Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

k'ofa, da sauri kamar zatayi gudu ta riskeshi yana shirin shiga gabjejiyar motarshi fara tas, rik'eshi tayi ta baya tana turo baki, juyowa yayi ya kalleta fuska a had'e yace "Ya dai malama? Sake ni sauri nake."

Ba tare data saki rigarshi ba taja ta har k'asa ta durk'usa gabanshi ba tare da jin nauyin cikinta ta marairaice tace "Ammar karka min kishiya ko ta waje ce dan Allah, ina sonka ba zan iya rabaka da kowace mace ba wallahi, dan Allah kayi hak'uri ka fad'a min duk abinda kake so da wanda baka so zan yi wallahi."

Saida yayi da gaske ya cije dariyar dake son taho mishi, kallonta yayi yana d'an basarwa yace "Kin tabbatar za kiyi komai nace miki?"

"Allah kuwa zanyi, na rantse maka."

Kamo hannunta yayi ta mik'e yana kallon fuskarta yace "Da fari ina so ki daina kirana Ammar gatsau babu sayawa, in baki manta nasha fad'a mikibana so, amma dana ga kin k'i dainawa saina zuba miki ido."

Da tsantsar gaskiyar dake tattare da ita tace "Allah daga yau ba zake sake jin baki na yace hakanen ba, *duniya ta*, nima zanyi kamar yanda yer uwata ke yi."

Ajiyar zuciya ya sauke cike da k'aunar wacce ta ambata yace "Allah ya gafarta mata."

Kamar za tayi kuka ita ma tace "Ameen."

Kallonshi tayi tace "To sai me kuma?"

Kallon fuskarta yayi yace "Ko daina min rashin kunya, bana son ina cutar dake."

A marairaice tace "Shi ma na daina."

Murmushi yayi ya shafi fuskarta yace "To shikenan babu ke babu kishiya ko ta cikin gida ce barz ta waje, yanzu kije ki huta abinki kafin na dawo na tayaki hira."

A sangarce tace "Ka kula min da kanka."

"Ke ma ki kula min da kanki." Ya fad'a yana shiga motar, ta cikin gilashi ya bita da kallo har ta shige kafin ya tayar mai gadi ya bud'e masa k'ofa ya fita. Dariya kawai yake shi kad'ai Hamna ce durk'ushe a gabanshi, yana sonta kuma ya yarda ita ma tana son shi, yana jin dad'in zamantakewarsu kuma yana alfahari da hakan, sau da dama sukanyi fad'a har ta kai basa kula juna, amma ko awa basa yi suke shirya kansu cikin sauk'i, wani lokacin ma daga inda aka samu sab'anin ake d'inkewa ya shiga wainata yana rawa da ita ko ya goye har su shirya, hakan ne yasa zaman nasu dad'i da fahimtar juna.

*Kamar* tsautsayi kam akan hanyarshi sai ga d'aya daga cikin mutanen da har yau idan ya tunasu sai yaji kamar yayi kuka, kaf tsawon rayuwarshi babu wanda suka tab'a wulak'antashi sama dasu, ba'a tab'a mishi cin zarafin da suka mishi ba, ba'a tab'a mishi abinda bai rama ba, amma su sun sha daga kalaman mahaifiyarshi, alk'awarin daya mata ya tseratar dasu daga d'aukar fansar shi.

Amma kuma yanzu ga d'aya a cikin jami'an da suka dinga hantararshi da hana shi abincinshi, yana gaba akan mota yana birka gudu sosai da hular kwanon da ba mai rufe kai ba duka, d'an lumshe ido yayi tare da bud'ewa yace "Ummy ki gafarce ni, wallahi zuciyata tsayawa za tayi idan ban d'an tokareshi ba."

Yana fad'a ya jawo belt d'inshi ya mak'ala sai kawai ya k'ara gudun motar, saida ya daidaici tayar moton kawai ya zungureshi, sai kawai ji akayi gijim ya wuntsile ya fad'i kan moton, da sauri ya taka birki haka mutane dayawa ma duk aka zagaye shi ganin soja ne fan a cikin tenue yake.

Da sauri ya fito daga motar yana rΓ©action irin abun a bazata ne ya zo, ko da ya k'araso wajenshi suka had'a ido sai yace "Yallab'ai, kai ne ashe? Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un, na shiga uku yau, sannu yallab'ai dan Allah kayi hak'uri, wallahi..."

Bai barshi ya k'arasa ba dan shi kanshi ko da ya ganshi a ranshi ma yace ai dole ya hak'ura, mik'ewa yayi cike da dauriya yana fad'in "Kai haba ba komai Elaji, tsautsayi idan ya wuni baya kwana ai."

Hannunshi ya damuk'o ya rik'e sosai yana fad'in "Wallahi hakane, kawai wata waya ce aka min da nake da tabbacin ba lafiya ba, kasan ai ita yar gwamnan naku nake aure, to ita ce na baro gida da tsohon ciki, shiyasa hankali na baya kwanciya idan na fito."

Murmushin dole ya mishi yace "Ah to Allah yasa alkairi, Allah ya raba lafiya, ba komai kaje kawai."

Da sauri yace "A'a ka bari na aje ka asibiti ko?"

Shima da sauri yace "A'a wallahi ka barshi, ai banji ciwo ba."

Mik'ewa yayi ya mishi sallama ya juyo zai koma mota, murmushi yayi murya k'asa k'asa yace "Da ubanka ne zai kaika asibitin, daka yarda ka shigo mota ta da nufin na kaika asibiti da sai dai a wuce da kai morgue daga nan, kad'an ma ka gani wallahi Ummy ta cece ku."

Bayan ya dawo daga inda yaje gida ya wuce, yara na ganinshi suka ce ai sai dai ya koma dasu, da k'yar ya lallab'asu suka rabu, saida ya keb'e da Ummy yace "Ummy dan Allah ki yafe min duk laifin da kika san na miki, kina sane ko rashin sani."

Da murmushi a fuskarta tace "Ba komai Ammar, na.
yafe maka duniya da lahira."

"Nagode Ummy." Ya fad'a yana musu sallama ya bar gidan, saida yaje ya samu Hamna ya shiga fad'a mata abinda ya faru dalla dalla sala sala, ita dai tayi dariya kamar cikinta zai fashe, daga bisani kuma ta raka shi addu'a.

*Rayuwa kenan*, abun kamar jiya ne aka fara sai gashi yanzu da aurensu *shekara uku* kenan, yanzun ma namiji ta haifa wanda ya ci sunan *Hassan* suke mishi alkunya da *Elhaj*, Ammar ya tayar da billi shi fa yan uku yake so ya haifa, Hamna kuma dake k'ok'arin cika alk'awarinta duk in yana tijara yanzu sai dai tayi gum da baki tana saurarenshi, in yayi ya gaji sai ya koma ya fara juye mata yana kiran ta raina shi ta d'aukeshi mahaukaci ne, duk da haka bata kula shi sai dai ta bar mishi wajen har sai ya gaji dan kanshi.

*Yau* hankalin Jibril in yayi dubu ya tashi, yarinyar da yake saka mata ido, yarinyar da duk inda zata je tare da dreba take, amma aka wayi gari da sunan taje Γ©cole kawai ya had'e da ita a wani babban store tare da k'awayenta da kayan makarantarsu alamar daga can suka wuce, hakan na nufin tana fita daga makarantar kenan? Ya so mata dukan mutuwa sannan yaji daga ina suke kuma ina zasu je, amma Jamila ta shiga tsakani tace ba za ayi haka da ita ba, tunda tace abu suka je siya kuma su koma kawai ya hak'ura, amma tsoron kar wani ya mishi kutse a rayuwar yarinyarshi da kuma kiyaye maimaituwar tarihi sai kawai ya yanke wani tsatsauran hukunci a kanta.

*Sadiq* zaman d'a yake ga Husseina, ya yarda da yaron yana d'aya daga cikin masu kula mishi da mangazarshi da ake aje kaya, ganin tunda yan uwa ne kawai yasa shi cewa in yana sonta ya bashi aurenta, yaro ya ga banza ta ina zai bijire? Sai kawai yace yana so shima ya amince, kamar wasa sai manya suka shiga maganar akayi komai a gaggauce, inda yace zata kammala karatunta a gidan mijinta.


*Alhamdulillah*
04/11/2020 Γ  14:40 - Ummulkhairi: πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨
*BADAK'ALA*
πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨

*Labarin Gaske*

*NA*

_SAMIRA HAROUNA_

*Litattafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._

*SADAUKARWA GA*

πŸ‘¨β€πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘¦ _*AHALI NA*_πŸ‘¨β€πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘¦

πŸ’«βœ¨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🀝

β˜† *[ T.M.N.A]* β˜† πŸ“–πŸ–ŠοΈ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_

_78_


*Zo* ka ga uban amarya uban d'aurin aure Ammar, shi Jibril ya bawa d'aurin auren wanda hakan ya masa dad'i, Mari tayi jarabar a kai mata Huda ayi biki ranar bikin sai a dawo da ita, amma Jibril sam ya gama fita harkar Mari yace ai kawai ta zo in tana so amma babu inda Huda zata je, har Amar saida ta ma magana a waya wai ya lallab'ashi, amma shima hak'uri ya bata yace Jibril bai amince ba.

*Yau* d'aurin auren Huda, Ammar ya kashe d'aurin hula ya k'ayatu cikin babban riga ta wani gallelen boyel bleue bics, ya gama had'uwa da tsaruwa fiye da ma angon.

Hamna ma ta gama shiryawa cikin shaddarta gezna colour bleue omo zasu tafi tare, tsaye suke dukansu gaban madubi yana ci gaba da gyara zaman hularsa, ita ma kallabi ta gama d'auri ta d'auki turare zata fesa ya fige yace "Turaren me kike buk'ata?"

Kallonshi tayi tace "Cikin mutane fa zan shiga."

Shareta kawai yayi ya aje kwalbar ya d'auki na shi turaren zai fesa, da sauri ita ma ta fige tana ja baya da gudu tana fad'in "Tunda ban saka ba wallahi kai ma ba zaka saka ba, duk mu tafi haka."

Juyawa yayi ya kalleta yace "Hamna kawo min turaren nan."

Hanyar fita tayi tana fad'in "Ba zan bayar ba Allah."

Ko da ta fita d'akinshi ta nufa da niyyar shiga ta rufe ta d'auke turarukan dake nan, dan tasan su zai nema duk da dai yafi aikida wanda ke d'akinta, amma kafin ta rufe ya biyota yana tattare babbar rigar yana fad'in "Ke in rashin mutumcin kike ji saina kwab'e wallahi mu daku yanzu nan."

Baya tayi tana fad'in "Me yayi zafi da zamu daku ni da kai? Turare dai ne ba zaka saka ba kai ma in dai ban saka ba."

Ko da taga ya tafi a guje zai kamota saita tsorata kawai ta buga kwalbar k'asa ta kuwa fashe saboda akan tiles ne babu carpet wurin, bud'e baki yayi da ido yana kallon kwalbar.

Saida ya b'ata rai ya kalleta yace "Hamna ni kika fasawa turare? Ni Hamna, ai ko zaki ga rashin mutumci a gidan nan."

K'uri ta masa da ido tana so tace ba dagangan tayi ba amma ta kasa, cire babbar rigar yayi ya aje kan gado ya tunkareta, ihu kawai ta saki dan ba zata iya guduwa ba kan hanyar fitar yake tsaye, saida ya tak'ark'are yasa k'arfi ya kimkimeta gaba d'aya, bai tsaya komai ba ya shiga wani irin juyin bala'i da ita yana hajijiya, tun tana ganin d'akin tana gane komai, har saida jiri ya d'ebeta ta dinga ganin d'akin na juyawa gaba d'aya.

A hankali taji kamar kanta zai cire duk tunani da lissafinta sun fara barin kwanyar kanta, rik'eshi tayi gam ta rintse ido tana jiran ranar da zai sauke ta, saida ya gamsu cewa ta kuru yanzu kad'ai ya direta k'asa, ganin wani luuuuu da tayi kamar zata kifa yasa shi b'anb'are hannayenta data rik'eshi gam, ai tuni d'aurin d'an kwalin ya rigata kaiwa k'asa duk suka watse a wurin, dafe k'asa tayi sosai saboda har yanzu juyawa ake da ita.

Rigarshi ya saka ya kalleta yace "Idan ki kayi wasa Hamna d'aurin auren nan da za ayi har da nawa za'a d'aura, kuma ke nake jira karki b'ata min lokaci."

Saida ya kai k'ofa zai fita ya juyo yace "Amma Hamna Allah ya saka min wannan wulak'ancin da kika min, yanzu waccen turaren kike sona saka mai warin yan wuta?"

Hamna da a lokacin kad'ai ta fara jin dama dama kallonshi tayi tace "Kenan kasan k'amshin yan wutan?"

Saida ya wani had'e fuska yace "Ina d'an ji kad'an kad'an."

Mik'ewa tayi tana ganin yana juya mata a hankali tace "A jikinka kake ji ko?"

πŸ˜‚πŸ˜‚πŸ˜‚

Da sauri ya dawo d'akin yana fad'in "Fito kai tsaye kice d'an wuta ne ni mana."

Hannayenta ta d'aga tana tare shi dan ba zata iya gudun ba tana fad'in "Ni fa tambayarka ne nayi a jikinka kake ji ko a jikin wani."

Juyawa yayi zai fita yana fad'in "Kinyi sa'a yau nake aurar da 'ya wallahi, da sai na miki cikin yan uku."

K'eyarshi ta ma gwalo tana fad'in "To inba d'an wutar ba wannan jirin daka d'iba dani kamar wacce ta hau jirgin sama."

Tafiya suke a hanya tana d'aura d'an kwali, cike da nishad'i yake biyar wak'ar wani film wai ita *madubin dubawa* wacce Ali Nuhu da Rahama Hassan sukayi play roll d'in, yana biya kamar abun gaske, amma daga jin baitin da jarumar ta fad'a ya kalli Hamna yace "Kinji wai ta sauke farashi, yo shi ba dan ma ana so a bada maza ba wane farashi ne har mace zata kallemu tace ta sauke, ke baki ga inda muke tsada ba ma ku ne ke biyanmu sadakin."

Shiru ta masa tana d'aura kallabinta kafin ya sake cewa "Kuma fa ita ba wata kyakyawa ba banda dai Allah ya taimake ta tana da manyan kaya."

Kallonshi tayi ta harareshi sama da k'asa tayi k'wafa, kallonta yayi yace "Me ye na hararata ke kuma?"

Saida ta gyara d'an kwalin tace "Inba gulma ba da sa ido har ka mata kallon k'waf ka gane manyan kaya ne da ita ko?"

"To makaho ne ni?" Ya fad'a yana kallonta, a hassale ta kalleshi tace "Ba mahako bane, amma idan na cire maka su zaka dawo makahon."

Wani kallo ya mata yace "Wai ke mayya ce?"

"Eh." Ta fad'a tana kumbura, tab'e baki yayi yace "Wai ma me ye farashin da take magana akai?"

Kallonshi tayi tace "Ka tambaye ta mana."

Tab'e baki yayi yace "Wai haushi kike ji saboda naga ita ma k'atuwa ce kamar ke? To naje na ce a dafani a cinye."

Wani kallo ta masa bata sake cewa komai ba har suka isa.

Yau fa akayi ta kam a wajen d'aurin aure, bayan an d'aura ya shigo da ango har cikin gidan, har d'akin Ummy inda amarya take ya zaunar dasu, hud'uba ya musu sosai mai ratsa jiki, saida ya gama kamar abun arzik'i sai kuma ya kalli Huda yace "Kina ji na? Duk sanda ya guma miki laifi ki zo ki same ni, sai kin fad'i yanda kike so na miki dashi, in na dafa miki shi da fatar jikinshi ne, ko kuma sai an cire fatar a dafa sai kin zab'a."

Ango dai murmushi ya saki inda ya kalleshi shima yace "Kai ma kuma idan ta b'ata maka, ka zo ka same ni zan fad'a maka yanda zakayi da ita."

Kud'in hannunshi ya mik'a ma Huda yace "Karb'i nan sadakin ki ne."

Cikin lullub'inta na dara tace "Abba ka rik'e kawai, ni babu abinda zanyi dashi."

Kallonsu Ummy dasu Zeinabu yayi yana dariya yace "Kunji wai Abba, yanzu nan fa ya ce na aurar, kai Allah nagode maka, yanzu nan da yan shekaru kad'an Amnata ma zan aurar da ita."

Kallon Huda yayi ya kamo hannunta ya damk'a mata kud'in yana fad'in "Wannan sadakinki ne, kamar yanda mijinki ne kad'ai ke da wani muhimmin hurumi akan ki yanzun, haka wannan kud'in ma ke ya dace ki rik'e abinki, lada ce ta wani muhimmin abu da zaki rasa a jikinki."

Sautin kukanta ta k'ara hakan yasa shi dafa kanta yana fad'in "Kar kiyi kuka mana, ni ma saiki saka ni kuka."

_(Allah ya bar mana kai kakanmu Tahir, ka iya wakilci)_

Saida ya kai k'ofa zai fita ya kalli Zeituna yace "Uwa wai me yasa amare ke kuka ne? Wani abu suke tsoro ko kuma fargaba ne?"

Da kunya ta shiga rarraba ido ta kalli Ummy tace "Aunty ce zata fad'a maka."

Da sauri ta bar wajen Ummy na fad'in "Ke dawo ke zaki iya da kayanki, ai ba ni ya tambaya ba."

Murmushi ya saki yana kallonta yace "Ummy na ma gane, to amma naga ai daga baya kuma idan kuka saba kun ma fimu zak'ewa."

Da k'arfi ta dafe k'irji tace "Mu kuma?"

Cikin i'ina yace "A'a ina nufin su, su matan."

Ficewa yayi ta bishi da kallo, ko data hange shi tsaye kan Hamna dake shirya yaransu da suka kwana anan tace "Allah fidda *A'i* daga rogo."


*Badak'ala na ban kwana insha Allah*


*Alhamdulillah*
04/11/2020 Γ  14:40 - Ummulkhairi: πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨
*BADAK'ALA*
πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨

*Labarin Gaske*

*NA*

_SAMIRA HAROUNA_

*Litattafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._

*SADAUKARWA GA*

πŸ‘¨β€πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘¦ _*AHALI NA*_πŸ‘¨β€πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘¦

πŸ’«βœ¨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🀝

β˜† *[ T.M.N.A]* β˜† πŸ“–πŸ–ŠοΈ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_

_79_


Ana ta cashewa a wajen bikin Hamna na zaune k'ofar gida tare da wata k'anwar Soueiba, ta baza mata hajar kayan mata tana dubawa inda Ameera ke kusanta tsaye, Ummy ce zata shiga cikin gidan ta kalli Ameera tace "Wai ke yaushe zaki girma ne? Kina nan k'ugunta ba zaki je cikin yara kuyi wasa ba."

D'agowa Hamna tayi ta k'ara mannata a jikinta tana fad'in "Ummy ki barta dan Allah, ni kaina bana so tana min nisa ai, mace ce dole ina buk'atar tafi sabawa dani fiye da kowa."

Tab'e baki Ummy tayi tace "Amma kuma bata sakewa cikin yara taya za tayi wayo da fasaha?"

Turo baki Hamna tayi tana kallon Ummy har ta wuce, kallon Ameera tayi ta manna mata sumba a kumatu tana fad'in "Ai kina da wayo ko?"

Kallonta tayi tana mak'ala hannayenta a wuyan Hamna tana dariya da fad'in "Ummy, in fad'a miki wani abu?"

Kallonta tayi tace "Fad'a min mana yer uwata."

Saida ta kalli k'anwar Soueiba dake ta mik'owa Hamna magani tana karb'a tana dubawa, cikin kunne ta rad'a mata magana, bud'e baki tayi da dariya a fuskarta ta kalleta tace "Da gaske? Haka yace miki?"

Cikin jin kunya ta rufe fuskarta da kallabin Hamna, jinjina kai tayi tana fad'in "Ina ga fa za ayi yar gida ce ko?"

Dariya suka saka gaba d'aya, tana cikin dubawa ta ga motar Ammar ta paka, da sauri ta shiga tattara kayan tana fad'in "Taimaka b'oye kayan nan kar mutumin nan ya sauke min kwadon tsiya a wurin nan."

A tsorace matar ta shiha tattarewa tana fad'in "Baya so kina aiki dasu?"

Saida ta gyara zamanta tana kallon motar tace "Ba haka bane, bana so ya sani ne kawai zai min tsiya wallahi."

Suna kallo ya fito ya canza kaya bana safe bane jikinshi, a hankali Ameera ta tarbeshi inda ya kamo hannunta suka k'araso, yana zuwa ya dangwari kan Hamna yana fad'in "Kankana me kike fad'a ma 'yarki naga kuna ta dariya?"

Matar na kallonshi tana musu dariya sai Hamna data dafe kanta tace "Yaushe?"

Kallonta yayi yace "Ke ni ba makaho bane ina gani, me kike fad'a mata?"

Turo baki tayi tace "To wai banda ikon da zanyi magana da "yata ne? Sirri mukeyi mana kai ma kaje ka kama naka yaran mana."

Tab'e baki yayi yace "Ke dai kika sani, yanzu tashi shiga cikin gida."

Da sauri ta mik'e tana fad'in "To yallab'ai." Kallon mai maganin tayi ta k'yabta mata ido ta shiga ciki tare da Ameera, a baya ya bisu yana fad'in "Yau ma ana bikin ba zaku rabu ba? Wai ke wace jaraba ce kika koyawa yarinyar?"

Gum tayi da baki dan ta fahimci me yake nufi, tayi magana ne ya fara tayar mata da hankali cikin mutane, rik'o mayafinta yayi hakan yasa ta juyowa tana kallonshi, kallonta yayi yace "Yunwa nake ji."

Wani kallo ta masa tace "To ya zan maka kenan?"

Shima wani kallon ya mata yace "Ya rage naki."

Wucewa yayi tana kallo har yayi bayan gidan, tasan kuwa d'akin lieutenant zai je ya zauna jiranta, girgiza kai tayi suka wuce ciki, inda ake girki taje ta samu an idar amma ana so ayi sallah la'asar sai a raba, plate ta samu ta zuba masa taje ta kai masa, har zata fita daga d'akin yace "Ke."

Saida tayi jim saboda ta tsani ya kirata da ke, juyowa tayi tana kallonshi yace "Zauna ki bani a baki."

A marairaice ta kalleshi tace "Yallab'ai biki fa ake gidan nan, kar kasa a saka mana ido mana, dan Allah ka ci abincin kai ma ka fita kafin ayi sallah."

Wani kallo ya mata yace "Yanzu Hamna saboda bikin ne yasa ba zaki bani abinci a baki ba? Bikin ya fini mahimmanci kenan?"

Tahowa tayi a k'ufule ta zauna ta jawo plate d'in zata bashi, mik'ewa yayi yana kallonta yace "Ke ni ba d'an iska bane, kawai daga bani abinci a baki shikenan na miki laifi, to bana ci Hamna."

Har ya juya zai fita da sauri ta mik'e da niyyar taroshi ta bashi hak'uri, sai kuma ya juyo a hassale yace "Ki same ni a mota yanzu har ke ba zaki zauna a wajen bikin ba."

Juyawa yayi ya fita hakan yasa ta dukan cinyarta cikin jin haushi, kai da kawo ta fara a d'akin tana tunanin abinyi, da sauri ta zabura ta tafi da sauri zuwa fita kafin tayi wani laifin, haka ta ratsa mutane ta fita ta same shi.

Tunda ta shiga motar babu wanda ya kula wani har suka kai gida, ta riga shi fita ta nufi hanyar shiga cikin jiki a sanyaye, taji sanda ya rufe motar amma bata juyowa ba, sai ji kawai tayi ya fizgeta zuwa cikin gidan da sauri kamar zata kifa k'asa, saida ya tsaya zai bud'e k'ofar da makullanshi ta samu ta durk'usa kan gwiwoyinta ta rik'e k'afarshi tana fad'in "Dan Allah yah Ammar kayi hak'uri, ni wallahi raina bai b'ace ba."

Uwar d'aki ya shiga da ita ya shiga bata horo kan abinda ta masa, horon bala'i wanda ta wani fannin gwara duka dashi, ya gama gigitata tare da galabaitar da ita, zuwa ne na k'eta da bak'in ciki yake mata, saida ya gaji dan gaban kanshi kuma ya koma kimtsata da rarrashi wai tayi shiru ta yafe masa.

Haka Ummy tayi ta kiranta tana ina sai shi ya fad'a mata ai tana gida, a hassale Ummy tace "Uban me take gidan to bayan nan ana nemanta?"

Cikin rarrashi yace "Kiyi hak'uri Ummy zata dawo anjima."

Cikin fad'a tace "To me taje yi a gidan ne wai?"

Cikin nutsuwa yace "Ummy ibada ta zo, kuma ni da kaina na kawota."

Kashe wayar tayi ba tare data k'ara jan zancen ba, kallon Hamna yayi dake kusanshi ta zuba masa ido yace "Lafiyar kallona?"

Da sauri tayi k'asa da idonta, k'ura mata ido yayi shima yace "Kina lafiya?"

Ba tare data kalleshi ba tace "Bana jin dad'i k'asa, ka mayar dani gida ina so na ga Ummy."

Kamar daga sama kawai taji ya bud'e mata k'afafu ya zura hannu yana fad'in "Bari na duba ki watak'ila k'ari kikayi."

Rintse ido tayi tana jin zafi duk inda ya tab'a, saida taji ya ciro hannunshi ta bud'a ido, gani tayi ya kafeta da ido yana kallo, jawo kanta yayi cikin kunne ya rad'a mata "Kin fiye zak'i da d'and'ano ne, uwa uba ga ruwa."

Kamar yau ne haka ta fara faruwa kawai sai taji kunya ma ta rufe ta, sunkuyar da kai tayi hakan yasa ya sumbaci goshinta yana fad'in "Kankana ta uwar ruwa, a ci gaba da shan kankana ba d'aga k'afa, ni ma ba zan gaji da kawota ba, haka kuma ba zan gaji da tsotsar ruwana ba."

Mik'ewa yayi ya shiga d'akin daya ware na magunguna, ba jimawa ya fito sai ji tayi ya kwantar da ita yana gyara zare da allura, da sauri ta tashi tana fad'in "Me za kayi kuma?"

Hararanta ya shiga yi sama da k'asa yana fad'in "D'inki zan miki, kin k'aru Hajiata."

Girgiza kai ta shiga yi tana fad'in "A'a wallahi bana so, ni ka bari Ummy na zata min, bana so gaskiya."

Sake kwantar da ita yayi yana fad'in "Ni kuma ga mahaukaci kullum sai mu tsaya Ummy ce zata dinga d'inke b'arnar da d'anta ya aikata ko? Ai ko ban iya d'inkin ba kinsan na koye shi dan na dinga gyara kayana da kaina, bare kuma na iya har tiyatar zuciya na iya."

Tana kuka tana k'ari tana ihu tana bata so tana rirrik'e shi haka ya mata d'inki uku, saida aka gama ta yunk'ura da k'yar ta tashi zaune wai sai gani tayi yana share hawaye (D'an iska rairai neπŸ˜‚), da mamaki tace "Lafiya kake kuka kai kuma?"

Kawai fad'awa yayi kan k'afafunta har da jan majina yana fad'in "Wallahi tausaya miki nake, akwai zafi d'inkin nan, sai naji kamar a zuciyata nake soka
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment