."

Wani yamutsawar hanji Ummy da Hamna suka ji a lokaci d'aya, Husseina dake karin kumallo kallonta tayi irin kallon anya kuwa Amna, da sauri suka kalli juna suna zazzaro ido na alamar tambayar me ke faruwa, kallonsu Amna tayi a tare saida ta gama kallonsu sai tayi dariya ta nuna Hamna da hannu tace "Sakarya, ji yanda kika zaro ido kamar mahaukaciya, ko ke ma kin haukace irin na k'awarki?"

Da sauri suka saisaita nutsuwarsu, sai Ummy data kalli Husseina tace "Anya Hajia kuwa lafiyarta k'alau?"

Cikin murya k'asa k'asa tace "Ni ma dai abinda nake tunani kenan."

Amna kam kallon Shureim ta sake yi tace "Baka tafi islamiyya ba kai?"

A hankali yace "Yanzu Ummy zata kaini."

Murmushi ta masa tace "Yawwa, kana ji ko? Ka dinga karatu sosai saboda ka zama babban malami, kana so ka zama kamar wannan kai ma?"

Ta fad'a tana d'aukar wayarta, wa'azin *ustaz Rayyadun* (Allah k'ara girma malaminmu) ta nuna masa na vidรฉo tace "Ka gani ko? Ka zama kamar wannan kaima, kana so?"

Kai kawai ya d'aga mata irin shi dai yana saurarenta, su dai kallonta suke har Ummy ta mik'e ta kama shi suka fita, hankalin Hamna ya kasa kwanciya duk a takure take jin kanta, ta k'i yarda su had'a ido da Amna wacce ita kuma take ta binta da kallo har yanzu, idan ta ga Hamna ta k'i kallonta sai ta bushe da dariya, duk wanda ya zo gidan haka zai iskota a wannan yanayin, gashi kuma Hamna babu damar da zata barta dan wani abun sai tace dole Hamna ce kawai zata mata, haka suka dinga wannan zama babu dad'i babu hira tsakaninsu, sai dai ita Amnar tayi ta nata maganganun masu kama dana mai shirin barin duniya.

*Kwana uku* yau da faruwar wannan lamari, shirin biki ake ta yi sai dai ba wani da karsashi ake yinshi saboda yanayin jikin mai jego, kullum cikin taka tsantsan ake kan d'inkinta, ana yawan kwakwafarta kan rage magana da dariya mai k'arfi, amma abun sai a hankali in tayi wani abun kamar dai k'walwarta ce ta fara samun matsala. Yanzu ma Ammar ne ya shigo da babbar leda a hannu, ko da ya gaishe da mutanen d'akin ya nufi nashi d'akin, kamar daga sama aka tsinci muryar Amna tace "Ammar."

Cak ya dakata ya juyo ya kalleta, *Ammar*? Tunda yake da ita daga k'uruciya har girmanta bai tab'a ji ta kama sunansa ba haka, dama dai waccen marar kunyar ce, su kansu mutane mamaki ne ya kama su jin yanda ta kira sunan nashi kamar sunan Ammar k'arami, shi kanshi Ammar k'arami saida ya juyo ya kalleta, har ya cire hannunshi daga abincin da yake ci zai taho tace "Ba kai ba zauna."

K'ok'arin mik'ewa ta shiga yi hakan yasa Ummy taimaka mata ta tashi, saida taje kusanshi ta kalle shi tace "Muje ciki."

Kallon Ummy yayi daga nesa, ita ma shi take kallo kallon nima bansan komai ba, wucewa yayi d'akin ta bishi a baya, sua shiga ta zauna kan gadonshi tana kallonshi tace "Kana ji ko? dan Allah ka kula min da yarana, ka dinga kaisu makaranta kan lokaci, kaji ko?"

Shi mamakin yanda take masa magana kamar wacce ta haife shi ne ma yake, ganin bai ce komai ba yasa ta amso ledar hannunshi tana fad'in "Kawo to, watak'ila kallon nan da kake min dan ban karb'a bane."

Aje ledar tayi kan gado ta mik'e zata fita sai kuma ta juyo ta kalleshi tace "Kasan wannan k'awar ta mu Amie?"

Kai kawai ya jinjina mata yana ci gaba da kafeta da ido, dariya tayi sosai tace "Baka san ta hauka ce ba? Kasan haukan data zo min dashi gidan nan?"

Kai ya girgiza mata kawai dan jin maganarta yake kawai a sama, wata dariyar ta sake yi tace "Wai a haukanta cewa tayi kai da Ummy da yer uwata kuna cin amanata, kasan me ta fad'a min?"

Ajiyar zuciya ya sauke ba tare daya daina kallonta, jinjina kai tayi ta matso kusanshi cikin rad'a tace "Wai cewa tayi Shureim d'an ka ne, kaji fa mahaukaciyar, ta manta Ummy ce ta haife shi, to kuma ni ko wa ma ya haife shi ina son shi, inda yer uwar ta wa ta haife shi wallahi da naji dad'i."

Kallon fuskarshi tayi da kyau sai tayi dariya tace "Kai ma ka girgiza ko? Karka damu ci gaba da abinda kake."

Ko da ta fad'a ta juya a hankali ta bar d'akin, shi fa tunda ta fad'i haka gabanshi ya yanke ya fad'i, kawai bata aje hankalinta bane data fahimci tashin hankalin daya shiga jin wannan magana, ita dai ta d'auki abun wasa da k'arya da kuma hauka, amma shi baya da dalilin da zai k'aryata Amie, hasalima zai iya cewa ya yarda da abinda ta fad'a d'in, yana da gamsassun dalilai da hujojji.

Yanda ya zazzare ido haka ya zauna bakin gado, tunani ya durmiya yana tuna faruwar komai sala sala, tabbas bayan faruwar al'amarin ne cikin Ummy ya bayyana, lokacin daya ga canji a jikin Hamna har ya so fallasawa Ummy ta jijjiga sosai har ta mare shi, sannan ta matsa sosai har saida aka mata hanyar data shiga sahun masu tafiya France kuma ta k'ara kan lokacin daya kamata ta dawo, kuma ai Hamna bata nan a lokacin, to kenan taya haka ya faru? Girgiza kai ya shiga yi yana ta tunanin abubuwa da dama, ji da yayi kamar kanshi zaiyi bindiga yasa shi mik'ewa da sauri ya fito.

Har tsakiyar mutanen da take zauna ya ja hannunta inda hankalin kowa ya koma kansu, janta kawai yake ita kuma tambayarshi take ina zai kaita lafiya? Saida ya kaita kusan d'akin mai gadi ya tsaya ya saki hannunta, rik'e k'ugu yayi da duka hannayenshi yana kallon fuskarta kamar ba gobe, ajiyar zuciya ya sauke mai k'arfin gaske.

Cikin wata sanyayyar murya amma sautin ta zai nuna maka babu wasa a cikinta kuma mamallakin muryar zai iya yin komai a yanzun yace "...


*Alhamdulillah*
14/10/2020 ร  00:58 - Ummulkhairi: ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ
*BADAK'ALA*
๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ

*Labarin Gaske*

*NA*

_SAMIRA HAROUNA_

*Litattafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._

*SADAUKARWA GA*

๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ _*AHALI NA*_๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

๐Ÿ’ซโœจ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*๐ŸŒŸ
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_๐Ÿค

โ˜† *[ T.M.N.A]* โ˜† ๐Ÿ“–๐Ÿ–Š๏ธ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_

_63_

"Ummy, da gaske wai Shureim d'ana ne?"

A firgice ta kalleshi yayin da taji har ruwan jikinta na neman tsayawa, yanda ta zaro ido zai nuna maka bata da gaskiya, gudun kar ya fahimta sai tayi saurin b'atar da firgicin ta jawo mamaki ta dasa a fuskarta tace "Ammar, wace irin magana ce wannan? Wane Shureim d'in?"

Da hannu ya mata alamar ya isa haka tare da cewa "Ummy, kin sani na sani abinda ya faru, idan zan iya kawo miki hujojji na sai mu kwana anan ban gama ba, tun waccen lokacin ma nayi shiru ne saboda gudun b'acin ranki, Dan Allah Ummy inhar gaskiya ne abinda naji ki fad'a min."

Cikin fad'a tace "Ammar wace maganar banza ce wannan? Ya zaka tasa ni a gaba kana tambayata wai Shureim d'anka ne? Zargina kake da cin amanar mahaifinka ko me? Ni sam ban ma fahimci me kake nufi ba."

Matsawa yayi daf da ita murya k'asa k'asa yace "Ummy ba haka nake nufi ba, Shureim an ce d'ana ne dana haifa tare da Hamna, shine nake so naji gaskiyar."

Cikin b'acin rai da d'aga murya ta rintse ido tace "Ammar bana son maganar banza, uwarka ce ya zaka sani gaba kana min wannan tambayar rashin mutumcin? Fad'a min wane d'an iskan ne yake son shiga tsakani na da kai da har ya fad'a maka wannan banzan shirmen?"

Cikin fitar hayyaci da b'acin rai da yanayin da shi kanshi baisan yayi magana dashi ba ya d'aga murya sama da ta ta yana fad'in "Ummy babu wani dake son shiga tsakani na dake, magana ce ta fito kuma ina so na sani nima, a matsayi na na d'anki ina da hakk'in da zan san haka."

Saida ya dasa aya ya iya jiyo sautin muryarsa can sama, dafe kanshi yayi da hannu biyu yana d'an murzashi a hankali, kallonta yayi ya rik'o hannayenta duka buyu yasa idonshi cikin nata yayin da take mishi kallon mamaki yace "Ummy ki daure ki fad'a min mana, da gaske d'ana ne ko kuma k'arya aka fad'a?"

Cikin zubo da hawayen da suke nuna ta k'are min ta kafe shi da ido tace "Ammar waya fad'a maka maganar nan? Wane d'an banzan ne?"

Kamar zai fashe d a kula yace "Ummy abinda nake so naji daban, abinda ke ma kike so kiji daban, amsar tana da sauk'i fa Ummy idan kikayi niyyar fad'a min, kawai zaki ce min eh ne ko kuma a'a."

K'yabta ido tayi tana kallon gefenshi, jinjina kai yayi yace "Zan tabbatarwa kaina."

Ko da ya fad'a ya wuce da k'arfi ya tunkari falon Hajia, da gudu gudu ta bi bayanshi tana fad'in "Ammar ina zaka je? Me kake shirin yi ne wai? Ammar..."

Bai tsaya ba har saida ya shige falon, shigarsu yayi daidai da fitowar Hajia daga d'akin tare da duk yan kuci-kucin yaran suna ta mata shirme, da sauri ya tunkareta inda ya ga Shureim, hannunshi ya kama ya juya zai fita dashi Ummy ta rik'e hannun Shureim ita ma, juyowa yayi yace "Ummy dan Allah sake shi."

Matsowa tayi kusanshi tace "Ammar baka da hankali ne wai? So kake ka min terere cikin mutane? Ina zaka kai shi?"

Gyara tsayuwa yayi yace "Asibiti zamu je."

Ko da taji yace asibiti tasan me zaiyi acan, sunkuyar da kai tayi k'asa sai Hajia data matso kusansu tana kallon kowane tace "Ku kuma lafiya? Meya faru ne haka?"

Kallon Hajia yayi yace "Hajia, Shureimmm..."

Yanda Ummy tayi saurin rufe masa baki yasa shi jan k'arshen sunan, kallonta Hajia tayi ta fahimci bata so taji, sai kawai ta kama hannun Ummyn da Ammar ta tura su d'akinta, Shureim ta kama hannunshi shima suka shiga ta mayar da k'ofar ta rufe, zaune tayi kan gado ta kallesu ta nuna musu kujerar dake d'akin mai kama data gwal tace "Ku zauna dan Allah."

Ummy na kallon Ammar ta tsoma mazaunanta kamar tace wayyo ita wayyo kanta, a nutse ta kallesu ta tattara hankalinta gaba d'aya kansu tace "Me yake faruwa Sa'ada?"

Cikin in'ina tace "Hha.jia, ba kommai..hajia."

Murmushi tayi ta kalli Ammar tace "Ammar lafiya? Me yake faruwa da kake d'aga murya fiye data mahaifiyarka?"

Ummy ya kalla ya sunkuyar da kai yace "Kiyi hak'uri Ummy ki yafe min, wallahi bansan na d'aga murya fiye da taki ba, kiyi hak'uri dan Allah."

Dan motsa kanta tayi wanda yake nuna tace ba komai, Hajia ya kalla yace "Hajia, in baki manta ba na fad'a miki abinda ya faru tsakani na da Hamna shekaru kusan biyar kenan."

Sororo Ummy ta kalle shi da wani fitinannan mamaki, ya fad'a mata? Yaushe akayi haka bata sani ba? Kuma shine Hajia bata nuna mata ta sani ba? Tana kallon bakinshi taji yace "Shine yanzu aka fad'a min Shureim d'ana ne, Hamna ce ta haife shi, kuma ina tambayar Ummy amma ta k'i fad'a min, Hajia ina so na sani d'ana ne ko kuwa."

Hajia ma mamaki ne ya bayyana a fuskarta, kallon Ummy take tace "Sa'ada."

D'ago kai tayi ta kalleta, d'orawa tayi da "Da gaske ne abind yake fad'a?"

Cikin sanyin jiki tayi shiru ta kasa cewa komai, ba zata yarda ta sake yin k'arya ba, tunda gashi wacce tati shekaru ma yau ta fito, sai dai kuma ba zata iya amsa kai tsaye da eh ba, ganin wannan shirun na ta yasa Ammar kallonta da mamaki yace "Ummy me yasa kika yi haka?"

Kallonshi tayi saita sake yin k'asa da kanta ta fara zubar da hawaye, girgiza kai yayi kamar zai yi kukan shima na tausayin mahaifiyarshi yace "Ummy me yasa kika aikata haka? Dama har soyayyar da kike min ta kai wannan matakin?"

Fashewa ta sake yi da kuka sai kawai yace "Ummy in kinyi hakane saboda ki kare mutumci na dana Hamna, ai da fad'a min kikayi saina tayaki kare wa har zuwa lokacin da kike so kowa ya ji, idan kuma kinyi ne saboda gudun abun kunya da kallon da mutane zasu mana, Ummy ai naga ba akai na aka fara abun kunya ba, a gidan nan bani ne farkon daya fara aikata irin wannan laifin ba, Ummy ina kika kai tonton Labaran? naga shima ba da aure aka same shi ba kuma yana rayuwarshi hankali kwance, hasalima ba tare daya tab'a ganin mahaifinshi ya taka wani babban matsayi na rayuwa."

Cikin nuna mata da hannu ya ci gaba da fad'in "Sannan ki dubi Huda, gata nan tana rayuwa cikin dangin mahaifinta ba tare da tsangwamar kowa ba, haka ma Junaid, rayuwarsa yake yi bai damu ba, kuma babu wanda yake iya d'aga ido ya kalleshi ya fad'a masa hanyar da aka same shi, Ummy sai ni ne dan na aje d'an gaba da fatiya za'a min zund'e da kinibibi, Ummy hakan ma ai tayar da lissafi ne yayi, kinga kenan zai zamana a kowane d'aki akwai shege."

Yanda ya fad'a da k'arfi yasa ta rintse ido, kallon Hajia yayi yace "Hajia, ki fad'a mata ko ta kwantar da hankalinta ta nuna wa yaro ubansa, ki fad'a mata abun kamar a jininmu yake."

Wani murmushin rainin hankali Hajia tayi ta kalli Ummy tace "Hakane Sa'ada, ki fad'a masa in dai har kinsan d'ansa, karki ji komai a game dani, kamar yanda ya fad'a ne a kowane d'aki akwai yaro irin Shureim, sannan ni kaina da kike gani fa sanda nake budurwa na tab'a yin cikin nan, ni na ma fisu laifi saboda zubarwa nayi, su kuma basu zubar ba sun haifi abinsu, to kika sani ko fantin dana shafawa kaina ne har yanzu yake biyar zuri'ata."

K'ara saita muryarta tayi ta dafa hannun Ummy tana kallon fuskarta tace "Sa'ada, ba zan manta sanda aka kawoki gidan nan ba, ni shaida ce Hassan ya same ki a tsarkake, haka ma Hadiza ina d'aya daga cikin wanda suka taimaka mata a daren farkonta, wannan duk ya isa ya zama hujjar da yaranku zasu k'auracewa zina, amma inda gizo ke sak'ar shine ni, ni d'in ne duk ni na gurb'ata muku iyali, ki dubi Alhaji bawan Allah wanda bai san hawa ba bare sauka, shi ya kamata ace yafi kowa damuwa, amma shi ma ido ya saka min yayi hak'uri dani har saida mai rabawa ta raba."

Numfasawa tayi tana ci gaba da kallonta tace "Sa'ada, ki dubi girman Allah ki fad'a masa gaskiya, Shureim d'an waye a cikin Ammar da Hassan?"

Kutumar bala'i! Shine abinda Ummy ta fad'a a ranta, Hajia! Ciki? Lallai ma, idan ta fahimci inda zancen ya dosa duk ita ce ma silar komai, lallai su Hajia manya, k'warin gwiwa ta samu daga jin kalaman Hajia, sai kawai taji bari ta fad'a da alama ta samu sauk'i.

Ba tare data kallesu ba ta fara goge k'walla cikin muryar data sha kuka tace "Gaskiya ne, Hamna ce ta haife shi bani ba."

Hajia ce tace "Amma Sa'ada taya kika iya shirya lamarin nan ba tare da mijinki ma ya sani ba?"

Tsaf Ummy ta fad'a musu duk yanda akayi har haihuwarta, d'orawa tayi da "Wallahi a lokacin na tsorata ne sosai na rasa yanda zanyi, tunanin hukuncin da zaku d'auka akan shi ke da mahaifinshi ya k'ara tunzari muka ci gaba da b'oye, amma dan Allah kuyi hak'uri ku yafe min, ya lalata rayuwar yarinya ni kuma na taimaka masa, a idon doka da mutane duk mun aikata laifi."

Cikin kuka
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment