Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

a bayansu tace "Duk wannan yawon naku amma girki ya kasa kammala sama da awa d'aya?"

Kowa a tsorace ya juyo uwa uba Zeituna da taji kamar tayi fitsari, cikin i'ina Nana tace "Kiyi hak'uri Hajia, saura kad'an ya k'arasa nuna ne."

Zeinabu ma wurk'il wurk'il tayi da ido tace "Bari naje ni na gyara wurin cin abincin kafin ku ida"

Fita tayi Hajia ta bita da harara kafin ta kalli Nana tace "Na baki minti biyar naga komai a gabana, idan ba haka ba kin dai san akwai masu neman aiki dake jiran samun irin damarki."

Tana fad'a ta juya ta fita, da sauri Nana ta sake bud'a tukunyar dan duba perper soup d'in kayan cikin ragon, amma abun mamaki da al'ajabi yana nan kamar dai yanda ta sakashi, a hakan ma wai dan ta silalasu tun jiya ta aje, amma yanzu kama daga kayan miyan zuwa naman komai na nan da ranshi yanda ta zuba, idonta cike da hawaye ta kalli Ummy tace "Aunty, wallahi har yanzu ko alamar dahuwa baiyi ba, bansan ya zanyi ba, gashi Hajia ta bani k'ank'anin lokaci, nasan lokacin barina gidan nan ne yayi."

Soueiba da ummy6ne suka matsa suka duba tukunyar, da tsantsar mamaki Soueiba tace "Amma ya ci ace abun nan ya dahu duba da ko da na sameki madafar nan har kin soya miyarki."

Ummy ce tace "Gaskiya kam, dan ko ni da na zo daga baya na samu tana shirin tsayar da ruwan miyar, da shigowata kuma yanzu a k'alla na d'auki minti kusan talatin, amma ace bai dahu ba? Abun kam da mamaki."

"Yanzu ya zamuyi? Wallahi a tsorace nake, Hajia ta turo ni ne dan na kama aiki, kar ta d'ora min laifin." Cewar Zeituna a matuk'ar razane. Matsawa Ummy tayi ta sake bud'ewa tukunyar wuta tana motsawa ta ga ko ya fara d'aukar hanyar dahuwa, babu wannan alama dan haka ta rufe tukunyar tace "Mu bashi minti biyar d'in shima muga ko zaiyi."

Baya suka ja wasu daga ciki suka zauna kan kujerun da suka k'awata madafar suka buga tagumi, dan kowa yana da tabbacin ba zai sha ba inhar basu gama kan lokacin da aka basu ba. Lokacin da aka basu na cika Ummy tayi saurin bud'a tukunyar, amma juya iya yau babu abinda ya sauya, abun mamaki ne wannan matuk'a, dukansu babu wacce bata nuna alamar wannan mamakin ba, Ummy ce tace "Anya kuwa? Ko dai..."

Sai kuma tayi shiru sai Soueiba ce tace " 'Yan biyu?"

Ba tare data kalleta ba tace "Bani da tabbas, amma kuma ai basu da k'ohi yanzu."

"Kada muyi saurin yanke hukunci, amma wannan abunda yake faruwa yafi kama da aikin 'yan biyun gidan nan." Cewar Soueiba, girgiza kai Ummy tayi tace "Ko hakane ma sai dai aikin Amna, dan tafi 'yer uwarta mugunta tun suna yara haka nasha wahalarsu."

Ajiyar zuciya Soueiba ta sauke tace "Sai kiji ki lallab'a mana ita mu samu mu ida girkin nan."

Murmushi Ummy tayi tace "In dai har Amna ce, to ba zata hak'ura ba sai dai kawai wanda ya rabasu jiya yanzun ma ya bata hak'urin, dan nasan tana fushi ne saboda an kirashi ya tilasta ta ko kuma dai dan tabawa yar uwarta hak'uri."

Soueiba ce tace "To kiyi magana da Ammar d'in mana shi ya rarrasar mana ita."

"Ba zan iya ba, ke kije." Ta fad'a kai tsaye. Kallonta Zeituna tayi sai Soueiba data kalli Nana tace "Kinga Nana, tun kafin Hajia ta dawo ki hanzarta b'angarensu Ammar ki kira shi, dan naga motar shi har yanzu tana nan alamar bai fita ba."

"To." Nana ta fad'a tana fita daga madafar, a hankali ta bi ta bayan Hajia ta sulale ta bar d'akin ta je b'angarensu Ammar, babu kowa a falon amma kuma k'ofar bud'e, ita kuma har ga Allah tana shakka da tsoron halin Ammar data shiga dan ta bubbuga k'ofar shi, dan haka ta juyo ta zab'i ta gaya musu su suje da kansu, tana dawowa kuma Ammar ya d'auki makullan mota ya bar gidan wanda yayi daidai da fitowar Soueiba dan ta mishi magana, amma kash har ya fita daga gidan sai komawa tayi.

Sanda Hajia taji meke faruwa da kanta ta samu Amna har d'aki tana gaggawar shiryawa zata tafi makaranta wajen jarabawa, tatas ta mata ta zageta uwa da uba sannan tace in har abincinta bi dahu ba zata kuma ci mata uwa, haka Amna ta fita rai a b'ace akan motonta dan Hamna ta jima da tafiya, amma tayi niyyar yau Hajia ba zata ci abincin ba ko da na rana ma tunda bata iya bayar da hak'uri ba.

A tak'aice dai ๐Ÿ˜‚ Hajajju sai yan dubaru tayi, yara ma haka aka musu dubaru aka tura su makaranta, Ummy ma haka dubarar tayi kafin ta wuce asibiti inda ta samu Ammar yau ya rigata zuwa, amarya Zeituna ma a d'akinta ta samu madara da cornflakes ta mishi had'in kauri tasha ta kwanta tana tunanin ahalin gaga. Da rana sam Nana ba tayi tunanin komai ba ta gyara shinkafa ta bayar aka b'arzota ta d'ora tukunyar dambu, ba b'ata lokaci tukunya ta taso aka fara yamutsa dambu, ana gama gyara komai aka d'ora a madambaci aka rufe, nan Nana ta shiga sarrafa mahad'in dambu, 'yar k'aramar sauce ce mai nik'akk'en nama da albassa mai yawa, saida ta fuskanci yanzu dambunta ya isa ta dubashi ta tunkari tukunyar, tana bud'awa bud'e baki tayi kamar zata k'urma ihu tare da d'ora hannu d'aya bisa kai tace "Na shiga uku, yanzun ma?"

Da sauri Zeinabu data shigo tace "...


*Alhamdulillah*๐Ÿ˜
09/09/2020 ร  17:58 - Ummulkhairi: ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ
*BADAK'ALA*
๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘จ

*Labarin Gaske*

*NA*

_SAMIRA HAROUNA_

*Litattafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._

*SADAUKARWA GA*

๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ _*AHALI NA*_๐Ÿ‘จโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

๐Ÿ‡ณ๐Ÿ‡ช *TAURARIN NIGER*
```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)```

_Bismillahir rahamanir rahim_

_30_


"Mun shiga uku! Kar dai ki ce har yanzu ma ba zamu ci abinci ba?"

Cike da tabbatarwa tace "Ai kuwa dai wallahi da alama."

Juyawa tayi ta fita tana fad'in "A'a wallahi ba zai yiwu ba, bari na d'auko wayata na kira Sa'ada ta zo ta sa Amna ta sakar mana tukunya, yau ni naga ikon Allah."

Tana daf da kaiwa d'akinta lieutenant ya shigo, wanda ya kasa zama ya matsu ya ga halin da Zeituna take ciki, sunkuyar da kai tayi tace "Ina wuni Abban Ammar."

Cikin sakin fuska ya amsa da "Lafiya lau, ya gidan?"

Ba b'ata lokaci tace "To da sauk'i dai gaskiya." Da mamaki ya kalleta yace "Lafiya dai ko? Ko wani abun ya faru ne?"

Cikin sunkuyar da kai ta fad'a mishi duk abinda ke faruwa, murmushi taga yayi yace "To ku samu ku lallab'a ta mana, kunsan dai fad'a da zagi ba zaisa ta huce ba."

"Eh hakane, yanzu ma zan d'auko waya ne na kira Sa'ada saita lallasar mana ita."

Da 'yar dariya lieutenant yace "To ke ba zaki lallab'ata ba?"

"To ai ni bansan ta inda zan fara bane, ita kuma ta saba da rigimar bibbiyu dama."

Dariya ya sake yi yace "Da gaskiyarki kuma, tana ina Amnar?"

Nuna sama tayi tace "Tana sama dai a tunani na."

"Bari na jaraba na gani ko zan iya." Ya fad'a yana wucewa d'akinsu dake sama, zaune tayi falo ta jira shi ya fito taji ya suka k'are, yana zuwa saida ya k'wank'wasa k'ofar d'akin yayi sallama, kusan a tare Hamna da Amna suka amsa wanda kowace ke kan gadonta babu mai kallon wata, saida kowace ta gyara zaman tufafinta kafin Amna da gadonta ne farko ta taso ta bud'e k'ofar, gaishe shi tayi ya amsa cikin sakin fuska tare da dafa kanta, murmushi yayi kafin yace "Amnata baki jin yunwa ne?"

Da sauri ta d'aga matsakaitan idonta ta kalleshi sai kuma tayi k'asa da su tana jujjuyasu, jin shiru yasa yace " 'Yata, yunwa nake ji, kuma na zo gida an fad'a min wai kin rik'e tukunyar girkin, shine nace bara na zo na rok'i alfarma, ko baki saketa dan ni ba ki saki dan k'annanki da kuma angonki Alhaji, wanda kinsan basa juriyar yunwa, da safe ma ance basu ci wani abun kirki ba."

Ganin tayi shiru yasa ya sake dafa kanta yace "A taimaka mana kinji, kiyi hak'uri komai ya wuce."

D'agowa tayi ta kalleshi tayi murmushi tace "Ba komai Abbanmu, nima ba'a son raina bane haka ta faru."

Murmushi ya mata yace "Nagode 'yata, Allah miki albarka."

Da murmushi ta masa da "Ameen Abbanmu."

Juyawa yayi ya samu Zeinabu zaune yace "To ku tashi ku duba tukunyar ku gani."

Yanda yayi maganar yasa ita ma tayi dariya tace "Yaran nan, mun gode Allah da yasa basu da k'ohi, da ina ga zuwa yanzu duk mun kamu da ciwon yunwa."

Dariya yayi yace "To wai ya akayi ma haka ta faru bayan kuma basu da k'ohi? Abun da mamaki fa."

"Wallahi nima ya ban mamaki." Madafa ta wuce shima ya shige d'akin Zeituna, kwance ya sameta akan sallaya ta idar da sallah, yanzu ma doguwar riga ce jikinta da hijab, sululu ta mik'e zaune cike da kunya tace "Sannu da zuwa, ina wuni."

Yaji dad'in gaisuwar data mishi dan haka ma ya saki murmushi ya sunkuya ya d'agota ta mik'e tsaye, saida suka k'arasa bakin gado ya zauna sannan ya zaunar da ita kan cinyarshi yana kallon fuskarta, yanda take sunkuyar da kai kamar zata nitse k'asa, d'ago hab'arta yayi ya juyo da kallonta kanshi yace "Wai ke yaushe kunyar nan zata k'are ne? Ba zan iya tuna ranar da muka had'a ido dake ba fa? Ya kamata ace ance yanzu kin saba ko dan igiyar data d'aure mu wuri guda ni dake."

Zeituna dai k'ala ba tace ba sai sunkuyar da kai da take, ba tare daya daina mata kallon nan ba yace " Na zo duba jikinki ne fa, to ya kike ji yanzu? Ba kya jin ciwon komai?"

Da sauri tasa tafukan hannayenta ta rufe fuskarta saboda tsananin kunyar data kamata, dariya yayi tare da k'amk'ame ta sosai a jikinshi yana sumbatar ta, (Harkar fa ta manya ce, nayi nan ni dai๐Ÿƒโ€โ™€๏ธ).

Zeinabu na zuwa suka duba tukunya sai suka ga har dambun ya fara rusuna alamar zai d'auki dahuwa, ajiyar zuciya ta sauke tace "Ikon Allah, duk da ana cewa a daina yarda da canfi amma wani abun idan ka ganshi dole ka amince, to Allah ka gafarta mana."

Lieutenant bai jima ba ya sake fita dan baya son Hajia ta saka masa na jiyamu, fitarshi kuma ta bawa Zeituna damar zuwa madafa aka k'arasa sauran aiki da ita, suna cikin jera kwanukan abincin Ummy ta dawo, wanka tayi ta fito lokacin har Hajia ta ci nata abincin ita kad'ai akan makeken teburin daya had'a kujera goma sha biyu, fitowar Ummy suma matan da su Hamna suka zauna suka ci na su abincin, a wurin ne Ummy ta dannawa Amar kira, bayan ya d'auka tace "Kana cikin gida ne?"

Daga b'angarensu ya amsa da "Eh Ummy, kin dawo ne?"

"Na dawo, ka jira yanzu za'a aiko miki da abinci." Amsawa yayi da "To Ummy."

Tana aje wayar ta kalli Kamal dake kusa da ita tace "Ka shiga madafa abincinsu na nan a kula ka kai musu."

Soueiba ce ta kalli Kamal tace "Daga nan ka duba ka gani ko Jibril yana nan sai su ci tare."

Da kai kawai ya mata alamar to, Zeinabu ce ta kalleta tace "Yana ciki ai, na ga shigowar motarshi kuma har yanzu tana nan, tare da Junaid ma suka shiga."

Soueiba ce tace "Ah to shikenan, ka kai musu kawai, kace idan ma bai ishesu ba sai su zo a k'ara musu, dan yau kowa ya wuni da yunwa saboda Amna yau ta hora mu."

Dariya suka kwashe da ita banda Zeituna da tayi shiru tsananin mamaki ya k'ara rufeta, sai yanzu ne data shigo gidan ta fara fahimtar wata b'oyayyar rayuwa da suke, kowa d'an shi kawai ya sani bai damu dana d'an uwa ba, sannan ita kuma Ummy da take da yara biyu d'ayan kawai ta damu da shi, amma Ammar dake babban d'an ta bata nuna kulawa a kanshi ba, kuma ta tabbatar yana gidan dan ya riga sauran ma zuwa gidan, hakan yasa taji ba dad'i sosai ta mik'e daga kujerar ta nufi madafa, wani kwano ta samu madaidaici mai kyau ta zuba dambun ciki sannan ta samu k'aramin shi ta zuba had'in nik'akk'en naman da petit poit sannan ta fito, kai tsaye hanyar waje ta nufa ta kuma sa'ar had'uwa da Kamal ya dawo, kwanon ta bashi tace "Kamal, ka kaiwa yah Ammar kaji."

Kallonta yayi yace "Aunty Zeituna, har yanzu yah Ammar zaki ci gaba da kiranshi?"

Dariya tayi tace "To ya kake so na kirashi? Ai yayana ne a zahiri, ka je ka kai masa ka dawo."

"To." Ya fad'a yana juyawa ya koma b'angarensu, yana zuwa wata sallamar ya sake yi ya shiga, kai tsaye d'akin Ammar ya nufa har Amar na fad'in "Autan Ummy ina zaka je?"

"Wajen babban yaya." Ya fad'a ko juyowa baiyi ba, k'wank'wasa k'ofar d'akin yayi tare da turawa ya shiga, kwance yake yana kallon sama yayi nisa a tunani, har ya tsaya gabanshi ya aje kwanon k'asa bai kalleshi ba saida yace "Yah Ammar ga abincinka nan."

A hankali ya kalleshi ya tashi zaune, kallon kwanon yayi ya sake kallon Kamal yace "Abinci na kuma?"

"Eh." Kamal yace ya juya da niyyar fita, sake cewa yayi "Abinci fa? Wa yace ka kawo min?"

Juyowa yayi yace "Aunty Zeituna ce, amaryar Abba."

Bushewa yayi da dariya kamar mahaukaci sabon kamu, irin dariyar da yake yi ce yasa Kamal cewa "Yah Ammar lafiya?"

Tsayawa yayi ta kalleshi yace "Ko da nace, ni nasan inba bak'o ba babu wanda zai aiko min da abinci, to naga dai ko uwar data haifeni bata damu da ci na ba bare kuma wanda suke kewaye da ita."

Jinjina kai yayi yace "Amaryar Abba, amma me yasa zata aiko min da abinci?" Kamal ne yace "Ni ma ban sani ba."

Da mamaki Kamal yace "Zaka ci kenan?"

K'uri ya masa da ido yana kallo hakan yasa ya fita ya rufe mishi d'akin, yana ganin fitarshi ya shafa cikin da har kukan yunwa yake masa amma kasala ta hana shi fita ya je ya ci abinci, murmushi yayi yace "Zan ci mana Kamal, har na manta kalar d'and'anon abincin gidan mu, ina ma Ummy ce ta aikoka da abincin nan, da na ci da farin ciki da kuma karsashi ko da bana yanayin cin abincin, amma gashi matar data shigo gidan nan jiya wacce nayi mata kashedi akan uwata ita ce ta zubo abinci wai akawo min, duk da bansan manufarta na yin haka ba amma dai hakan yasa na ji kamar an kula dani ne."

D'auko kwanon yayi ya bud'a, take yaji yawunshi sun tsinke, tashi yayi yaje ban d'aki ya wanko hanayyenshi ya fito, saida yayi bismillah tare da fad'in "A'u'zu bikalmatillahi tammat-min sharri ma kalaq." Duk yayi hakane dan aniyarta ta koma mata wai idan ma abinda ya mata jiya ne zaisa ta fara gaggawar d'aukar mataki akan shi.

*A gurguje*

Da magribar wannan ranar aka kawo kayan Amar ma, shi ma dai kamar yanda Ammar yayi haka ya kawo, sai dai ba shine ya kawo ba, wasu daga cikin yan uwa na dangin mahaifinsu da kuma abokan lieutenant ne suka kawo, anan kuma take kafin su tafi Hajia ta shaida musu nan da kwana goma sha hud'u sati biyu kenan za ayi bikin, dan haka a shirya da kyau kafin lokacin, da haka labari ya riski kowa inda aka shiga shirya ma wannan rana.

Wani ikon Allah kuma tun daga wannan ranar kullum akayi abinci na rana da dare sai Zeituna ta fitarwa da Ammar, duk yaron daya tarbi gabanta shi take bawa yana kai mishi, lokacin da lieutenant ya fahimci haka kuma sai yace ta rabu dashi mana shi fa ba yaro bane, akan me ma zata damu da shi ne? Dariya kawai tayi tace tana yi ne saboda Allah, kuma taga shi bai damu da ya zo ya karb'a ba, Hajia ma baida habaici da cewa neman gurin zama ne babu abinda take fad'a mata, haka ma Ummy gani take wahala ce take ba kanta, indai Ammar ne wata rana ya gwasaleta, wannan shine abinda take fad'a, Ammar kuma kuma yanzu ya daina cin abincin waje inba na safe ba, ya sakankance yana cin wanda Zeituna ke aika musu, dan lokuta da dama tare da duka sauran yan uwan take aika musu musamman da dare lokacin duka sun dawo, Ummy da kanta ta shirya tare dasu Amna suka je madarunfa aka kaiwa Hadiza kayan Amna ta gani tasa albarka, data tambayi Ummy abinda za ayi ko ya rage sai tace babu komai da suke buk'ata daga wurinta, alfarma kawai ta nema na ta zo ran damu taga d'akin yarta hakan zaisa taji dad'i, a haka kuma ake ta shirye shiryen biki dan lokacin ya taho sosai.

Wajen amare ma sun gama jarabawarsu sosai aka zage ana ta gyaransu kamar hauka, dan Hajia da kanta tasa ake musu gyaran, da farko suna zuwa ne a musu, amma daya rage sati d'aya sai mai musu gyaran take zuwa gida tana musu, kuma a haka yaran zamanin suma amaren suke k'arawa kansu wani had'in wanda suka koya, Ummy ma haka ta zage tana dafa musu kaji tunda ta ga sauran sati d'aya, da haka har aka riski daren da za'a saka amare lalle.

Duk iyayen na zaune akan teburin cin abinci suna ci suna hira, kuma hakan ya faru ne saboda Alhaji na wurin, ba dan haka ba babu wanda ya isa ya cika Hajia da surutu alhalin tana cin abinci, Amar ne ya shigo tare da Ammar kamar wasu zakuna, Amar ne yayi sallama suka nufi kan teburin yana gaishe da mutanen wurin, Ammar na zuwa hannu ya zura gaban Hajia ya d'auki robar ruwan da take sha ya kifa bakinshi yasha sosai, kowa kallonshi yake har da ita kanta Hajiar, saida ya sauke robar ya kalli kowa dake wurin shima yana murmushi, lokacin da kallonshi ya sauka kan Zeituna wacce kanta ke k'asa ne ya fad'ad'a murmushin shi yace "Ina wuni."

Da sauri ta d'ago kanta lokaci d'aya kuma ta mayar dashi k'asa dan bata zaton da ita yake, duk wanda ke gurin kallonshi sukayi da matuk'ar mamaki, *yau Ammar ne ke gaishe da wani?* gaisuwar ma ga wacce ba'a tsammanin zai iya gaisheta, ganin irin kallon da suke mishi yasa ya sake kallon Zeituna yace " Dake fa nake, *uwa*."

Sake d'agowa tayi cike da tsoron abinda zai iya fad'a mata, suna had'a ido bata san lokacinda tace "Yah Ammar ina wuni."

Murmushi ya mata yace "A'a uwa, ki kira ni Ammar kawai, ko kuma ki kirani da *d'an ki*, tunda ke ma uwata ce."

Wata irin dariyar rainin hankali Hajia ta bushe da ita har da gaggab'awa take, wani kallo Ammar ya mata kafin ya kalli Ummy yace "Ummy ina amaryata take? Ina so zamuyi magana ne."

Hararan sama da k'asa ta masa taja dogon tsaki, mayar da kallonshi yayi kan Zeituna yace "uwa dan Allah zaki iya fad'a min inda take?"

Zeituna da ita dai al'amarin d'an mijin nata ke tsorata ta da sauri tace "Tana d'akin..." Da sauri Ummy ta katseta da cewa "A'a Zeituna, rabu dashi kawai, uwar me zai bata yanzun?"

Tab'e baki yayi ya kalli Zeituna yace "Uwa zan iya baki sak'o wurinta?"

Kamar sakarai haka take kallonshi baki bud'e ta jinjina masa kai alamar eh, da hannu ya mata alama yace " Zo to, sirri zamuyi."

Mik'ewa tayi tsaye zata tafi lieutenant ya daka mata wata harara yace "Wai ke me yake damunki ne? Kanki d'aya kuwa ko kuma ke ma irinshi ce?"

Alhaji ne yace "Babba, ka barta dan Allah."

Murmushi Ammar yayi yace "Abba kwantar da hankalinka mana, babu inda zan tafi maka da matarka, nima fa uwata ce."

Wata harara lieutenant ya wurga masa wanda tasa Ammar kwaso shoki, har zai sauketa akan idon lieutenant sai kuma ya juya ya kalli Amar dake gefenshi ya watsa mishi ita a fuska, Zeituna na zuwa kusa dashi saida ya k'ara matsawa kusa da ita ya juya baya suka bawa mutanen baya kafin ya sassauta murya yace "Uwa ki samu Amna a d'aki ki fad'a mata ta baki kayanta ki kawo min za'a d'auki awonta ne (mesure)."

Jin abinda ya fad'a yasa Zeituna sauke ajiyar zuciya ta kalleshi tace "Toh." Da sauri ta juya ta nufi d'akin Ummy inda amaren suke, tana shiga ta same su tare da wasu daga cikin k'awayensu, gabanta ta tsaya tace "Amna, sak'o daga angonki wai ki bado kayanki za'a d'auki awonki ne."

Kallonta tayi tace "Yah Ammar? D'inkin zai min?"

Da murmushi ta amsa mata da "Ni ma ban sani ba, tashi ki d'auko kawai."

Mik'ewa Amna tayi ta fito Zeituna na biye da ita a baya, d'auko mata kayan tayi ta bata ita ma ta juyo dan kawo masa, tana zuwa ta same shi tsaye kusan Hajia sai kallonta yake, ita kuma ta had'e fuska sai hararenshi take, Amar dai dariya yake musu har yace "Dan Allah Hajia ki ci abincinki kar ki biye masa, so fa kawai yake ki biye masa kuyi fad'a."

Tab'e baki tayi tace "To ai yanzu ni ya daina bani wahala shalele, ka rabu dashi zaiyi ya bari ne inya gaji."

Da wani murmushi a fuskarshi yace "Da gaske Hajia? To zan gani."

Zeituna na bashi kayan a leda ya karb'a ya matse ledar a hammata, ba zato ba tsammani ya daddage ya samu hak'ark'arin Hajia ya danna mata cakulkuli, ( Hajia mutan makka๐Ÿ˜‚), ai wata zabura Hajia tayi daga kan kujerar tare da sakin ihu har cokalin hannunta ya fad'i abincin cikin cokalin ya zube, haba wa ai sai Amar ya fashe da dariya tare da taimakon Alhaji da Husseina, Ummy kam da Zeinabu da Soueiba duk rufe bakinsu sukayi suna toshe dariyarsu, Ammar da tuni ya zura a guje shima dariyar yake, yana kaiwa bakin k'ofar fita daga gidan ya had'e da Hamna ta shigo tare da k'awar ta wacce ya amshi lambarta, tsayawa yayi suna kallon juna da ita b'angare d'aya kuma yana kallon Hamna da wutsiyar ido, washe baki tayi tace "Lah mai kyau, sai ganshi dai yau mun had'u, dama kuma ina son ganinka dan naji dalili da yasa baka kirani ba."

Yanda ta kafeshi da ido alamar tana jiran amsa yasa yayi murmushi ya kalli Hamna yace " Hum! Kinga ranar da kika bani lambar nan, saboda ina tuk'i daga na bawa k'awarki ta saka min sunanki akai, sai kawai tace min wai ta goge, to har yanzu ina so na sani ne gogewa lambar tayi ko kuma gogeta akayi, shine abinda na kasa fahimta."

Wani marairaicewa yayi yace "Dan Allah budurwata ki tayani tambayarta ta fad'a min, na shiga damuwa sosai saboda rashin kiranki da banyi ba, da zaran na kwanta bacci ke nake gani a idona, idan ina wanka ma ke nake ji kamar kina goga min bay..."

Hamna ce ta fizgi hannunta tana fad'in "Dallah *Ami* wuce mu tafi, k'arshen marar kunya ne wannan yanzu saiya fad'a mana abinda kanmu ba zai iya d'auka ba."

Juyowa yayi ya bita da kallo yace "Kunya? Ai laifinku ne inma bana da kunyar, tunda sanda ake rabonta ina bacci kuma babu wanda ya tasheni."

Tsaki Hamna tayi wanda yasa ya juya da hanzari ya kamo k'aramin kallinta, duk da ta tsorata da yanda ya fizgota ya kuma kalleta da jajayen idonshi hakan bai hanata cewa ba "Dallah malam sake ni, ni yanzu sam bana son had'a hanya..."

Bai bata damar k'arasawa ba ya kama dogon hancinta yaja sosai, siririyar k'ara ta saki take idonta suka kawo ruwa saboda zafin da taji, k'ank'ance idonshi yayi yace "Na sake jin tsaki ya fito daga bakinki zuwa kaina wallahi zaki rasa hak'oranki."

Sakinta yayi ya juya zai fita Ami tace "Mai kyau."

Tsayawa yayi ya juyo a hankali ya kalleta, matsowa tayi tace "Nace ka kawo wayar taka saina saka maka lambar ko?"

Saida ya kalli Hamna yace "Ki barshi kawai, wacce ta goge lambar uta zata sake bani ita da kanta."

Yana fad'a
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment