Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

haba Ummita , kema kina da neman fitina ana kwatarki a hannunsa amman bakinki ba zai mutu ba ,a she kema dai da na ki halin ake ganin nasa" ? Kuka take sosai har da shesheka jin abinda ya Abdurrahaman yace , bakin ya rayhan ya mutu ya rasa me zai ce sai kare ummita yake dan kar maaruf ya ƙara mata

Sai daya furzar da iska mai zafi kana yace "ka mata gargadin ," ta kiyayi min rashin kunya ,ta daina faɗa min duk abinda ya fito daga bakinta ,kai ko aurenta kayi ,kayi make sure bata shiga hurumina ba, idan kuwa tayi ganganci sai na... .?"
" me zai faru Ma'aruf ?
"Enough Ma'aruf
bana son haka ,banason abinda kake min wannan ya zamo karo na karshe da zaka sake marinta a gabana ,bana jin zuciyata zata cigaba da daukar haka" .....
"Kai rayhan ina ruwanka?
" ban gane ina ruwana ba ta yaya zai dinga mata izaya irin haka, kalli yadda ya rike mata naman ciki yana ƙoƙarin illata yarinyar mutane "

" ai kana ji kuma kana gani tunda kai ba makaho bane
abinda tayi a yanxu agabanka ne kuma har yanzu bakinta yaki mutuwa amman da yake bakason gsky kake hakikance wa "a'a Inna karki ce haka ai ba karfinsu daya"
ba inji cewar ya Abdurrahaman "yi min shiru anan ,ka wani k'ame da wani gutun gemunka irin na munafukai"
""tsit ya Abdurrahaman ya kama baki yayi shiru cike da mamaki yana kallon Inna " babana Sau dubu ta zageka sau dubu kayi mata dukan mutuwa Ni na saka kuma babu abinda za'a yi ,ko ubanta bai isa ba bare ku"...

" Wannan ai daurewa karya gindi ne ,sam ba'ayin haka ,ai yanzu a gabanki nayi mata faɗa ,nasan itama da nata ,amman nashi yayi yawa .. Ma'aruf bai ce komai ba ya koma ya zauna yana huci ..
"To be the last time da zai kai hannunshi jikinta wani kallo Ma'aruf ya watsawa rayhan cikin yanayin maganarsa a hankali "ka canza tunani ɗaukar mataki babu abinda zan mata matukar zan faɗa tayi shiru ,duk sanda zan faɗa ta faɗa sai na taɓa lafiyar jikinta naga abinda za kayi"

Ummita da gudu ta juya tayi part dinsu tana kuka ko kallon mutane dake Parlourn bata yi ba , ta wuce ɗakinta tana kuka tana magana " ya Abdurrahaman me sonta shima ana so a shiga tsakaninsu , tunda bai taba mata faɗa ba sai gashi yau har da bata rashin gaskiya ita kuwa Inna dai so take kowa ya tsaneta ko cikakken minti goma batayi ba ya rayhan ya shigo "come on my princess ya fad'a tare da jawo hannuta sai lokacin tasan ya shigo haɗa ido sukayi na minti biyu wanda suna iya jiyo numfashin juna tuni idanunta suka sake kadawa "kiyi hakuri my princess komai lokaci ne ,shiyasa nake son kibani dama na daukeki na killace ki a gidana idan na aure bazaki sake zuwa gidan ba sai na tabbatar da Ma'aruf bai gida ,bazan bari ki haɗu dashi ba bare ranki ya baci .... ....kafin haka zan so ki fita harkarsa duk abinda zai yi karki sake kula sa ko daga kai ki kalleshi shi din kamar mahaukaci yake idan yana faɗa ana faɗa kin san halinsa ba tun yau ba sai kici maganin zama dashi sosai ya rayhan ya dinga mata nasiha yana kwantar mata da hankali har ta samu natsuwa "


waje kuma Ma'aruf ne da Abdurrahaman sukayi niyar zuwa masallaci sallah, suna tafiya Abdurrahaman na bashi hakuri da fahimtar dashi abubuwa da yawa akan ummita saboda yaga kamar ransa ya 'baci sosai ,"ka daina tsanarta haka Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama yace "idan zaka so mutun ka so shi kaɗan saboda wata rana zai iya zama makiyanka haka zalika idan zaka ki mutun kaki shi kaɗan saboda watan zai iya zama mayinka , ma'aruf ummita jininka ce halak malak ka daina cin zalinta ka guji ranar da hakkinta zai bibiyi rayuwarka ,, ina tabbatar maka zakayi nadama ranar da hakurin mama ya kare saboda kana kin yarinyarta ne without any reason ,sam ma'aruf baya ma sauransa gaba-daya hankalinsa yana wani gurin .....
******


Da daddare da misalin karfe bakwa da rabi hajiya ummah mahaifiyar Ma'aruf tasa aka yi mata kiranshi ,a hankali ya shigo bakinsa ɗauke da sallama ta amsa a ciki batare da kalleshi ba ,ya samu guri ya zauna
agabanta a kan kafet a babban parlour'n ta ya tankwashe kafafunsa sanye take cikin fari dogon wando da red din riga mai karamin hannu sai farar facing cap daya daura a kanshi duk cewar kayan shan iska ne na gida hakan bai hana kayan suyi masa kyau ba ..ganin yadda hjy umma ta haɗe rai yasa gabansa faduwa jikinsa a sanyaye ya gaisheta wannan karon ma aciki ta amsa idanunta cike da damuwa sosai ta maida gabadaya hankalinta a kanshi a matukar fusace ta soma "Ma'aruf ya d'ago ahankali ya kalleta a tsorace dan yasan duk abinda yasa tayi kiran sunansa kai tsaye abu ne mai mahimmanci ,dan ita mace ce mai tsananin hakuri da kawaici sannan bai taba jin ta ambaci sunansa ba ,wannan shine karo na farko "dan haka ya tattara duka hankalinsa akanta "hjy umma ya bata rai sosai "wai yaushe zaka canza ne ?
Yaushe zaka daina musgunawa yarinyar mutane ?

"Me yasa baka da alkunya da sanin yakamata?
Ahankali ya sunkuyar da kanshi saboda fahimtar inda maganarta ta ta dosa "sam baka da alkunya wallahi yarinyar nan fa bata da wani dan'uwa mafi kusanci da sukayi rayuwa a daki daya sai kai ,idan baka sake daita ba dawa zaka sake ?
"Kullun kana dakin uwarta amman saboda baka da mutunci itace abar wulakatawa gareka "me yarinyar mutane ta maka ?yayi mata shiru yaki cewa komai " tambayarka ne dan ubanka kabani amsa me tayi maka ?
"Bata jin magana ne sannan bata da kunya .."shikenan dalilin ?ya daga kai yana shafa sumar kanshi "kai kunyar ce da kai?
" da anyi magana kace yara basu da kunya , "to banaso takurawar ta isa haka , daga yau karka sake na sake jin ka taba lafiyarta a gidan dan bana so idan duka da zagi ya zame maka ibada kazo ga kannen naka nan ,bana so kaji na fada maka "tou hajiya ya faɗa yana dubanta "kiyi hakuri inshaallahu na daina "Allah yasa ta faɗa tana mikewa tayi cikin d'akinta jiki a sanyaye ya fito daga part din zuwa nasu ummita ya nemi guri kan doguwar kujera ya kwanta yana tunani ..
ranar ko abinci dare kasa ci yayi duk da irin faman da mama ta dinga yi dashi, tunaninshi ya tafi ne akan yadda zai yi aure ya tattara ya bar gidan gabad'aya ....

Two friend's (bsbs)

💗💗💗💗💗💗
WANNAN CE
QADDARARMU
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

~TRUE LIFE STORY~

FREE NOVEL NOT FOR SELL


AL'QALUMAN



*AYSHA A BAGUDO*
*FAIZA HAMMADU*


~DEDICATED TO~
*FAUZIYYA MB⏰*

WATTPAD @HAUESH

bismillahirrahmanirrahim


PAGE 12


" Kai ba sakaran namiji bane , dole ka sauya ,kuma dole ka dawo tsarin daya ya kamata , dole ka rarrashi zuciyarka ka danne abinda kake ji akanta sannan ka fahimce illar abinda kake aikatawa, kula ummita babban ci baya ne a gurinka , zubda aji ne mutane su dinga ji ko ganin kana sa'insa daita "wallahi wannan babban abun kunya ne a gareka" ......
idanunshi na runtse yake bawa kanshi shawara, ranshi duk a dagule ya mike tsaye a hankali yana layi tamkar wanda ya sha wani abun , da kyar ya iya buɗe bakinsa yayi wa mama sallama "mama sai da safe tare da ƙoƙarin fita daga ɓangaren gabad'aya , idanun mama na kanshi ta amsa masa "Allah ya tashe mu lafiya tana jin damuwa a cikin ranta saboda bata son ganin shi cikin damuwa .
a zafafe ya shige d'akinsa ya faɗa saman gadonsa hannunsa ɗaya dafe da goshinsa yana furzar da iska mai zafi " kar ka sake na sake jin ka shiga lamarin yarinyar mutane ,karka sake dukanta ,idan dukan ya zama dole , ka zo ga kannenka nan ka doke su , amman ita banason kana taɓa lafiyaryarta banaso" ...... maganganu mahaifiyarsa suka shiga dawo masa daki daki suna samu karɓuwa a cikin zuciyarsa naunauyen ajiyar zuciya ya sauke da karfin gaske yana fidda numfashi mai zafi " duk runtsi duk wuya bazan sake shiga rayuwarki ba ...... .ya furta hakan a kasan ranshi ..





Bangaren ummita itama kwance take a d'akinta har lokacin zuciyarta bata cikin walwala , ranta duk a 'bace yake , ta qullaci Ma'aruf kwarai da gaske a cikin zuciyarta , ba shi kaɗai ba hatta hajiya Inna tashiga sahu manya manyan makiyanta , ta san matsayinta da zata ajiye a cikin zuciyarta , ta sanyata a bagiren da babu wanda ya isa ya sauya ....
ban cin daraja mama ,da ita kaɗai tasan irin rashin mutuncin da zata shuka hajiya Inna , amman kullun maganar mama ɗaya ce gareta "kiyi hakuri ummita komai mai wuce wa ne har ya zamo labari , mai labarin ma wata rana baza'a ganshi ba , kawai ki share duk abubuwan da'ake miki matakin d'aukaka ne ,ki cigaba da addu'a Allah yana sane damu......
"bari na d'auko maka dorina mai baki shida tana tsallen kwado kana tsulawa yar banza yarinya ...
Wasu zafafan hawaye masu zafi da ciwo suka gangaro mata lokacin data tuno maganar hajiya Inna...
"Me yasa Inna ?
"Me yasa kika tsane ni haka ?
"da fari kin tsani mahaifiyata da bata rage da komai ba , kin fifita sauran surankanki akanta haka zalika kin fifita jikokinki akaina me yasa Inna ....?
Ta sake rushewa da wani sabon kuka "ki daina kuka ummita Inna da Ma'aruf ne kaɗai mutanen da suka tsaneki a cikin dangi bayansu kowa yana sonki dan me zaki damu kanki ?
"ki sharesu kiyi rayuwarki kamar kowa ,ko babu su a cikin rayuwarki zaki yi farinciki ....
Ta dade kwance tana zance zuci , kafin daga baya bacci barawo yayi awon gaba daita, da kyar ta samu ta tashi tayi sallar asuba ta koma ta kwanta .. ..

*******
Da gari ya waye ta tashi idanunta sun dan kunbura saboda kukan da tayi jiya ta ɗan dafe kanta da taji ya mata nauyi tare da sarawa kamar tana buga mata gudunma , hatta bangaren hango daidai inda zuciyarta take ji tayi yayi mata nauyi sosai sannan yana mata ciwo,




A hankali ta yaye bargon dake lullu'be da rabin jikinta ta zamo daga kan gado ta sauko ta tsaya gaban mirrow tana kallon idanunta da suka kunbura na two second sannan a hankali tayi
mika haɗe da sallati sannan ta shiga gyara d'akinta sai data gyara ko'ina sannan ta nufi bayi, ta soma da wanke baki sannan tayi wanka ta fito daure da towel tana goge jikinta har lokacin tana jin damuwa a ranta haka zuciyar bata daina mata ciwo ba .....hannu ta kai ta ɗauki man shafawarta piement lotion ta soma bin ilahirin jikinta dashi sai data shafe jikinta sannan ta nufi wordrob, ta buɗe inda bra da pant dinta suke ,ta d'auka ta feshesu da turare sannan ta buɗe bangaren kayanta ta ɗauki atamfar chigabi gold wanda aka yiwa dinkin riga da siket ta sanya ta shirya tsab ta shafa hoda kana ta fito ta rufo kofarta ta shiga dakin mama ta gaisheta "mama ina kwana ?
"Lafiya kin tashi lafiya ?
"Lafiya mama bari naje na gaida Abba na dawo "ai baya nan tun tara ya bar gidan nan tare dasu Ma'aruf ..saurin runtse idanunta tayi ,idan akwai abinda ta tsana bai wuce yadda iyayenta suke da close dashi ba tare da nuna masa kulawa ....mikewa tayi ta fito daga d'akin ta sauko parlour'n kasa ta ɗauki remote ta kunna ta,



tana zaune a dining tana breakfast meenal tashigo ,sosai ta maida hankalinta kan meenal dake ƙoƙarin karasowa inda take zaune "ummita gidan baba sarki zamu shine nace bari na zo na faɗa miki ko zaki "kuje kawai babu inda zani "
Meenal ta karaso kusa da ita sosai ta dafa kafad'arta "haba ummita karki ce haka mana, me yasa bazaki ba ?
"Ra'ayi cin buredi da sandi ko dole sai naje ....
" ni gaskiya dole sai kinje tafiya dake ai tafi dadi gaskiya, idan har da gaske ba zaki ba nima na fasa zuwa bari naje na fadawa su aunty jiddah su wuce kawai "better zauna ga guri nan muyi kallo "maza ki qarasa cin abinci kije ki canza kaya ki bita ku wuce mama ta fad'i haka tana saukowa daga step "amina jirata ta qarasa cin abinci .
"Inna kwana mama ?
Cike da sakin fuska mama tace "lafiya kalau amina yasu hajiya umma ?
"Lafiya lau kowa yake ..."
Azafafe ummita ta mike ta ture plet din abinci tayi hanyar step, taku biyu tayi ta tsaya sakamakon muryar mama data doki dodon kunneta "dan nayi magana shine kika tashi mama tayi magana, kuma dan bak'aramin so take wa ummita ba ?
" ki dawo ki qarasa cin abincin , juyowa tayi a hankali fuskarta a shagwa'be kamar zata yi kuka "ni na koshi "shikenan Allah ya shiryeki naga ranar da zaki canza ,shiyasa har abada ba zaki sha inuwa ɗaya da ma'aruf ba ,ke dai idan ba ra'ayinki ba ba zaki yi abu ba , kina da aiki domin idan kika je gidan miji kina irin wannan halin wuya zaki sha a hannunsa "a fusace ta juya tana taka step da karfi "ni babu wani aure da zanyi tayi murmushi "kai ummita rigima zauna mana amina ..

kai tsaye cikin d'akinta ta shiga, ta dauki bakar abaya ta ɗaura a saman kayan dake sanye a jikinta , ta nade kanta da mayafin abayar sannan ta ɗauki turare mai sanyi kamshi ta sake fesa a ilahirin jikinta ta karasa gurin takalmanta ta dauki cover shoe yellow mai ratsin baki ajiki ta sanyawa kafafunta , ahankali ta sauko tana turo baki tare da ƙoƙarin daurawa tsintsiyar hannunta agogo .
Meenal dake zaune a falon tana ganinta ta mike tsaye ,idanunta akanta meenal , ta kamo hannunta " kai gaskiya kin yi kyau sosai yar'uwa ina sonki ummita ta kwace hannunta tana bata rai "muje yar matsala banason dogon turanci ,kawai mutun na zaman zamansa zaki wani....
"Ni zaki zaga ba ita ba, tun da ni nayi miki dole, meenal ta sake kamo hannunta" mama mun wuce "to Amina yar albarka sai kun dawo Allah ya kiyaye hanya ku gaishesu , har zasu fita taji mama bata ce komai ba dan haka ta kwace hannunta cikin na meenal ta dawo ta rungume mama dake mike tsaye "mama kiyi hakuri ni baki min addu'a ba ..
"ai baki nema bane "to ai itama meenal bata rokeki ba ki ka yi mata " "to shikenan Allah yayi miki albarka, Allah ya shirya min ke shiri na addini muslunci sai kun dawo ,dan Allah karki yi faɗa da kowa .."naji mama amman kiyi addu'ar Allah yasa kar wanda ya shiga track dina "inshaallahu babu mai shiga tace "ameen uwa ta gari abar alfaharina ina sonki sosai mamana ta fad'i haka tana sakin mama kana ta juya ta sanya kai suka fice .....
"Ina sonki ummita , Allah ya nuna min aurenki , ya albarkace da samun zuri'a masu albarka ..

A hankali take taku kamar bata son taka kasa , cike da yanga da karairaya , har suka qaraso inda sauran yan'uwansu ke tsaye jikin mota tsayuwar jiransu , ammar na ganinta ya washe mata baki " kunga hajiya ummita gimbinbid'a ta ya rayhan kinyi kyau sosai , wani irin kyau kika yi kamar yanzu aka saukar dake daga sama "dan Allah malam dakata ya isa ban son magana da salo karka bari na sauke haushina gabad'aya akanka"

"wa ni ?
"Gaskiya ba'a yi haka ba ranki shi dade shiga mota muje , kyau kam kin yi sosai kuma dole a aya ba , tayi masa banza gabad'aya babu wacce ta kalla har aunty jiddah , ta samu guri ta zauna a baya saboda aslamiyya ta kame a gaban motar,tun da ta kame a gidan baya babu wanda tace wa qala
har suka iso gidan baba sarki hira ake amman ban daita sam bata saka musu baki ba illa wayarta data ciro ta shiga danne danne duk yadda ammar yayi ƙoƙarin janta da hira taki yarda ta saka baki ..

Suna shiga gidan baba sarki ,gidan ya hautsine da hayaniya da ihun aunty sakina da yaran gidan ,tazo da gudu tamkar wata yarinya ta rungume aunty jiddah ajikinta tana murna ganinta ,cike da farinciki ta janyo hannu aunty jiddah "muje daga ciki ,a babban parlour'n hajiya kulu suka zauna gaba-daya su .

Ummita kuwa tunda ta gaishe da mutane gidan tayiwa kanta mazauni a kujera mai zaman mutun ɗaya ta cigaba da game a cikin wayarta , bata sake kallon inda suke ba haka suma babu wacce ta saurareta murnar ganin juna kawai suke , cikin minti goma aunty sakina ta cika musu gabansu da ruwan sha da drinks har ma da smallchop's "kai yau ina da manya baki tun jiya na kasa samu isasshen bacci saboda zuwanku me zaku ci a dafa muku ?
Aunty jiddah tayi murmushi tace "kai daga zuwanmu sai dai zuwa anjima dan gaskiya yanzu a koshe muke ko ta fadi tana kallon sauran yan'uwanta duk suka daga kai alamun eh " hira suka shiga yi kowa na fadar albarkacin bakinsa amman banda ummita da ko ruwa bata sha ba, sai dai duk abinda suke faɗa yana shiga kunnenta can aunty sakina tace "wai ummita me kike yi a waya ne sama da awa biyu baki ce komai ba baki sha komai ba ,ga duk yan'uwanki na walwala ban da ke ?

aslamiyya tayi tsigil tana yatsina fuska tace"wai nan fushi take damu tun jiya taki yiwa kowa magana "
"akan wani dalili kenan ?
"Oho mata mu dai zamu yiwa mutun magana tun da mun san illar yin gaba a ddini , kuma mun san illar kasani ka take sani " aslamiyya meye haka idan zakiyi magana kiyi sak akan abinda akayi tambaya akai ba wai ki dinga fadar abinda bai dace ba ?
"Ce miki akayi tana gaba daku ko me ?
inji cewar meenal.

"Sai an faɗa mana, halinta ne bamu sani ba ko me ?
" ko me zatayi tayi ai bamu muka ce tayi rashin kunya har a samu damar jibgi banza aslamiyya ta K'arasa maganar tana kwashewa da dariya, sauran ma duk suka dara har ammar , "Inna jiya fa har da guzirin dorina mai baki shida Allah ya taimaketa ya rayhan da ya Abdurrahaman suka shiga tsakani da Allah kaɗai tasan irin dukan da zata sha inji cewar Ammar , sakina tace " waye ya jibgeta saboda Allah ?
"Wa kika sani daya wuce ya Ma'aruf shi tayi rashin kunya kinsan shi babu hakuri .....
Nan kuma hirarsu ta dawo kan Ma'aruf
Ummita tayi shiru taki cewa komai sai dai idanunta sun kad'a sunyi jazir ,ta lumshe fararen idanunta tana cizan lip's dinta na kasa a hankali.. ..

"Aunty sakina ta sake cewa " ummita kice wani abu ,akan Ma'aruf mana kinsan fa ni ina son ayi yar gida ne , "kin manta ne aunty sakina ni ba hanyarmu daya dashi ba ,da
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On WANNAN CE QADDARARMU
avatar
amina-4

11 months ago

Reply

Interesting novel

avatar
amina-4

11 months ago

Reply

Interesting novel

Please Login or Register in order to submit comment