Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

masa? Kallonshi yayi yace "Hak'uri fa? Ai wannan maganar ma bata taso ba yaro."

Hanyar fita yayi Hajia ta fizgo hannun Hamna cikin rad'a tace "Ki wa Allah Hamna naga kamar ke d'in aljanunshi na sonki ki dakatar dashi, karya je ya kashe d'an mutane."

Kallon Hajia tayi ta had'e fuska tace "Ni kuma Hajia? Rufa min asiri na mutu maza su binne ni, ba wani aljanu wallahi iskanci ne."

Cikin rad'a tace "Amma dai kinsan zai iya ko?"

Tunawa tayi da abinda ya faru jiya sai kawai tace "Gaskiya kuma."

Turata Hajia tayi tace "Yi sauri to ce ya hak'ura ya dawo zan aura masa ke."

Hararan Hajia tayi tace "Karku sa haukansa a kanku mana."

Da sauri ta fita daga d'akin inda Amar ya kalli Hajia yace "Da zaku ji tawa Hajia sai nace ku aurar dasu, a yanda na fahimta duka suna son junansu."

Murmushi Hajia tayi tace "Ba zasu yarda cikin sauk'i ba, amma zan musu na babba da yaro, in sun san wata ai basu san wata ba."

Husseina ma dariya tayi tace "Gaskiya kam, musamman ma Hamna dai tafi taurin kai, amma shi na ga kamar k'uli yake duk inda ya fad'i gaba ne."

Dariya Junaid yayi yace "Kai shi fa babu ruwansa, anya ma kuwa zai iya soyayya?"

Zeituna da tunda suka gaishe da Amar bata sake cewa komai ba sai yanzu ne tace "Ai kuwa idan ya tashi yi zai baka mamaki, dan soyayya ma sai tafi wahalar dashi fiye da tunaninka."

Kallonta yayi yana dariya yace "Tanti Ammar kuwa zai bari soyayya ta bashi wahala, ba fa zai iya rarrashi ko lallab'a ba bare kalaman soyayya."

Amar ma dariya yayi yace "Ai daya fara ma zai ce ke dan ubanki dan kinga ina lallab'a ki."

Ihun Hamna suka ji yasa suka dakatar da dariyarsu suka fita da sauri sai Amar kad'ai ke zaune yana girgiza kai, ko da suka fito a farfajiyar suka same su yayi k'arfa k'arfa ya shiga har d'akin mai gadi ya d'auko labceciyar wuk'arsa ko kuma takobi, Hamna ce tace mai gadi ya rufe k'ofa shine fa ya d'aga takobin yace bari ya fara ta kan mai gadin, dalilin kuwarta kenan, cikin tashin hankali da son kwantar da tarzomar kowa ya shiga bashi baki, anan Hajia tace "To kai da yanzu muke maganar aurenku kuma kana so ka shiga gidan yari, kasan dai ba zan aura maka jikata bayan ka fito daga gidan nan ba ko?"

Husseina ce tace "Nima ban goyi da baya ba gaskiya, dan wata rana yar tamu zai kashe."

Cikin nutsuwa Zeituna tace "Yah Ammar, ko ba komai dan Allah kayi tunanin yaranka mana, ko so kake ka mayar dasu marayu gaba da baya? Mahaifiyarsu ma Allah ya jikanta da rahama ba zata so ba hakan ba, ko ka manta ka tab'a fad'a min bata son rigimar da kake yi."

Mik'awa mai gadi takobin yayi yace "Shikenan kun kashe wannan fitina, amma ku sani ban muku alk'awarin cewa idan na ganshi ba zan murd'e wuyan tsinanne ba."

Kallon kallo suka shigayi suna ma kansu tambayar wannan ai shine an kashe maciji ba'a sare kansa ba, can kuma sai suka ji yace "Shiit, to ai kuma banga fuskarsa ba."

Murmushi kowa ya saki na jin dad'i sai kuma ya kalli Hamna wacce tuni ta shiga rarraba ido dan tasan ba shakka zai koma kanta yace "Munafuka ke ai kin san shi, dan haka tare zamu fara yawo yanzu har sai kin nuna min shi."

Hararanshi tayi tace "Saboda banda aikin yi? Ko kuma saboda kai na ya zare?"

Da sauri Hajia tace "To kai yanzu ka yarda kayi ta yawo da matarka a gari kowa na kallo?"

Kallon Hajia yayi yana murmushi yace "Mutane ai ba zasuyi kyau ba babu ido."

"Kamar ya?" Cewar Junaid, kallonshi yayi yace "Idan na fara k'wak'ule maka ido zaka fahimta."

Dariya yayi yana matsawa daga kusan shi, ta gabanta yabi ya shafi kumatunta yana fad'in "Allah ya gafarta miki duniyata, har nayi kewarta wallahi, da yanzu tana nan tana kuka tana cewa dan Allah yah Ammar ka tausaya min, karka fita ka zauna a gida, ni ka dake ni ma indai zaka huce."

Da kallo su dai suka bishi har ya shige b'angarenshi, girgiza kai Hjia tayi tace "Allah ka shirya mana bawan nan naka, wannan idan muka k'ara samun wani kamar shi zamu mutu da ranmu." Dariya kowa yayi suka shiga ciki suna sauke ajiyar zuciya.

*Da safe* ko da ya tashi da abun ya tashi a ranshi, sai yanzu ne yake asalin jin haushin abun sosai, ya zage shi ya zage abar son shi, a hakan ma wai bayan yasa an daddaka d'an uwanshi, a gaskiya ya gama shawowa dashi ba kad'an ba, wai shi ya kira da mai k'walwar kifi kuma dak'ik'i, shiryawa yayi ya fita bai tsaya ko ina ba sai alimentation, kifi ya siyo kifin ma babba ya kamo hanya ya dawo gida.

Cikin madafa ya shiga dashi su Zeituna na ta k'ok'arin had'a abin kari, da kanshi ya d'auki babban faranti ya juye shi ciki ya d'auki wuk'a, suna kallon ikon Allah su dai ya cire kanshi tare da bud'e cikinshi, kwatta kwatta ya dinga k'arewa kan kifin kallo, basu ankara ba suka ji ya jefa wuk'ar ta bigi tagar dake kallon bayan gidan yana fad'in "Kaji haushi Ammar, ya had'aka da kifi kuma babu abinda kayi."

Juyawa yayi zai fita ya ga duk suna kallonshi, nuna musu kifin yayi yace "Ku je ku duba kuga k'walwar tashi sai kuji dad'i tunda ya kamanta ni dashi." A hassale ya fita rai b'ace ya bar gidan gaba d'aya.

*Tunda safe* lieutenant yaje dan su tafi, k'in fitowa tayi da farko amma tanti Ardayi tace ba za ayi wannan da ita ba, hannunta ta kamo ta damk'awa lieutenant sannan tace "To Allah ya kiyaye gaba, Allah ya kaiku lafiya sannan aci gaba da hak'uri."

Saida ya duk'a har k'asa yace "Nagode Hajia, Allah ya k'ara girma da d'aukaka."

Ko da suka fito waje ta fincike hannunta ta tafi da sauri ta shiga ta zauna inda dreba ya bud'e mata, rumgume hannaye tayi sai had'e rai take har suka d'auki hanya, babu wanda yace ma wani uffan har sukayi doguwar tafiya, lokaci lokaci ya kan kalleta sai yayi murmushi ya juya shima, wai hushi take bayan ita ce mai laifi, saida sukayi doguwar tafiya suka tsaya kan hanya wata k'aramar shago ya kalleta yace "In akwai abinda kike so ki fad'a min?"

Shiru tayi kamar ba taji ba saida ya sake maimaitawa tace "Bana buk'atar komai."

Kallonta yayi sannan ya kalli dreba yace "Mu tafi kawai."

Suna hanya Hadiza ta kirata sosai suka gaisa kamar yanda suka saba kafin daga bisani suyi sallama, ko da yaji yasan da wa take magana dan haka ba tare daya kalleta ba yace "Mutuniyar kirki ce, dukansu sun yafe laifin da aka musu."

Ita ma ba tare data kalleshi ba tace "Uwa ce ita, dole ta fahimci abinda yanda ya kamata."

Murmushi yayi ya lumshe idonshi, shima fa yanzu baya jin haushinta kan abinda tayi, irin dai kawai shi namiji ne ba zai sauko da wuri ba, to kuma sai ita ma Ummyn ta hau sama, dan tun daga maganar nan bata k'ara cewa komai ba har suka isa garinsu.


Hajia da kanta ta kira Hadiza ta sanar da ita maganar nan fa babu fashi, kawai su ma yaransu addu'a ta alkairi, haka ma Gambo ta kirashi ta fad'a mishi ya kuma ce wuk'a da nama na hannunta duk yanda tayi su addu'a da kuma yanda take so ne nasu, da kuma su Ummy suka dawo da dare take sanar dasu, duka dai kowa farin ciki ya nuna, amma da Ummy ta samu Hamna da maganar saita nuna ita fa bata so, duk k'ok'arin Ummy na son fahimtar da ita ta dage kan ita bata son auren Ammar, ba wai ba zata iya aurenshi bane kasancewarshi tsohon mijin yer uwarta yasa ba zata iya zama dashi ba ita, k'arshe dai haka Ummy ta rabu da ita dan karta takura ta har ta amince ba da son ranta ba.

*Da sauri*

*Abu* kamar da wasa sai magana ta girmama inda Hajia tace mishi za'a saka musu rana, amma fa duk abinda yasan ya ma Amna sanda zai aureta ita ma saiya mata shi, bai musa ba yace ya ji ya gani shi ai yaga abinda ya gani kuma yaji abinda yaji a na farkon ma, dan haka ribarshi ce bata wani ba.

Tana ji sama sama aka saka ranar kawo kayan, haka duk take kallonsu da wutsiyar ido da gari ya waye taga suna shirin tarban bak'i, dan wannan karan tunda abun ya sauya daga dangin lieutenant zuwa na Ummy ga kuma abokan arzik'i da dangin Hadiza duk sun hallara, kamar yau ake d'aurin auren saboda yanda ake ta kayaniya ta ko ina.

Da yamma aka shiga shigo da akwatina, tunda taji bud'a gabanta ya shiga fad'uwa tana tambayar kanta wai dama da gaske suke? Ammar? Ita? Lallai za'a mutu, tana sama ita dai tana jin gidan kamar zai tsage, a sama sama take jiyo maganganun mutane inda suke fad'in "Lallai wani hanin ga Allah baiwa ne, wani jinkirin kuma alkairi ne."

Saida aka ci aka sud'e an kawo ashirin ta arzik'i an koma da arba'in ta arzik'i, dan Hajia ta bud'e bakin jakarta ta zazzagawa kud'i rashin mutumci, a cewarta *auren sabon shalelenta ne* sannan ba k'arya k'ok'arinshi ya birgeta duk da dai tasan kud'i sun sake zaunawa yanzu, amma shima ya rintse ido sosai wajen kashe yayan banki.

Cikin k'ank'anin lokaci Hamna ta fara ganin statu d'in yan uwa har sun manna hotonta dana Ammar da kayan da kud'i da goro, statu d'in Sayyada (gaisuwa gare ki, sannunki da k'ok'ari da juriyar bayar da labarin yan uwan nan naki, wallahi kina k'ok'ari dasu😎 amma dan Allah karki fad'a ma cousine d'inki Hamna), d'aya hoton akwatina ne har goma ras an jerasu wasu na bin wasu, sai hoto na gaba inda aka bud'e dukansu kowa taf take da kaya har suna amai, sai na gaba d'aurin goro har guda hud'u da kud'i zube kan carpet yan jaka goma goma na million biyu, sai wata malet daban mai d'auke da tanfatsetsiyar sark'ar zinariya k'irar Agadez babu algus a cikin tare da awarwaro, wacce ita kad'ai ma kud'inta sun ishi mai rai rayuwa.

Ba tace bata ji dad'i ba gaskiya, dan saida ta murmusa ma amma bata san na miye tayi ba, amma daga nan ta shiga tunanin yanda zasu yi rayuwa da mutumin nan, a gaskiya ba zata iya rayuwarshi ba ta sani, bata sani ba waye zai wahalar da wani cikin ita ko shi, gashi bata da ta cewa yanzu tunda sun riga da sun gama magana ba zata kunyata su ba, idan kuma iska ne jikinta dake hanata aure, to ta sani shi zai dakatar da auren inhar lokacin aurenta baiyi ba.

Washe gari tana duba sak'onni WhatsApp d'inta ta samu sak'on Amie wacce rabonta da ita har ta manta, sak'o ne na neman tijara gajera kamar haka _"Burinki ya cika tunda gashi zaki auri mijin da yer uwarki ta bari bayan ta mutu."_

Ji tayi ba zata hak'ura ba ta maida mata da _"Na d'auka kin jima da fahimtar bana mu'amula da munafiki, amma bansan wace uwar kike nema tare dani ba."_

_"Ba ko d'aya, sai dai har yanzu ina tausaya ma yar uwarki, sannan da kike cewa baki zama da munafiki, ni ya kamata na fad'i haka, ko ke baki lura dana bar kulaki ba tunda nasan wacece ke ba."_

_"To kenan meya kaiki yi min magana kenan?"_

_"Dan na tayaki murna."_

Cewar Hamna _"Na ko gode."_

_"Mtsssss, anji haushin duniya, ki rasa wacce zaki ci amanar sai yar uwarki."_

Fita harkarta kawai tayi dan a ganinta ba zata b'ata lokaci kanta ba, sak'on Sayyada ta shiga wacce ke tambayarta ankon da zata fiddo musu, dariya kawai ta mata ita ma ta share ta, dan haka ta turo mata da "Karki d'aukeni yar iska mana Hamna, zan zo gidan da kaina naje na fito da anko."

Maida mata tayi da _"Hakan shi yafi, amma duk abinda zakuyi tsakaninku ne ni bana ciki."_

Dariya ta mata ita ma tace _"Zaki sauko ne daga inda kika hau wallahi."_

_"Babu abinda zai sauko dani."_

Dariya ta sake mata tace _"Ai kuwa d'an uwana zai sauko dake da k'arfin cin tuwo."_

Maida mata tayi da _"Ke dashi duk baku da aikin yi."_

_"Ke ma zaki samu aikin yi idan aka d'aura, dan tunanin d'an uwana ma kad'ai ya ishe ki."_

_"😑."_ Shine abinda ta tura mata.

A safiyar aka raba goro wani kamar zaiyi wanka dashi, sam kowa ya goyi da bayan a saka k'ank'anin lokaci, hutu aka saka na babbar sallah da za ayi na yan makaranta wanda duka *sati uku* ne ya rage, ai sai Ummy ta aje maganar aiki gefe ta fara shiga da fita tana gyara yar tilon yarta data rage mata mace, duk abinda ta wa margayiya shi take mata yanzun har da k'ari na sabbin sirrika, ita kanta Hamna wani abun in tasha sai jikinta yayi sanyi, wani in tasha tsikar jikinta ce zata dinga tashi, wani kuwa sai taji jikinta har rawa yake, turaren da take sawa a ruwa wurin wanka har gadonta ya kamu da k'amshin shi ma, ta samu gyaran fata tayi luwai luwai abinta tayi masara shar da ita, kullum kuwa tana sama d'akinta bata ganin ko falon Hajia bare rana, har yanzu kuma basu had'u da jarabun nata ba dan ba d'akin yake zuwa ba, dan danan kuwa sai gashi an gama shirye shiryen sallah an gama.

_Zuma_
Idon zakara_
_Kanunfari_
_Garin rud'i_

Ka had'esu ka sha da nono ko madara.

_Minanas_
_Hakk'in daka_
_Cukui_
_Zuma_

Saika had'esu kana sha da madarar shanu d'anya

_Kankana_
_Gwanda_
_Abarba_
_Pomme (Apple)_
_Zuma_
_Madara peak_

Kayi jus na su kana sha.

_Habba cokali 2_
_Garin rid'i cokali 3_
_Garin raihan cokali 4_
_Yayan zogale yanda kake buk'ata_

Ka zuba cikin dahuwar tantabaru mace da namiji.

_Dabino_
_Nonon rak'umi_
_Hulba_
_Ayaba_
_Abarba_
_Zuma_

Ka tafasa nonon rak'umin idan ya huce saika juye shi cikin markad'add'sn dabino da ayaba da abarba ka zuba garin hulba kasha.


*Kwana uku* daya rage kowace rana da shagalin dasu Sayyada suka gwangwaza, su da abokan Ammar sunyi shagali sosai ba kama hannun yaro, Hamna kam mulkinta take buga musu son ranta, har kamu akayi cikin gidan nan amma babu wanda ya ga k'afar amarya, anyi anyi ta shirya sai ma ta fashe da kuka dole aka k'yaleta, sai nan d'aki suka mata wanka turare, Ammar kam ko a jikinshi saida yaje gaban iyaye ya kwashi shokinshi ya duk'a suka fesa masa turare kafin ya bar wurin, wannan karan ma gabjejen sa ya aiko dashi ayi girkin biki tare da jus kamar za ayi wanka dashi.

*Ranassss*

Ya baje cikin shigar fararen kaya, lieutenant colonel da Gambo da Labaran duk shigar kala d'aya ce, su Amar Jibril da sauran dangi ma matasa kamarsu duk suna cikin fararen kaya, to anko ne da aka sa kowa yayi dan dole ko bai shirya ba, anan lieutenant ya bayar da auren yarsa inda Labaran ya karb'a wa d'ansaπŸ˜‚ (kune gayyar tsi...), daga k'arshe dai an d'aura auren *Hamna Harouna Suleymane Gaga* da *Ammar Hassan Suleymane Gaga* akan sadaki jaka hamsin mafi k'arancin dan albarkar auren.

*Yanzu ciwon kaina zai k'aru ku taimaka min da panadol da paracΓ©tamol da doliprane a kusa.*


*Alhamdulillah*
04/11/2020 Γ  14:39 - Ummulkhairi: πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨
*BADAK'ALA*
πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨

*Labarin Gaske*

*NA*

_SAMIRA HAROUNA_

*Litattafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._

*SADAUKARWA GA*

πŸ‘¨β€πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘¦ _*AHALI NA*_πŸ‘¨β€πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘¦

πŸ’«βœ¨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🀝

β˜† *[ T.M.N.A]* β˜† πŸ“–πŸ–ŠοΈ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_

_70_



*Biki yayi biki* ta bakin wani mawak'i, ba kid'a ba wak'a amma fa holewa ake, b'angarenshi ya sake tabka mishi gyara na rashin mutumci, haka kuma yana can ana gyara masa gidansa dan yace wannan ita ce abokiyar gwabzawa sai sun matsa daga kusan manya karsu kashe su basu shirya ba. Ita kanta Hamna k'awayenta sun mata bajinta sosai, dan har daga Niamey da Katsina wasu sun zo aurenta, taji dad'i sosai na ganinsu a kusa da ita a wannan lokaci.

Ko da magriba tayi Ummy ta tsaya tsayin daka wajen gyara amaryarta kuma surukarta, wata mahaukaciyar doguwar riga ta tsadadden tissue aka saka mata, yaji d'inki sosai mai d'aukar ido da d'aukar hankali, tun daga sama zuwa hannaye har gwiwa a matse yake, amma daga k'asa sai aka bud'e sosai yayi tsatsaye har yana jan k'asa, kwalliya ta d'auka daga wajen wata k'awarta ta ban mamaki, kwalliya ce daidai da fuskarta inda aka d'ora komai kan muhallinsa, d'aurin d'an kwali kam kamar ba hannu ne yayi aikin ba, dama duk wani abin da zata saka saida Ummy ta turare shi har da pant da bras d'inta, sannan ita ma aka sa ta zauna kan kujerar turaren bayan an turare mata jiki, abubuwan da Ummy ta k'ara bata tasha ta ci taji tana neman yin amai, tana daf da fashewa da kuka tana fad'in "Wallahi Ummy amai zanyi, ya ishe ni haka dan Allah."

Da sauri mai kwalliyar tace "Rufa min asiri Hamna karki zubo da hawaye a idon nan."

Hararanta tayi tace "Dallah kwalliyar me?"

Karb'a Ummy tayi tace "Shikenan to barshi haka, ai muna tare dake a gidan."

Ummy zata fita daga d'akin wayarta tayi k'ara, ko da ta d'auka tace "Ango ya akayi?"

Daga inda yake yace "Ummy kun shirya? Mota fa na nan tafe d'aukar kankana."

Saida ta kalli Hamna dake ta had'e rai k'awarta na cewa ta dinga murmushi dan Allah sannan tace "Me ye na sauri Ammar? Kuma nan da can d'in zata shiga mota? To ai ko hannu aka sa sai a tura motar k'ofar gidan."

"A'a Ummy sarauniya ce yau, bari mota zata kaita."

"To shikenan." Ummy ta fad'a dan abar canzen, ta d'auka mota d'aya ce yake nufi da zata d'auki amaryar, amma abun mamaki da firgita tunanin mai rai sai jininin motoci suka ji, sanda aka fito ne suka ganewa kansu sarautar Allah, kai Umy ita dai a ganinta motocin nan bana abokanshi bane kad'ai kamar harda hayarsu akayi, mota ta bawa guda arba'in baya ta kusa kaiwa hamsin, to wace tsiyar zasuyi da su, in suka shiga ina za'a kaisu, to wata motar ma yanda ta zo haka ta juya ta koma bata d'auki ko sauro ba bare mutum.

Bakin duniya, da suka kwashi matan mutane gudu na idon duniya suka dinga yi dasu, aa fa gudun ma a cikin tsari suke yin shi, dan babu motar data fita daga layin da suke, saida suka lula suka kai k'uryar ali d'an sofo sannan suka kutsi hanyar da saida ta sada su da zarya ta k'arshen k'ashe-sheshe, yawo kawai sukayi mutune tun ana jin dadi su dai har wani ya fara k'orafi saboda dare ya k'ara yi, sai lokacin kad'ai suka koma aka aje amarya aka shigar da ita gidan ta.

Iyaye duk kanta suka taru inda suke mata nasiha kan hak'uri, saida kowa ya gama na shi Hajia da Husseina su dai suka fad'a mata ta zama mai d'auke kai daga lamarin bawan Allah nan, wannan taurin kai da fad'a masa magana kai tsaye ta kiyaye, tayi kamar yer uwarta har ta koma ga Allah ba'a tab'a jin ko sautin muryarsu ba da sunan tashin hankali, ita dai sauraronsu kawai take, amma ba zata iya abinda Amna tayi ba, wacce ta fad'a mata idan wani ya b'ata mishi rai saiya huce kanta ta hanyar darzata kan gado ko kuma ya mata wanka da ruwan sanyi ko sata cin abincin da batayi niyya ba, to ita yaushe zata iya da kwatirarsa? Ai ya kasheta ko ita ta kashe shi ne kawai.

A sannu sannu aka watse aka barta ita kadai, zaune kan gado tana k'arewa d'akin kallo, saida ta gama tas sannan ta mayar da fuskarta cikin babban mayafinta tana kallon hannayenta masu ban lalle, Ammar? Ammar? Mahaukaci ne fa suka had'ata dashi.

*Uwar Lalla kinji fa?*

*Yana* saman hanya tare da Amar na tuk'i sai su Junaid a baya lieutenant ya kira shi, d'auka yayi lieutenant yace "Kana ina Ammar?"

"Abba ina kan hanya."

Cikin d'an jin kunya yace "Ka siye kaza ne?"

Murmushi yayi yace "Abba duk angon dake son jin dad'i dolenshi ai ya siyo kaza."

Su Amar kallonshi sukayi sai Abba da yace "To ka siyo guda biyu ina son d'aya nima."

Tafin hannu yasa ya rufe fuska wai kunya yana fad'in "Lah Abba na wallahi ka bani kunya, kai ma kaza kake so? Kenan dai uwata zata mana k'ane."

Had'e fuska yayi yace "Kai bana son iskanci, ita kad'ai ce mai k'wan haihuwa? To da uwarka nake ni."

Ido ya zaro cike da shak'iyanci yace "Kai Abba na Ummy fa, kayi hak'uri dan Allah kaje wajen uwa Zeitu."

"Ammar." Ya fad'a cikin muryar karsashi, a hankali yace "Na'am Abba."

"To ka siyo ka kawo min, kuma dan ubanka da kai zamu je siyan bakin uwarta ka tunda kai ka zigeta har yanzu bata kula ni."

Tintsirewa yayi da dariya yace "Abba na karka damu, ni d'in nan nine na rabaku kuma ni zan had'a ku, bari na siyo maka kaji manya guda uku, d'aya ta yau d'aya ta gobe d'aya ta jibi."

Girgiza kai lieutenant yayi kawai ya kashe wayar, shi kam gyara zama yayi kamar mai shirin bacci yana fad'in "Abba ba dan karka karya min uwa ba ma ai da saina saka maka magani a kazar nan."

Dariya suka saka inda Junaid yace "D'an iska dai baiji dad'i ba wallahi."

"Inji uban wa?" Ya fad'a idonshi a rufe, Jibril ne yace "Inji shi mana."

Wata k'arar ya fitar a bakinshi irin a banza kenan, Amar yace ma "Muje a siyowa Abba kaji, shi ma yau dad'i yake so yaji."

Kallonshi Amar yayi yace "Yanzu kai banda abunka ina Hassan ina wannan abu na yara? Ai sai ku masu tafasashen jini."

Bud'a ido yayi ya kalleshi sama da k'asa yace "Ko yanzu ka had'ashi da yarinya Allah zaka yi mamakin sakamakon da zai haifar."

Su dai dariya suke har suka isa wajen maduguπŸ˜‹, tik'a tik'an kaji ya siya kafin suka wuce gida, da shigarsu suka samu lieutenant a waje, wuyan rigarshi ya shak'a yace "Sai mun je ka bata hak'uri, tunda ka hure mata kunne yanzu gaisuwarma sai dai kaji ta wani ce, ina kwana."

Dariya yayi yace "Abba sake ni to ai ba guduwa zanyi ba."

Sakinshi yayi suka shiga ciki gidan ya d'an fara yin shiru alamar kowa ya tafi bawa makwancinshi hakk'inshi, kai tsaye d'akin Ummy suka shige a tare.

Ja sukayi suka tsaya ganin Ummy ta gama saka doguwar rigar bacci har k'asa tana d'aure gashinta da k'aramin mad'auri, kallonshi Ammar yayi yana dariya yace "Abba da alama ita ma hak'uri zaka bata, to gashi ni na tafi kafin na makance."

Juyawa yayi yana ajiye leda d'aya lieutenant ya jawoshi, juyowa tayi ta kallesu tace "Ya zaku shigo haka babu sallama?"

Juyawa tayi tana fad'in "Ko da yake ai kamar uba kamar d'ansa, ba mamaki kam."

K'arasa shiga sukayi inda lieutenant ke fad'in "To miye a ciki dan bamuyi sallama ba, kai da kaya ai duk mallakar wuya ne."

Kallonshi tayi fuska a had'e tace "Amma ai shi yaron mamallakina ne, ba shine ya mallake ni ba."

Kallon juna sukayi da Ammar yace "Wannan shalelen Hajia ko bayan raina fa shi zai rik'eki."

Ba alamar wasa tace "Shiyasa dama ka k'i bani takardata saboda kaga ka kusa mutuwa, kana so dole sai nayi maka wankan takaba."

Gaba d'aya suka juya suka kalleshi yana dariya, zaune Ummy tayi bakin gadon tana kallonshi, saida ya gaji da kanshi yace "Ummy Abba na kike wa fatan mutuwa? To ai bai tsufa ba."

Da hannu ta nuna masa tace "Ka duba da kyau ka gani, kwana nawa ne ya rage masa yayi ritaya (retraite)?"

Murmushi yayi yace "Amma Ummy ai a wajen aiki ne zaiyi ritaya, a gida kuwa yana nan da k'ark'onshi."

Lieutenant ta kalla tana d'an jujjuya baki tace "Zaku iya fita idan kun gama abinda ya kawo ku."

Kallon juna suka sake yi sai yayi laushi sosai yace "Abba ni zan tafi fatan nasara, mata uku
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment