Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

har ya kasa iya aiwatar da komai, bud'a idon yayi ya sauke kanta yace "Kunna fitilar."

Rintse ido tayi, har ga Allah tasan inta juya saiya kalleta, fuskantarshi tayi sai kawai ta dinga yin baya baya tana nufa wajen kunna hasken, murmushi ya dinga yi yana kallon fuskarta a ranshi yana godiya ga Allah data rufa masa asiri ta juya bayan, dan shi fa ko matarsa idan zata juya masa bayan nan sau dubu sai yaji buk'atarta sau dubun, kuma yana tsoron sake faruwar al'amarin a bisa wasu dalil...Hasken d'akin daya kawo ne ya katse masa tunaninsa ta hanyar kallonta.

Da kallo ya bita ta shige madafa, wayarsa ya fito yana dannawa yana jiran fitowarta ya sata dariya ko hankalinsa ya kwanta.

Ta d'an jima kafin ta fito rik'e da robar jiya da k'aramin towel, har gabansa ta aje masa ruwan kafin tace "Wai inji ta ka ci abinci ka gasa k'afarka sannan kasha magani."

Murmushin gefen labb'a ya mata yace "Ashe kema kina jin maganar zuciyarki akai na?"

Da sauri ta d'ago kai ta kalleshi da sauri kuma tayi k'asa da kanta saboda kallon da yake mata, ganin tayi k'asa da kanta yasa yace "Mai ladabin kunama, yanzu sai kin tashi zaki fita ki juyo ki ce min Allah ya isa ko?"

A hankali ta girgiza kai tace "A'a, me ka min da zan maka Allah ya isa?"

"Kinfi kowa sani." Yana kallonta, mik'ewa tayi zata fita yace "Baki k'arasa ladanki ba ai, ki zuba min abincin idan kin gama ki gasa min k'afar tawa, ko ba abinda tace kiyi ba kenan."

Yamutsa fuska tayi tace "Ni ce zan gasa maka k'afar? To ba haka tace nayi ba, wannan ma saida ta rok'e ni nayi."

Sakar masa duka giman idonshi yayi wanda hakan ya tsorata ta, ba shiri ta matso tace "Zan zuba to."

Durk'usawa tayi ta fara zuba abincin, yana kallonta cikin taushin murya da alamar gaskiya ya karkace kai yace "Kiyi hak'uri Hamna, ki yafe min kinji."

D'agowa tayi ta kalleshi babu alamar annuri a fuskarta tace "...


*Alhamdulillah*
14/10/2020 Γ  00:58 - Ummulkhairi: πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨
*BADAK'ALA*
πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨

*Labarin Gaske*

*NA*

_SAMIRA HAROUNA_

*Litattafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._

*SADAUKARWA GA*

πŸ‘¨β€πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘¦ _*AHALI NA*_πŸ‘¨β€πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘¦

πŸ’«βœ¨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🀝

β˜† *[ T.M.N.A]* β˜† πŸ“–πŸ–ŠοΈ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_

_53_


"Akan me zan yafe maka?"

Cikin ladabi yace "Akan komai ma dana miki wanda ya tsaya miki a rai kike kallona da shi."

Wata dariyar ka raina min hankali tayi tace "Abubuwan fa dayawa, ba zan iya ba gaskiya."

Cikin wata siga yace "Yanzu kankana ba zaki iya yafe wa d'an uwanki ba? So kike mu tsaya gaban Allah ya mana hisabi? Ashe dama ba sona kike ba da kike so Allah ya k'ona ni, shikenan nagode."

Rumgume hannayenshi yayi ya turo baki gaba alamar yayi hushi, kallonshi tayi ido cikin ido tace "Bana so gaskiya."

"To ki yafe min." Ya fad'a da k'arfi yana gyara zama, girgiza kai tayi alamar a'a, dan haka ya d'ora gwiwar hannunshi kan cinyoyinshi yace "Saboda me?"

K'asa tayi da idonta tace "Saboda suna dayawa."

Cikin kafeta da ido yace "Fad'a min guda goma naji wanda suka tsaya miki a rai, ni kuma na miki alk'awarin duk'awa har k'asa na nemi affuwarki."

Saida ta aje masa abincin gabanshi ta
tsiyaya ruwa ta aje mishi sannan ta kalleshi tace _"Ranar da mukayi fad'a da Amna ka hukunta mu ta hanyar samu tsayuwar awa uku ba tare da mun motsa ba, a gaskiya ranar naji haushinka, saboda babu irin hak'uri da magiyar da bamuyi maka ba amma baka k'yale mu ba, sannan bana manta ranar daka sameni da saurayi na k'ofar gida kawai ka dinga zagina shima ka kore shi kace wai an min miji kuma mahaukaciya ce ni ya daina kula ni, har saida nayi kuka ranar fa."_

Cikin jin haushin ta ambaci saurayinta, wai saurayinta ko kunyarshi bata ji yace "Yanzu ma ashar d'in zan daddana miki idan kika kuma kallona kika fad'a min wai saurayinki."

Kallonshi tayi tana k'yabta ido yace "To naji ci gaba."

Cikin turo baki gaba tace "Shikenan ma kawai na yafe k'ananan laifukan amma ban yafe manyan laifukan ba."

Mamaki ne yasa shi bud'e baki yace "Wanene kika yafe to wanene baki yafe ba?"

Saida ta mik'e tsaye tana d'an jan siket d'inta sama alamar dakawa zatayi da gudu sannan tace "Kamar mari wanda ka min ba adadi, duka idan munyi laifi da zagi, sanda ka kusa sa min k'adangare a jiki, d'ora ni saman bishiya duk na yafe, amma ban yafe manyan ba har da keta min haddi na da kayi."

Juyawa tayi da k'arfi zata zuba a guje yace "Dawo nan, in kika fita Allah saina biki."

Tsayawa tayi ta juyo tana kallonshi kamar zatayi kuka, kujarar dake gefe ya nuna mata yace "Zauna nan."

A hankali ta lallab'a ta zauna tana satar kallonshi, saida ya fara cin abincin kamar ba zai kulata ba kafin ya kalleta yana tauna lomar bakinshi yana fad'in "Wai ke kika haifi barewa ne ko kuma ita ta haifeki da ba kya gajiya da gudu?"

Girgiza kai tayi ba tace komai ba, d'orawa yayi da "Zaki je asibiti ki taho tare dasu."

Wani irin kallo ta masa, ta d'auka fa zai sake jadadda neman afuwarshi ne, amma ya canza maganar zuwa wata daban, mik'ewa tayi saida ta kai k'ofa ta juyo, rik'e da cokali ta ganshi zaisa bakinshi amma bai kaita bakin ba yana kallonta yana jiran ta juyo ta fad'i abinda zata fad'a, ai kuwa saida ta shirya gudu sannan tace "Ai ba sai ka fad'a min zanje ba, yer uwata ce ita baka fini sanin abinda ya dace na mata ba."

Sakar mata ido kawai yayi yana kallo har ta fita a b'angaren, murmushi yayi mai sauti yace "Duka manyan ma zaki yafe Hamna da zaran kinji matsa."


Tare da ita suka tafi asibiti kuma suka dawo tare, tana rik'e da macen jaririyar (ni dai bansan sunan da zan kira yaran nan na Ammar ba dan ya birkita min lissafi) suka shiga ciki, aje yarinyar tayi ta d'auko katifa ta mata shinfid'a a falo, inda Soueiba kuma ta d'ora mata ruwan wanka sai Zeituna data shiga kawo mata abinci mai lafiya da gina jiki, bayan ruwan sun tafasa ta shiga wanka su ma yaran aka fara musu ana canza musu kaya, ya shigo gidan da k'atuwar leda da kayan bebys ciki, Amna dake shan tsumagiyar kaba a hannun Husseina tana mata wanka ce ta dasa wata k'ara tana fad'in "Zafi, zafi Hajia ba zan iya ba, bana so wallahi ya isa haka."

Kallon Zeituna yayi dake shafawa yarinyar kwalli yace "Uwa me take ma kuka ita kam?"

Dariya tayi tace "Wanka ne ake mata."

Zaro ido yayi yace "Da tafasashen ruwa halan?"

Kai ta d'aga masa hakan yasa shi zabura ya nufi ban d'akin dake cikin falon yana fad'in "Na rantse da Allah babu mai toya min mata kamar yar wuta, ta gama azabar nak'uda kuma ta koma shan ruwan zafi, anya kuna da imani kuwa?"

Soueiba ce tace "Ammar mu ne marasa imanin da muke taimakawa matarka? Kasan dai inba wankan nan aka mata ba da kanka wata rana zaka ce a mata shi."

Juyowa yayi yace "Haba tanti, ni d'in banza da zan kiraku da marasa imani."

Ban d'akin ya shiga saida Husseina taji tsoro, ita kanta Amna kunya ce taji ta kamata, kallon Husseina yayi da tace masa "Lafiya Ammar? Wani abu kake so?"

Cikin taushin murya yace "Hajia bari na k'arasa mata wankan nan, naji sai ihu take mana daga wankan da bai taka kara ya karya ba."

Tsaye ta mik'e rik'e da kabar hannunta ta kalleshi sai ta rasa me zata ce mishi ma, Amna na jin haka tace "Hajia ci gaba dan Allah, yah Ammar ka fita zan tsaya yanzu."

Ummy na shigowa aka ce mata ya shiga kawai tabi bayanshi, tana zuwa ta tsaya bayanshi tace "Bawan Allah ko zaka iya basu wuri suyi abinda ya dace?"

Juyowa yayi yace "Me zai hana kuwa Ummy."

Kallon Husseina yayi yace "Ayi wanka lafiya."

Juyawa yayi kamar zai fita saiya sunkuya cikin kunnen Amna yace "Karki bari ta k'ara k'ona min ke wallahi, inba haka ba ita ma saina mata wankan jegon nan, haka kawai ba za'a barki ki huta ba."

Mik'ewa yayi ya fita Husseina ta bishi da kallo baki bud'e, kallon Amna tayi da mamaki tace "Anya kuwa Amna mijin nan naki zai bari a miki abinda ya kamace ki?"

Ita dai k'ala ba tace mata ba kawai tana jiran taji saukar ruwan zafin, ko da ta gama shiryawa ma tuni gidan ya fara gaurayewa da yan barka.

*Da dare* Jumare ta zo tare da Jumma suka ga yara suma, suna fita lokacin Hamna ta raka k'awarta Amie data zo ita ma, kusan a tare suka fita sai Ammar daya zo zai shigo, yana ganin Amie yace "Lah budurwata ce? Kina lafiya?"

Kallonshi tayi ita dai har ga Allah matashin ingarman saurayin na birgeta, ko yanzu idan zai fito da niyyar aurenta saita aure shi, amma matsalar d'aya ta fahimci mutum ne da kanshi ke rawa, murmushi ta masa tace "Angon jego kasha k'arni, barka to Allah ya raya."

Murmushi ya mata yana sunkuyar da kai yace "Har kin sani jin kunya wallahi, to ameen dai tunda addu'a kika min."

Murmushi tayi ita ma ta mik'a masa hannunta tace "Ina tayaka murna sosai."

Hannunshi ya mik'a mata shima suka gaisa yana fad'in "Nagode sosai, yanzu ya labarin soyayyarmu?"

Sosai tayi murmushi tace "Labarin soyayyarmu kai zan tambaya."

Saida ya kalli Hamna wacce ko da taga hannunshi da nata sun had'u taji bak'in ciki da wani mak'ok'on abu ya taso mata ta fara hararensu, Jumma da Jumare dake gefensu ne Jumare tace "Inna ashe d'an iska ne, kiga fa gaisawa yake da ita."

Cikin sassauta murya Jumma tace "Rufa mana asiri Jumare karki sa ya jefa mu kurkuku."

Kafin ya bawa Amie amsa ya kula dasu Jumare suna kallonsu, Jumma ce tayi saurin cewa "Ina wuni yallab'ai, dama Zeituna ce ta fad'a mana an samu k'aruwa shine muka zo barka, Allah ya rayasu akan sunna, saida safe."

Daga yanda take magana ya nuna masa har yanzu a tsorace take dashi, cikin sakin fuska da fara'a ya amsa mata da "Lafiya lau, mun ko gode Allah ya saka da alkairi, ina baban namu?"

Jumma ce tace "Malam yana gida yace dai a gaisheku."

"Muna amsawa." Saida suka fara tafiya yace "Budurwata ya kike?"

Tsayawa Jumare tayi wanda hakan yasa Hamna da Amie kallonta da kyau, tab'e baki Hamna tayi taja hannun Amie tace "Muke kinji, wannan duk yan matan garin nan ina ga fa nashi ne."

Ita dai wuk'il ta masa da ido kawai sai shi daya matsa kusanta yana mata shak'iyanci wai saita fad'a asa tana son sa, Jumma ma dai matsawa tayi nesa dasu ta basu waje, saida Amie ta samu adaidaita sannan Hamna ta dawo, nan ta same su tsaye saida ta harareshi sannan ta nufi cikin gidan, yana ganin haka yace "Ke zo nan."

Abinda ta tsana a duniya yace mata ke, kuma a gaban yarinyar nan yar k'auye zai ce mata ke zo nan, da k'arfi ta juyo cikin b'acin rai ta tsaya gabanshi tace "Gani lafiya?"

Murmushi ya mata dan yana son cikata yace "Daga ina kike?"

Saida ta sake had'e fuska tace "Daga inda ka aikini mana."

Kallon Jumare yayi yace "Kinji gani ko? Da ita ce zan aura to matsalar k'walwa gareta, shiyasa nake so na aureki Jumyta dan naga uwata Zeituna tana da hankali nasan ke ma kamar ita ce."

Bud'a baki tayi zatayi magana sai kuma ta kasa ta kalleshi da tsananin mamaki ta kalli Jumare data kalleta, sake d'aga labb'enta tayi sai taji sun mata nauyi, amma fa ya wulak'antata mutumin nan, kallon Jumare tayi rai a b'ace cikin d'aga murya tace "Ke bar nan wajen kafin na miki dukan tsiya."

Baki Jumare ta saki kawai saita yarda da abinda ya fad'a, ganin ko niyyar barin wurin ba tayi ba yasa ta sake d'aga murya tace "Zaki b'ace ne ko saina karyaki a wurin nan."

Da sauri Jumare ta wuce sai kuma ya bita da dariya, yana cikin k'yalk'yala dariya ya kalleta sai kuma yayi tsitt kamar ba shi ba, saida ta harareshi sama da k'asa tace "Idan ni mahaukaciya ce kai kuma fa? Mai kula dani?"

Tsaki tayi ta shige cikin gidan inda ya sake bushewa da dariya yana cije leb'en kasa shima ya shiga, kai tsaye b'angarensu ya nufa, tun a k'ofa yake jin kukan Amna k'arama, yana shiga ya ganta hannun Amna sai nono take saka mata tak'i karb'a sai harshenta ke rawa tsabar kukan da take cancarawa, kakanni kam sai sharri ake mata suna kiranta da mai la'ana kamar uwarta, tak'im tak'im yaje gabanta yasa hannu ya amsheta ya fara jijjigata ya nufi d'aki da ita, bayanshi Amna tabi dan tana so ta fad'a mishi abinda take so, yana jin motsinta a bayanshi ya juyo yace "Wai me aka mata ne take wannan kukan?"

Kafin ta bashi amsa yaja hannunta ya zaunar da ita bakin gado ya d'ora mata ita a k'afa yace "Bata tasha."

A hankali ta fito da nonon dake mak'ale a k'irji ta d'aga kan jaririyar sosai tana so ta sa mata, amma daya shiga bakinta sai tak'i kamawa, cikin d'aga murya yace "Wai lafiyarta k'alau kuwa? Naga lafiya lau take yau."

Kallonshi tayi tace "Yah Ammar kawai fa dan an mata hujen kunne ne take wannan kukan?"

"Me?" Ya fad'a da k'arfi yana k'are mata kallo, cikin yanayin da yake nuna zai iya tabka rashin mutumci yace " Amna wannan yarinyar ce kika sa aka ma hujen kunne? Kuma shine har kike cewa wai dan an mata, wai ma ne kenan?"

Nufa yayi wajen coiffeuse (dressing miror) yana fad'in "Yau na tabbatar da ke baki da hankali har da ma wacce ta mata hujen, amma zan nuna muku ni na dameku na shanye wallahi, inba raina mutane ba yarinyar da aka haifa jiya, ke kikayi nak'udarta amma a gaban idonki ana juheta kina kallo, to ko de bake kila haifeta bane?"

Ya juyo yana kallonta, ita dai kallonshi take tana so kuma ta kama nonon, tana kallonshi ya fito da yan kunnanta na ziraniya da Hajia ta siya mata da kud'in daya bayar ya nufo kanta, ita dai bata san me zaiyi ba ta kuma kasa tuna girman abinda zai aikata, karb'ar yarinyar yayi ya aje gefe duk kukan da take kuwa, idonta ya kalla ya rik'e k'ugu yace "Ke mahaukaciyar ina ce Amna?"

Cikin fara tsorata da yanayinshi ta fara matso k'walla ta girgiza masa kai, nuna k'aramar Amna yayi yace "To uban wa yace ki yarda a mata huje tun yanzu? Waje zaki fara aikata ne tun yanzu da kike son ganin ta fita da kyau? Ko kuma idan ba'a mata yau ba shikenan zata mutu ne? Me zaisa ba za'a bari har ta k'ara wayo ba? Kawai tsabar rashin imani irin na ku Amna ku kama min 'ya ku huje mata kunnuwa, kuma ni abun bak'in cikin ma shine a gabanki, kuma wai har kike cewa wai dan an mata huje, kiji fa wai dan an mata."

Saida ya saita d'an kunnan hannunshi ya fizge hijabinta yana k'ok'arin rik'o kunnenta yana kallon yarinyar da har yanzu ke kuka yana fad'in "Ke yi shiru abinki yarinyata, da ubanki fa a raye waye zai takaki a garin nan? Ai ban ganshi ba na rantse da Allah, bari kiga yanda zan d'au maki fansar cin kacar da aka miki, yo mu rashin mutumci ai gidanshi ne aka zo har na siyarwa muna da."

Amna na ganin yana shirin burma mata kunne huje na uku kenan dan dama biyu garesu ita da Hamna, zabura tayi zata bar wurin ya kwantar da ita kuma tsaf yayi zaune kan ruwan cikinta, had'e hannayenta tayi wuri d'aya cikin fad'uwar gaba da kuka tace "Dan Allah yah Ammar kayi hak'uri, Allah wallahi ba zan sake ba na rantse maka."

Juya fuskarta yayi ko saurarenta baiyi ba ya saita daidai huje na biyu wanda ke sama ya turtsa mata d'an kunnen nan, wata uwar ihu ta saki jin abun ya zo mata bata shirya ba, cikin azaba da rad'ad'i ta fara fad'in "Dan Allah kayi hak'uri ba zamu k'ara ba yah Ammar, zan mutu wallahi dan Allah ka d'aga ni na tuba wallahi."

K'ok'arin juyo d'aya b'angaren ya shiga yi yana fad'in "Yo ku k'ara mana, ai ba musaki bane ni da zan kasa rama mata ba."

Da k'arfi ya juyo d'aya b'angaren ya janye hijabinta nan ma ya jawo kunnen ya saita shi, shima burmuk'a mata yayi na uku kafin ya d'agata yana d'aukar yarinyar yace "Shiru shiru yar baba, tuni ubanki ya d'auki fansa, a shirye muke da duk abinda zai faru ya faru, ba tsoron bala'i muke ba."

Ummy da taji kukan yarinyar ya k'i k'arewa kuma k'arshe taji na uwar yasa ta shigowa d'akin ko sallama ba tayi ba dan tasan d'anta ne ke wani mugun abun, ai kuwa ta samu Amna sai sharar hawaye take da hijabi tana rufe kunnenta, matsowa tayi tana musu kallon tuhuma tace "Me ka mata ita kuma?"

Kallonta yayi yace "Ki tambaye ta Ummy tasan abinda tayi."

Kallon Amna tayi tace "Me kika mishi?"

Cikin rage sautin kukan tace "Ba komai Ummy, marata ce ke ciwo."

Kallon tuhuma ta masa dan bata yarda ba, jinjina kai tayi tace "Karb'i yarinyar ki zo falo to."

Mik'ewa tayi ta tara masa, saida ya kalli idon Amna yace "Gata nan amana na baki, aka sake cutar min 'ya sai ranki ya b'ace."

Juyowa Ummy tayi ta kalleshi jin abinda ya fad'a, shima kallon Ummy yayi yace "Ummy waya ma yarinyar huje saboda Allah?"

Da d'an mamaki tace "Tantinku ce *Zuweira*, da matsala ne?"

Jinjina kai yayi ya nufi kan gadon ya d'auki yan kunnen daya ma Amna huje dashi yace "Yau ko zata ga rashin mutumci wallahi, dama ba shiri muke da ita ba saboda tana kirana da mai kamar shaye shaye, to yau zan mata aikin da ko mai shan cocaΓ―ne ba zai mata ba."

Da sauri Amna ta rik'e rigarshi ta baya ta kalleshi tace "Dan Allah yah Ammar ka rufa masa asiri, kasan halin tanti Zuweira fa."

"To sai me? Ita tasan nawa halin amma kuma ta aikata min wannan ta'asar."

Ummy dake kallonsu cikin rashin sani ne tace " Wai miye ya faru?"

Da sauri Amna ta kalleta tace "Ummy dan Allah ki bashi hak'uri karya je."

Kallonshi Ummy tayi tace "Miye wai?"

Ba tare da fargaba ba yace "Ummy huje aka mata bata isa ba, shine zan rama mata."

Zaro ido tayi ta matso kusan Amna ta d'aga hijabinta, tana ganin kunnenta ta kalleshi rai a b'ace tace "Me kayi haka Ammar? Me yasa wai kai duk abinda ya sab'a ma hankali shi kake aikatawa? Hujen daya zama dole dan an ma yarinya shine ka rama kan uwarta, me kenan hakan ke nufi? Ka fita k'aunarta ne?"

Cike da rashin ko in kula yace "Haka aikinta ya nuna bata k'aunarta."

Cikin jin haushi ta nuna mishi k'ofa tace "Fita a gidan nan, ko ko k'ala ban yarda ka fad'a ma Zuweira ba in dai ni na haifeka."

Saida ya rusuna yace "Angama."

Fita yayi yana zuwa falo yayi tsaye yana kallon Zuweira dake shan kunu a babban roba tana ta hira abinta, saida ya rik'e k'ugu ya dinga motsa bakinshi yana fad'in "Shirgegiyar wofi, ki samu yar jaririya ki taushe da uwar cinyarki ki mata hujen, kuma tana kuka hankalinki kwance kina shan kunun da ubanta ne ya siyo hatsin yake biyan ruwan da aka dama kunun, kai amma matar nan fa akwai yar rainin hankali, yau kinci albarkacin Ummy da sai na cire miki zaninki ta kai, amma ba komai ai akwai wata rana."

K'wafar da yayi ce tasa hankalin wasu dawowa kanshi wanda basu kula dashi ba, Ummy suna fitowa tana fad'a ma Amna cewa "Kiyi hak'uri kinji, kar ma ki bari kowa ya sani, ki k'yale shi kawai."

*A gurguje fan's*


Komai ya tafi daidai inda Ammar yayi iya bakin k'ok'arinsa wajen gwangwaje amaryar jego da yaranta, saida ya mata d'inki kalar shida na tanfatsa tanfatsa leshi da shadda, ranar suna kuma kamar yanda ya fad'a ne sunansu ya mayarwa yaranshi, ranar biki gidanshi dake nesa da nan suka zauna shi da abokansa inda Amar dasu Junaid suka d'auki nauyin abinci da abin sha. A gida kuma ko Hamna saida sukayi d'inki har kala uku ita da Amna, anci an sha anyi bidiri sosai an gode Allah sai fatan Allah ya raya yaran.

Bayan kwana shida kuma akayi bikin Jamila ita ma, bayan biki Zeinabu ta so ta koma d'akinta sai Jibril yace kawai su barta har ta gama wankasaita koma. Umaimah ce kawai yanzu ake jiran haihuwarta, cikin ikon Allah kuma saida ta shiga wata na goma sannan ta haifi 'yarta ita ma masha Allah, haka akayi shagalin sunanta aka gama lafiya.

Kwana biyu da kammalawa Hamna ta rok'i Hajia ta barta ta tafi Abuja wajen koyon kwalliyarta, ta tafi kuma tana yin abinda ya kaita cikin kwanciyar hankali, sati biyu ta d'auka kafin ta dawo gari, Gambo dake hushi da ita na tafiyarta basu sani ba ne ya sauka yanzu da sa bakin Hajia ya bud'e mata gwangwajejiyar salon da babu abinda babu, sabuwar duniya kuma sabuwar rayuwa gareta, tana zuwa aikinta kuma tana yinshi da himmada kulawa saboda tana so, tana iya zuwa ko ina saboda yi wa wasu kwalliya kamar amarya ko mai jego.

*Shekara d'aya*

A cikin shekara d'aya abubuwa dayawa na ta faruwa, wasu na farin ciki wasu na bak'in ciki wasu na jimami, Hamna kuma yanzu mota take hawa tana murzata duk inda take so, sai dai har yanzu taka tsantsan take wajen nunawa yaronta soyayya, wanda yanzu ya saba da ita sosai yana kiranta da *Tata*, lokuta da dama idan ta ga Ammar da yer uwarta suna rayuwar farin ciki sai taji kowa a gidan yana bata haushi, takan ji kamar an daketa kuma an hanata kuka ne, amma aikinta yana d'an d'aukar hankalinta zuwa wani wurin.

Yau ma kamar kullum ko da Amar ya shigo ya samu Umaimah a yanayin daya fi samunta kullum, tsaki kawai yayi ya shige d'akinshi bai kulata ba, saida gabanshi ya fad'i ganin Farisa k'anwar Jibril ta zage tana gyara shinfid'ar gadonshi, cikin mamaki yace "...


*Alhamdulillah*
14/10/2020 Γ  00:58 - Ummulkhairi: πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨
*BADAK'ALA*
πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨

*Labarin Gaske*

*NA*

_SAMIRA HAROUNA_

*Litattafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._

*SADAUKARWA GA*

πŸ‘¨β€πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘¦ _*AHALI NA*_πŸ‘¨β€πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘¦

πŸ’«βœ¨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🀝

β˜† *[ T.M.N.A]* β˜† πŸ“–πŸ–ŠοΈ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/


_Bismillahir rahamanir rahim_

_54_


"Farisa me kike yi a d'aki na?"

Ba tare data d'ago ba ta juyo dan ganinshi, hakan ne yasa rigarta dake da sakakken wuya k'irjinta ya fito har yakan iya hango matashiyar inda nononta suka taso, lumshe idonshi yayi ya d'an kawar da kanshi yana sauraren muryarta da yaji yau ta masa daban tana fad'in "Sannu da zuwa yah Amar, aunty Umaimah ce tace na gyara maka d'akinka."

Bud'a idonshi yayi ya sauke su kanta, wani tartsatsi yaji tare da mummunan fad'uwar gaban da baisan da zuwanshi ba ya ziyarce shi, daga k'asa har sama ya kalleta kamar yau ne ya fara ganinta, yarinyar duka shekara ta sha biyar ce take ciki yanzu, amma da yake tana da girman k'asusuwa saika d'auka ta wuce shekarun, a yau dai kuma a yanzu take sai yanzu kibiyar sonta ta harbeshi babu shiri, da fari yayi niyyar mata kashedin karta sake shigo mishi d'aki ne, amma ganinta a cikin riga da siket na katin da suka karb'eta sun tafi da masifar da
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment