Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

Allah kayi hak'uri ka gafarce ni."

Fuska a had'e yace "Ina iyayenka suke?"

Ba tare daya tsagaita kukan ba yace "Ba yan garin nan bane, suna zinder ne, almajiranci suka kawo ni."

A lokacin ne su Junaid suka fito sun gama tattaunawa, Amar ne yayi saurin ciro wayarshi ya duba mai kira, saida gabanshi ya fad'i ganin Hajia ce, Junaid daya fahimta yace "Karka d'auka tunda yanzu zamu koma, gwara musha giyar ta dubu sai ayi kankat."

Wayar ya kashe tare da jefata aljihu a lokacin ji sukayi kawai Ammar yace "Shiga mota zan mayar da kai gidanku."

Pik'i-pik'i yayi dan shi dai bai bai yarda gidansu zai kaishi ba, amma tsoro yasa ya mik'e yana d'an rakub'ewa da d'ar-d'ar har ya shiga inda su Junaid suke, saida suka d'auki hanya Amar ya tambayi Jibril meya faru? Jibril da yake tunanin wai Ammar wane irin mutum ne? Anya wannan ba Allah ne ya dubesu ba ya k'i bashi aikin sojan da yake so, girgiza kai yayi yace "Kai dai abar kaza cikin gashinta kawai."

Junaid ne yayi dariya a harshen fransanci yace "Dan Allah ka bamu musha mu ma, meya faru?"

Nan Jibril ya canza harshe shima ya fad'a musu, ba jimawa kuma sun iso gidansu kaka, ko cikin gidan basu shiga ba sukayi alwala suka shiga masallacin dake kusa da su sukayi sallah, nan kaka tace su shigo su ci abinci, basu mata musu ba suka shiga ciki suka zauna kan tabarma, shinkafa ce da miyar taushe (tauhe ๐Ÿ˜‚) aka kawo musu, sai ruwan sanyi a gafe suna korawa, duk da Ammar sai wani had'e fuska yake amma har ranshi miyar ta birge shi, tare da almajirin nan suka ci har suka ida sukayi hamdala, nan suka musu sallama suka tafi tare da cewa sai sun dawo, daga nan suka sake d'aukar hanyar komawa gida.

*Gidan roumji*

Suna sauka suka fahimci babu motar yaransu samari wanda suke jinsu kamar wasu garkuwarsu ne idan suna tare da su, mamaki suke ko lafiya, amma sai Labaran yace watak'ila ko motarsu ta samu matsala dan k'arfen nasara babu tabbas, a haka aka bar maganar aka shiga abinda ya tara kowa, har akayi addu'a aka gama aka kwashe awa d'aya babu su babu labari, nan aka fara kiran wayoyinsu amma a lokacin suna hanya akwai matsalar hanyar sadarwar yasa kiran ma baya shiga, wannan abu ya basu mamaki hankali kuma ya fara tashi, lieutenant da ranshi ya b'ace ne yace kar wanda ya sake kiransu, ai babu yaro a cikinsu, kuma da idonshi ya ga motarsu biye dasu har cikin garin nan, dan haka ba musakai ne ba zasu iya k'arasowa k'asa ai, idan kuma hakan ya gagara ai zasu iya kiransu su fad'a musu, dan haka yace su k'yalesu kawai su zuba musu ido, amma basu bari Hajia taji me ake ciki ba, duk da kowa ya bar maganar a zahirance amma haihuwa ta shiga tsakaninsu da b'acin ransu, kowa da abinda yake tunani a ranshi a game da nashi yaron da sauran yaran, a hakane fa har lokacin sallah azahar yayi, lokacin ne Hajia tace ayi haramar tafiya gida dan ita ta gaji da zaman k'auyen nan, a lokacin taji abinda ke wakana, kafin tace komai ne ta kira lambar shalele amma bai d'aga ba, tana sake aika wani kiran kuma sai aka ce wayar kashe, lokacin ne ta rufe ido ta dinga surfa masifa a cikin gidan har akayi sallah hankali ba kwance ba, kuma abinda yafi damun lieutenant da Sa'ada shine cewa da take wannan d'an banzan Ammar d'in ne ya d'auke mata shalele, ita bata ma san ina ya kaishi ba, inda Zeinabu ta tabbatar lallai Hajia bata k'aunar nasu yayan saina Sa'ada suma kuma d'a d'aya take so, Soueiba kuma ta k'ara yarda bata son duk wani jini daya fito daga jikin sarakuwarta Husseina, Alhaji kuma yana ji ya zuba mata ido dan in yace yayi magana zata mishi rashin mutumci ne cikin mutane, dan haka kawai yake kallonta har tayi ta gama, a haka dai tasa suka sake dawowa gida dan ganin meke faruwa.

Tashin hankali, labarin da suka samu a gida ma shine ai tare kuka fita dasu, cikin masifa Hajia tace "Kuma basu dawo ba?"

"Basu dawo ba Hajia." Cewar Nana mai aiki, cire gyalenta tayi da jakarta ta aje ta zauna kujerar falo tana rau da kanta, duk wani motsin Sa'ada saita kalleta, hakan yasa ta kasa motsawa daga inda take saboda gudun karta zargeta, sallah la'asar kad'ai tasa kowa ya gusa daga falon dan gabatar da sallah, haka gidan ya ci gaba da zama shiru Hajia kuma na zaune a falo ta kasa ta tsare sai taga shigowarsu, inda Alhaji ke zaune a bayan gidan iskan 'ya'yan itatuwa na kad'a mishi.

*Saida* wannan yaron ya nuna mishi har k'ofar gidansu saidai kamar suna k'uryar gari ne, yaron na fitowa Ammar ya ciro lalitarshi ya fito da kud'i, jaka goma goma guda uku ya bashi yace "Wannan kayi sana'a dashi, idan kuma na sake ganinka a irin wannan banzar rayuwar wallahi saina lahira yafi ka jin dad'i, kasan dai da aljanuna zasu iya nuna min duk inda kake ko?"

Da sauri yaron ya dinga girgiza kai alamar eh kamar k'adangare, jinjina kai shima yayi alamar ah to ka ma shiga hankalinka kafin ya sake had'e fuska yace "Idan kuma ka shiga gidanku ka ce da iyayenka shugaban *sojojin niger* (general) ne ya dawo da kai yace ka zauna gida, idan har suka sake mayar da kai..."

Saida ya kalli gabanshi ya d'an cije leb'e ya kalli yaron yace "Ka fad'awa mahaifinka da kaina zan sauke mishi kafad'a ta hannun hagu."

Da sauri yaron yace "Babana ya rasu, nan daga mamata ne sai k'annan Baba na."

Zaro mishi ido yayi cikin d'aga murya yace "To su k'annan baban na ka basu da kafad'a ne?"

"Suna da." Ya fad'a a muryar kuka, wani jinjina kai yayi alamar jin dad'i yace "To ka fad'a musu haka."

Yana fad'a ya d'aga gilashin motar ya fizgeta da k'arfi ya tayar da k'ura suka koma baya dan su hau titi, yaron da baki sake saida ya ga b'acewar motar ya juya gida, tunaninshi wannan ba wai aljanu ne dashi ba, shi da kanshi ne aljanin, amma inba haka ba taya kawai zai d'auko ni ya dawo dani? Yanzu karatun nawa fa da nake duk da yunwa bata vari na ma fahimta? Ya malaminmu zaiyi? Ya k'annan babana da kakata zasuyi idan suka ga na dawo? Zasu d'auka tserewata nayi ai tunda dama banso nayi nisa da uwata ba, da wannan tunani barkatai ya shiga cikin gidan, duk abinda aka fad'a mishi ya fad'a sai dai bai fad'i gaskiyar dalilin rabuwarsu ba, gidan tunda suka ji yace shugaban sojoji ma suka sha jinin jikinsu, kakar yaron wacce ta haifi babansu ce tace ma autan ta ai a kwaso duk yaran dake sauran garuruwa su zo nan suyi karatun, dama can yawan gidan ne yasa suka rage ta hanyar turasu almajiranci.

Su Amar banda dariya babu abinda suke, amma Ammar kamar baisan sunayi ba sai tuk'i da yake, a *Ague* sukayi sallah magriba suka sake wucewa, wannan karan ba jimawa suka shigo cikin gari sai dai anata sallah isha'i saboda tsakanin lokacin dama ba wata tazara ake samu ba, sannan gashi Ammar ba wani gudu sosai yake ba da zai kawosu gida cikin k'ank'anin lokaci, suna kaiwa *immeuble Gago* ya taka birki ya juya yana kallonsu, Junaid dake gaba ne ya washe baki saboda hango mai gasa kaza da yayi ya kalli su Amar yace "Kai 'yan uwa, babban yaya fa kaji zai siya mana mu ci, kai Allah dai ya k'ara girma yayanmu."

Wani jan kallo Ammar ya mishi yace "To jikan kura, kazar uwar wa zan siya muku? Sai kace na d'auko karuwa a mota zan tsaya siyen nama a hanya?"

Jibril ne ya kece da dariya yace "Wato ita karuwa idan aka d'auko ta sai an siye nama?"

Ko kallonshi baiyi ba sai gani da sukayi ya bud'e ya fita ya zagaya mazaunin Junaid, da sauri Junaid ya fito ya dawo mazauninshi ya tayar da motar suka fara tafiya, cikin masifa Ammar ke fad'in "Shegu 'yan banza, ai dama zura muku ido nayi naga mai hankalin da zai iya karb'ar tuk'in nan a hanuna, ashe duk k'ananan marasa mutumci ne ku."

K'wafa yayi sai Amar da yace "Yi hak'uri yaya, ni wallahi in so na karb'a amma a raina kuma nace watak'ila dan kana babba ne shiyasa ka hutashe da yan uwanka ababen soyuwarka."

Wata ashar ce ya malmalo irin ta yan zamani yace "Na soya mata..."

Gyara zama yayi ya jingina tare da lumshe ido yace "Ku tanadi abinda zaku fad'awa tsofaffin can, dan ni nan banga abinda zai sani magana ba."

Kallon kallo suka fara, ai kuwa sai suka fara shiga k'irk'iro labarin da zasu fad'a a gida wanda zai dace da hankali, suna tsaka da haka Ammar da idonshi ke rufe yace "Ya kamata kusan cewa da Allah yana so ku zama sakarkaru to fa daya halliceku babu baki, akan me zaku musu k'arya? Duk cikinku akwai wanda zai tsireku ya rataye? Ko kuma akwai mai wutar da zai saka ku a ciki? Kunga, ban yarda na biku ba saida na tabbatar aikin alkairi muka je yi, amma kuna so ku mayar da kanku lusarai kamar ba maza ba, a hakane yanzu kuke so kuyi aure, to ya zakuyi da matan?"

Cikin turo baki irin na shagwab'a Junaid yace "Yanda kowa yake yi da su mana."

Tsaki Ammar yayi ya bud'e ido ya kalleshi yace "Shin ko kasan a cikin maza akwai mata-maza? Sannan akwai muna-maza, kamar yanda ke akwai mun rako maza duniya, to zaku kasance d'aya daga cikin ukun nan ne in kuka ci gaba da haka."

Amar ne yace "Ammar zafa mu baka mamaki wallahi, ai namiji zai amsa sunanshi ne a lokacin da yake iya ciyar da matarshi, yake mata sutura iya iyawarshi, yake kula da lafiyarta da addininta, sannan yake gamsar da ita a shinfid'a."

Murmushi yayi wanda Junaid dake gaba ne kad'ai ya gani kafin yace "To ko ita gamsarwar da kake magana a kai tana buk'atar zarra, sai ka zama namijin gaske kafin ka gamsar da yan matan yanzu, idan kuma ba haka ba wallahi kaine zaka wahala har ka zubar da hawaye, dan irin kayan da suke anfani dasu wajen gyara jikinsu sunfi k'arfin tunaninka."

Jibril ne ya d'an lek'o kai ya dafa kafad'ar Ammar yace "Babban yaya ince dai in zamuyi aure kai zaka zama malamin mu?"

Bige hannunshi yayi ya juyo a harzuk'e yace "Saboda d'an iska ne ni?"

Kwashewa sukayi da dariya, suna tsaka da dariya yace musu "Billahil-azeem duk wanda ya fad'a musu k'arya saina tona asiri, dan ni ba zan yarda ayi k'arya dani ba."

Da haka dai suka iso gida suka danna ham (๐Ÿ˜‚) mai gadi ya bud'e musu suka shiga, a wajen ajiye motoci suka paka ta su kafin suka fito cike da gajiya, cikin wani takon izza da k'asaita Ammar ya nufi b'angaren su, Junaid ne yace "Ammar ka zo mu fara shiga ciki dan Allah, ni nafi son ayita ta k'are."

Tsaye yayi ya juyo ya kalleshi yace "Kai ne uban tafiyar ai, ka fara shiga ciki ka fara d'aukar naka rabon, ni daga baya na shigo bayan nayi wanka."

Jibril ne yace "Amma dai da mun fara shiga a mana bala'in, in ya so daga baya ma huta gajiyar."

Rai had'e yace "Na ce wanka zanyi ko."

Amar daya d'an lek'a kusa da falon Hajia ne yace "Ka zo muje dan Allah, wallahi nasan mu suke jira dan ayi magana."

Juyawa yayi ya fara tafiya yana fad'in "To duk wanda ba zai iya hak'ura na fito daga wanka ba kuce su sameni a ban d'akin sai muyi maganar."

"Kana wankan?" Cewar Jibril yana zaro ido, ba tare daya juyo ba yace "To meye a ciki, su d'in iyayena, ku kuma yan uwana ne maza, hallitar iri d'aya ce, ko kun kalla babu abinda zaku ji a ranku, wannan tsohuwar ce ma kawai bana so ta ganni babu kaya, kallon data min ina yaro ma ya isa haka, taje ta kalli mijinta."

*Ma Sajida sai kin taimaka min da lema (para-pluie) wacce zan dinga kare wannan katob'arar fa, dan wani abun idan ya murguzo kasa duk'ewa nake.*

Lieutenant da yake son fita amma Hajia tace babu inda zashi sai yaran sun dawo taji daga inda suke, yana jin k'arar motar ya fito ya duba, ai kuwa a lokacin da Amma ke tafiya zai bud'e k'ofar b'angaren su suka ji yace "To ku wuce muke ciki."

Take suka fara rarraba ido suna kallon kallo, kamar wanda k'wai ya fashe ma a ciki haka suka fara tafiya, murmushi Amar yayi yace "Abba barka da dare."

Dak'uwa ๐Ÿ–๏ธ ya watso mishi tare da nuna musu hanya su wuce gaba, Ammar dake kallon abinda ke faruwa baida niyyar tahowa, lieutenant ne yace "To ubana, sai nayi magana ko?"

Wani farrrr yayi da ido kamar mace na son karb'ar kud'i hannun mai gida kafin ya taho ciki takun k'arfi, saida ya kawo daf dashi zai wuce lieutenant ya d'aga hannu da nufin bugunshi a k'eya, da sauri ya duk'e tare da ja baya ya d'ago yana kallonshi yace "Abba wai sau nawa zan fad'a maka ka daina sarar dukana a kai? Kayi karatu fa, ko dai ka manta abinda ka karanta ne a cikin aji game da abubuwan dake cikin kai?"

A hassale lieutenant yayi kanshi ya zura hannu zai shak'o wuyanshi ya sake zillewa, tsaye yayi yace "To wai yanzu dukana ne kake so kayi ko me? Kasan dai na wuce wannan matakin ko?"

Saida ya nuna shi da yatsa yace "Dan Allah ka zo nan ka gani idan ban dake ba, Ammar ni zaka raina ka mayar wani mahaukaci."

Saida yayi nesa dashi ya ya wuce ya nufi falon Hajia yana fad'in "So ne kawai yake a kafa min mugayen hak'ora, ya bini a guje ya fad'i shikenan ace na kashe ubana, haba, tsofi sai jaraba bakinsu ko ciwo baya yi."

Yana dosowa falon ya canza salon tafiya da yanayin fuska irin ba magana kuma ba wasa bare dariya, yana shiga ya samu su Junaid sunyi cirko cirko zaune a k'asa kowa kanshi k'asa, gefenshi ya kalla inda Ummy, Soueiba da Zeinabu suke zaune, sai gefe guda su Amna ne da Umaima ke ta latsar wayar amma banda Hamna dake shan kankana da cokali mai yatsu, "Wato dan raini a gaban yaran nan za'a musu fad'a? Kai ba zai yiwu ba gaskiya."

Kallonsu yake yana so su kalleshi ko zasu fahimci kallon amma rashin sa'a babu wacce ta kalle shi har kankanar ma, a hankali ya cire takalmi ya k'arasa kusansu Junaid, amma saboda iko sai yayi zaune akan kujera yana kallonsu su dake k'asa kamar sun zo d'aukar karatu, Ummy ya kalla wacce idonta ke kanshi kamar ta zundumo mishi zagi, kallon Husseina yayi dake zaune kujera d'aya da Labaran da kuma Alhaji, hannu ya d'aga musu ba alamar fara'a yace "Barkanku da dare."

Husseina dake ta doka uban murmushi ce ta amsa mishi da "Barka Ammar."

Hajia ya kalla wacce bata da niyyar magana har yanzu, a ranshi yake fad'in "Wannan indai ba shanye Alhaji kikayi ba me zaisa gashi zaune amma ke ce mai zartar da hukunci, Allah ya sawak'e miki."

Ganin har yanzu shiru yasa ya kalli mutanen d'akin "Idan an gama karatun saimu rufe da salatin annabi ko?"

Su Amar dake kusa dashi duk rik'e dariyarsu sukayi, hakan ya hassala Hajia ta mik'e tsaye da fad'in "Kaiiiii."

Yana jin haka saiya jingina a kujera ya d'ora hannunshi a matangalin kujera yana shafar k'ulun hallitar dake mak'ogwaronshi wanda bak'in gashi mai silb'i ya rufe shi, kallon yan k'asa tayi dan sunfi dama dama tace "Daga ina kuke?"

Shiru ne ya d'an ratsa wurin yayin da Junaid ke ganin ba zai yarda a d'ora musu laifi ba, dan haka ya d'ago ya kalleta yace "Daga Goure."

Yatsina fuska tayi ta kallesu da kyau tace "Me kuka je yi a Goure? Wa ma ya aike ku?"

Junaid dake jin wani sanyi na ratsa zuciyarsa babu fargaba yace "Munje sulhunta tsakanin Maryama ne da iyayenta, sannan na gabatar da kaina a matsayin mai son aurenta, kuma sun amince."

"Wacece hakanan kuma?" Hajia ta tambaya cike da rainin wayo, shiru ya d'anyi dan haka ta kalli Zeinabu dake kallon Junaid da mamaki tace "Ke kinsan wacece hakanan?"

Cike da ladabi tace "Umma ita ce yarinyar da yace yana..."

Bata bari ta k'arasa ba tace "Ku ce min karuwa, wai karuwa kake nufi? Neman aurenta kaje kenan ko me?"

Shiru dukansu sukayi, cikin taushin murya tace "Shalele, har da kai da nake ganin kamar kana da hankali? Ya zaka biye musu wajen yin wannan d'anyan aikin? Halan wani ne ya tilastaka?"

Ta fad'i hakane tana kallon Ammar da shima yana jin haka ya kalleta, dan yasan shi take nufi, d'auke idonshi yayi dan haka Amar yace "Babu wanda ya tilasta ni, kawai naga yan uwana zasu tafi ne ni kuma na tafi tare da su."

D'aga kai tayi sama cikin gadara tace "Hakan na nufin kenan kun girma? Kun isa ku yanke hukuncin daya shafi rayuwarku ba tare da sanin kowa ba, hakan na nufin zaku iya ji da al'amari komai girmanshi idan ya taso muku ba tare da shawarar ko da iyayenku ba, to da kyau, amma ku saurare ni kuji."

Fuskantarsu tayi da kyau tace "A gidan nan ba ayi ba ba kuma za ayi wanda zai taka min doka ba ya kwana lafiya, matuk'ar ina raye banga wanda ya isa a gidan ya dinga juya rayuwarshi yanda yake so ba, dan haka tunda kun nuna min zaku ja dani, ni kuma zan dakatar da al'amarin yanzun nan."

Juyawa tayi ta koma inda take ta zauna ta d'ora gwiwoyin hannunta a saman cinyarta kafin tace "Hutun makaranta da za'a bayar na kwana goma nan da sati uku, ku shirya mishi da kyau, dan aurenku za ayi."

Da sauri suka d'ago suka kalleta inda Ammar ya dakatar da shafar gemun da take yana mata kallon mai bisa ruwa, jinjina kai tayi da yake nuna tabbas babu fashi tare da d'orawa da " *Shalele* zaka auri 'yar uwarka *Umaima*, *Junaid* zaka auri 'yar uwarka *Hamna*, kai uban sarkin marasa kunya zan had'a ka da wacce baka isa kace ta maka laifi ba bare harka zalinceta ( *Ammar*), za'a d'aura aurenka da *Amna*."

Juyawa tayi ta kalli Jamila sannan ta kalli Jibril, ita dai badan tana so ba zata had'a tsatsonta dana Husseina, amma idan ba tayi ba yanzu tsohon na zai kawo mata cikas a lamarinta, dan haka tace "Kai kuma *Jibril* zaka auri Jamila, wannan shine hukunci na, da wani mai ja."

Ta fad'a tana kallon iyayen duka, amma cikinsu sai kowa ya girgiza kai harda arhar murmushi da suke mata ana fad'in ai duk gida ne dan haka abun farin ciki ne, da murmushin k'asaita tace "Ku tashi ku bani wuri."

Mik'ewa sukayi kamar babu lakka a jikinsu, amma Ammar ko niyyar tashi ma baiyi ba, sun fara tafiya tace "Shalele."

Juyowa yayi tace "Idan kayi wanka ka ci abinci ka same ni d'aki na."

"To." Kawai ya fad'a suka bar falon, kallon Ammar tayi tace "Ko saina tasheka ne kai kuma?"

Saida ya d'an harareta na wucen gadi kafin ya mik'e ita kuma tsaf ta gane hararenta yayi, dan haka ma tace "To ko da magana ne?"

Cikin takonshi na isa yace "Ke ma kisan ai idan da maganar zan fad'a, dan bana tashi da kwananniyar magana a baki na."

Hamna ce ta saki cokalin hannunta saboda wani abu da taji, juyowar da Hajia tayi ne tasa ta saurin d'aukar cokalin, mik'ewa tayi ta aje farantin kankanar ta fita farfajiyar gida, Amna kuma Inna lillahi kawai take maimaitawa, wai da gaske ita ce aka had'a da Ammar? Tab', lallai sunanta margayiya daga yau, to ita ta ina zata iya da auren Ammar? Mutumin da idan ya fad'a maka wata maganar sai kayi sati kana kuka, shine zatayi zaman aure dashi? Umaima kuma har cikin ranta zab'in ya mata, dan dama Amar na masifar birgeta, haka ma Jamila sam bata ji a ranta wai an tauye ta ba, sai dai ta d'auka zata fara shan bikin yayunta ne dan ita ce k'arama a duk cikinsu, to amma haka Allah ya so sai fatan alkairi kawai.

Suna shiga b'angaren su kowa wanka ya shiga cikin matuk'ar sanyin jiki, amma banda Ammar da shi sam baiji wani abun bak'in ciki ba, hasalima yace Amna dai ce ta shigo d'akin shi a matsayin mata, Allah yasa ta mata shirin da zata uya zama da shi, duk ranar daya samu wacce zuciyarshi ke *so* to ko a yau Amna ta zo gidan saiya fad'a kuma saiya aureta babu mai hanawa.


*WAIWAYE*
_(ADON TAFIYA)_

*Suley Hassan Gaga*
05/06/2020 ร  20:32 - Ummulkhairi: ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ
*BADAK'ALA*
๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ

*Labarin gaske*

*NA*

_SAMIRA HAROUNA_


*Litattafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._

*SADAUKARWA GA*

๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ _*AHALI NA*_๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ


_Allah ba dan mu ba ka yafe mana zunubanmu, Allah ba dan halayenmu ba ka gafarta mana kurakurenmu, Allah dan rahamarka ka jik'anmu ka mana gafara, *Astagfirullah wa atubu ilaikh*._

๐Ÿ‡ณ๐Ÿ‡ช *TAURARIN NIGER*
```(Tsintsiya madaurinki d'aya)```

_Bismillahir rahamanir rahim_

_10_


*Suley Hassan Gaga*

Haifaffen garin *Marad'i* dake jamhuriyar Niger, a wata unguwa da ake kira *d'an gulbi*, mahaifinshi Alhaji Hassan yana da mata biyu, ta farko ita ce *Rumanatu* wacce suke kira da Ramma, tana da 'ya'ya uku, babban shine *Innusa* (Yunus), sai k'anwar shi *Barira*, sai kuma k'aramar *Rahmatu*, sai matarshi ta biyu *Saratu* wacce ita ce mahaifiyar Suley da 'yan uwanshi mata 'yan biyu masu sunan *Hassana* da *Husseina*, iyalin Hassan Allah ya musu baiwar haihuwar yan biyu, hakan yasa a ahalin nasu suke da yan biyu masu yawa maza da mata, Ramma na da 'ya'ya uku namiji d'aya da mata biyu, sai dai kasancewarta shu'umar mace yasa ita ke juya gidan da mutanen cikin shi.

Hassan yana da tarin arzik'i kama daga shanu zuwa tumaki da gonaki, a zamaninshi yana d'aya daga cikin masu kud'in da ake lissafawa a garin maradi da kewayenshi, amma dayake ya samu hatsabibiyar mata data riga ta gama mallakeshi da sihiri saiya zamana dashi da talaka duk d'aya, domin kuwa gidanshi ma ba'a cin abinci mai kyau bare suruta, tunda Saratu ta shigo gidan take fuskantar matsi daga gareta inda ta mayar da ita kamar baiwa a gidan mijinta, duk wahalar gidan ita ce har lokacin da rabon 'ya'yansu ya koka suma suka durmiya cikin wahalar, duk da kasancewar Suleymane babba kuma namiji amma haka ya zama kamar d'an daudu dan duk wani aikin gida na mata babu wanda bai iya ba, haka suke wannan rayuwar kamar bayin da aka siyo da kud'i dan babu wanda zasu fad'a ma ya taimakesu, duk da lokuta da dama Husseina na basu matsala dan ita ce marar hak'uri, amma haka zatayi saboda uwar na tausarta da cewa tayi hak'uri wata rana sai labari.

Saratu dama marainiya ce ba uwa ba uba, k'anin mahaifinta ya bayar da aurenta ne saboda dukiyar Alhaji Hassan, hakan ne yasa babu wanda suke kaiwa kukansu ma bare su saka ran za'a share musu, a cikin wannan bautar da k'ask'anci tafiya tayi nisa yara duk suka mallaki hankalin kansu, 'yan matan sun zama cikakkun 'yan mata da suka isa aure, haka shima Suley ya girma sosai, sai dai matan kamar mujiya suke a cikin tsuntsaye saboda bak'in jini, domin kuwa babu mai kallonsu da sunan so ko k'auna, abun duba kuma shine gasu kyakyawa saboda sunyi kama da mahaifiyarsu wacce ita d'in asalin *babarbara* ce ta *Diffa*, amma haka suke ba mashinshina sai wahalar gidan ubansu kamar zata kashesu, a cikin haka
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment