Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

daga officer din ba sai waigawa sukayi basu ganshi ba, suka fito suna murmushi kai tsaye inda yayi parking din motarsa suka nufa ya bude mata gidan gaba ta shiga ta zauna idanunta na kallonsa ya rufe ya zagayo ya bude mazaunin direba ya shiga ya tada motar sai gida a parloun kasa suka iske mama da hajiya umma suna ganin shigowarsu suka zuba musu ido suna kallonsu "sannuku da gida mah'ruf ya faɗa yana ƙoƙarin zaunar da ummita akan kujera mai zaman mutun uku ya kwantar daita "sannuku da zuwa ya mai jiki me likita yace yana damunta ?cike da murna da farinciki ya isa gaban mama ya zube yana faricikin ya daga hannun mama sama "kiyiwa godiya mamana Allah ya sake amsa rokonmu sai dai fatan Allah ya bar mana wannan babyn muga fitowarsa duniya "kana nufin wani ciki ga ummita mama da Hajiya umma suka hada baki gurin fadar haka ?
Ya gyada musu kai cike da zumudin yace "wallahi ya maida idanunshi ya zubawa ummita cike da qauna fariciki ya cika zuciyar ummita ganin yadda mah'ruf yake ta murna da rawar kai Hajiya umma ta maida hankalinta garesa ta galla masa harara "ta mike dan taga alamun idan tacigaba da zama rashin kunya zai yi a gabansu kafin kace me yan'uwa sun cika dakin duk a dalilin taya juna murna washegari da gudu menal tashigo tana ihu da murna ta rungume ummita tana kissing dinta wannan ihun murna da menal tayi ya gigita hajiya Inna dake bayi tana bayan gida ta soma ƙoƙarin mikewa tana mita "wannan wani irin maseefa ne za'a cikawa mutane gida da ihu ,mayar da gida kamar gidan cinima tana gama mikewa ta manta babu kafa ,take kafarta ta lankwashe a sakamakon jijiyar bayan kafarta data rike sai dif kake ji a kasan tayis ta fadi kan dayar kafar take ta zube kasa warwas haɗe da kifawa tana kiran sunan Allah da sunan ya'yanta , bayan kusan minti talatin tana kwance tana nishi ta kasa motsawa cikin haka Allah ya jeho aunty da shigowarta kenan har zata fara shiga part din mama ta fasa "Assalamu alaikum Hajiya inna ?
Shiru ta sake kiranta tana duduba daki tana mamakin inda take bayan tasan bata da lafiya sai can taji nishinta tana kiran sunanta da dasashiyar muryarta da sauri ta karasa ta bude kofa "subuhanallahi ta faɗa jikinta na rawa ta karasa shiga ta durkusa a gabanta, tana yi mata sannu sannan ta taimaka ta fito daita ta kwantar daita akan gado "garin yaya hajiya inna har kafar ta soma kunburi wa ya barki ke kadai a bayi ? "wallahi saudat ce wai ihu naji ya cika gidan shine garin na fito na manta bani da kafa wannan sabon iftilain ya saukar min tayi maganar da kyar tana matso hawaye daga idanunta take tausayinta ya kama aunty ta ciro wayarta ta Kira y'an'uwanta kafin kace bangaren ya cika makil da yaya da jikoki ban da ummita kowa sai sannu yake mata injiniya ya rufe saudat da fada "ka barta na dai san da mairo ce bazata tafi ta barni ba ...

*******
Cikin kwanakin ba karamin tattali mah'ruf kewa ummita ba
Bayan sati biyu babu abinda ke damun ummita sai rashin karfin jiki da kuma amai da take yawon yi wanda likita yace sai cikin yayi kwari zata daina sannan ya kafa doka banda aikin wahala , gabadaya mahruf ya tare a gindin ummita ,dan kusan rabin kayansa ya dawo dasu gida, jifa jifa yake zuwa gidansa "kwance suke cikin bargo suna manne da juna ummita ta shige jikinsa sosai tana shafa qirjinsa tana zuba masa shagwa'ba "ina sonka mah'shub bana son abinda zai nisanta da kai, idan ka rabu dani mutuwa zanyi ,dan bazan iya jurar zama a duniya ba, toshe mata baki da nashi yana shafa dukiyar fulaninta sai daya tsotsi bakinta son ranshi sannan ya zare yana tsura mata ido "nima haka nake ji ,ki daina kawowa zuciyarki zamu rabu da juna , ba rabuwa ba ko nisa bazan iya yi dake ba muna tare muddin rai kallonshi take bata ko kifta ido tana sakar masa murmushi wani irin kissing dinta ya soma yi yana sake rungumeta ajikinshi a hankali ta kai bakinsa cikin kunneshi "bacci mah'shub "tun yanzu ?
Ta lumshe masa ido "gaskiya ban yarda da wayon ba ina bukatar ganin babyna ya fito da kuzari ya kare maganar yana aikata mata da zafafan wasanni masu rikitarwa kissing din dukiyar fulaninta ya shiga yi take yanayinta ya sauya taji gabad'aya babu abinda take buƙata sai shi a hankali ya sake dulmiyar dasu cikin duniyar ma'aurata awa daya awa biyu yana kan abu daya tun tana cijewa da dauriya har ta fashe masa da kuka ganin halin da take ciki yasa ya saurara mata ba dan ya gaji ba d'aukarta yayi ya shiga bayi daita sukayi wankan tsarki tare, ya sake daukota suka fito ya sanya mata kaya ya kwantar daita yana massaging din jikinta ahankali bacci ya dauketa.

washegari ta dade tana bacci kafin ta tashi , mamaki ganinta ita kadai tayi bata san sanda mah'ruf ya fice ba saukowa tayi daga gadon ta nufi bayi ta watsa ruwa tana saka da shafa mai ,menal ta shigo bakinta ɗauke da sallama "ledar hannunta ta kalla "yaruwa me kika kawo min cikin dariya tace "kunjita kamar wani abun arziki take ci idan an kawo, ummita ta kwashe da dariya "ina kika baro min yarona ?
"Yana gurin mama a bangaren hajiya inna muka haɗu yaruwa wannan tsohuwar fa jiki yaki Kinga yadda kafafunta suka dawo har gani bata yi sosai idanuta sun kumbura da kyar take gane mutane ni dai nace haki ne yake bin hajiya Inna , ummita ta sauke ajiyar zuciya "ai duk wanda ya shuka irin abinda hajiya inna tayi bazai gushe batare daya girbe abinda ya shuka ba ,"gaskiya kullum ina mamakin yadda mama ta tsaya tsayin daka gurin kula daita wallahi da nice ko kallon inda take bazan yi ba "wannan shine nawa tunanin amman zuciyarmu ba daya ba ita mama daban take ,kinsan Allah tunda tayi faduwar nan ko hanyar part dinta ban bi ba bare mu hada ido har nayi mata sannu wannan matar idan na tuna abinda ta min ina jin kamar na kasheta dan dai kawai ba'a rama sharri da sharri ne amman duk da haka mummunar addu'a zan cigaba da yi mata har zuwa sanda zata gangara ..
Ranar da cikin ummita ya cika wata cif ranar ta soma nakuda tun tana yi ita kadai har ta faɗa wa mah'ruf suka nufi asibiti suna zuwa nakuda ta kama zanga zanga cikin kankanin lokaci ta haifi kyawawar babynta mai kama da mahaifinta sak likitoci suka gyara suka canza mata daki, idanunta ta lumshe lokacin da suka sauka akan babynta dake kwance a gefenta tana tsotsan hannu kafin kace asibiti ya cika da yan'uwa da abokan arziki murna gurin mah'ruf kamar an haifa masa duniya tunda akayi haihuwar yake makale da baby da uwar baby abun nasu gwanin ban sha'awa suna gudanar da soyayya ya dubeta yace ",nayi miki wayo dayawa babyn nan gabad'aya dani take kama mutum ya kwantar da baby ya dawo gurinta ya daura kanshi a kafad'ar yana manna mata kiss ta waigo ta kalleshi a dan firgice ta kalleshi ta kawar da fuska "karka sake kissing dina Kar aunty ta shigo ta ɗauka biyemaka nake bama haka doctor yace sai nayi wata wata uku wani abu bai shiga tsakaninmu ba saboda mahaifata nada saurin daukar ciki ka matsa ko na maka ihu "bisimilla gwada mu gani "ni dai kayi hakuri ka koma can wayar hannunsa ce ta shiga ring jafar ne dan haka ya daga "ganin nan zuwa ya kashe ba ya kalleta yana jan yatsun hannunta "ki shirya nan da wani shekarar ma zaki sake wani haihuwa sai kin dawo min da twins dina ta shagwa'be masa fuska "ba dai wani shekarar ba ya fita yana mata dariya ..

Washegari dakin ya cike yake da yan'uwa duk wanda ya daura ido kan babu baya son d'aukewa
, ta kalli menal da aunty ta yatsinsa "babyn nan fa yunwa take ji tayi maganar kamar zatayi kuka,aunty tayi mata banza ta cigaba da hada kayan da'aka yi amfani dashi , ganin haka yasa ummita ta kalli aunty Aysha "gsky baby tana jin yunwa "to ki bata nono tasha mana tunda kinsan tana jin yunwa duk nan ƙoƙarin muke muga ruwan nonon yazo ," kawai ummita ta kama kuka " tun jiya bata ci komai ba sai ruwa " cikin haka mah'ruf ya shigo da sallama Assalamu alaikum maida idanunta kanshi "subuhanallahi ya furta yana ajiye kayan hannunsa ya karasowa inda take da sauri "me aka miki kike kuka haka ..? "yauwa baba tunda ka shigo ka taimakawa wannan sarkin shagwabar ka janyowa baby bakin nono a samu tasha tun jiya bataci komai ba aunty Aysha najin haka ta mike ta fita menal ma haka , daya bayan daya suka dinga fita daga dakin , ya zauna kusa da ummita yana shafa fuskarta "kamar ya aunty? "Kamar yadda ka saba ta bashi amsa, ya ɗan zaro ido yana kallon ummita yana girgiza "me ye kake wani kallona kamar yanzu zaka fara sha tayi maganar can kasan makoshi aunty ta ɗauki bakin fida ta karaso inda suke ta mika mata" ungo kisa a bakin nonon ki bata nono mugani ,take ta amsa tayi kamar yadda tace ya ɗan zungureta "duk kin rude akan baby , wasa wasa ma mantawa dani zaki yi akan baby nan, yayi mgn murnushi na bayyana akan fuskarsa aunty ta fita daga dakin tana kiransa ya mike ya fita ya sameta "idan fa ruwan nono bai zo ba dole zaka zuko a samu kan ya fito tana gama fadar haka ta wuce ta barshi ya koma dakin yana shiga yaga ummita tayi kicin kicin da fuska tana kallon bakin nonon da kan fida har lokacin ruwa yaki zuwa ya zauna kusa daita bai ce komai ba ya kai hannunsa ya cire kan fida ya daura bakinsa cikin second biyu sai ga bakin nono ya fito ta dai ji zafi sosai " ta shiga bawa baby nono yana zaune yana Kallonta ta kalleshi yayi mata kyau sosai cikin shigar kananan kaya washegari aka sallamesu daga asibiti bayan dawo gida muhd Sa'id ya kawo matarsa tayi Barka ,ranar suna baby taci maryam sunan mama ummita taji dadi sosai da yarinya taci sunan mahaifiyarta take suka rada mata khairat an yi taron suna lafiya kowa yaci ya koshi a haka rayuwa tacigaba da tafiya yarinya tayi wayo sosai watan hudu ta soma rarafe nan take mah'ruf yace da alamun mamana fa tana son Kani ko kanwa koma kanne ummita ta hararesa "karka yiwa yarinya sha tun kafin takarasa ya rufe mata baki da nashi alokacin da menal ta sake samun wani ciki ..

******

Bayan wata bakwai

Rayuwa tayi suhaima zafi babu isashen lafiya ga mahaifiyarsu itama an sake yanke gwiwar kafarta , duk abinda ta mallaka sai data siyar hatta kayan d'akinta  , alhaji Umar kuwa duk  yasan zai nemi hajiya rahma yayi daga karshe suhaima ta faɗa masa gaskiya ai kuwa tun daga ranar bai sake zuwan ba ya dauko matarsa daga efe ya dawo daita gidansa cikin yayansa suka ci-gaba da rayuwa, wata rana suhaima ta shirya tazo gidan neman taimakonsa ,nan idanunta suka gane mata Fatima da ritsetsen ciki ,babban dan hajiya rahma bilal ta tambaya "wacece wannan yace "matar abbanmu ce tayi wata irin mutuwar tsaye "kana hauka ne ko ka fara shaye shaye  yaushe yayi aure ?"lafiyata lau matarsa ce wallahi ni ba wannan ne damuwata ba ya za'a yi mami ta dawo me yasa mami ta biyewa son zuciyarta ? me ta nema ta rasa data zabi wannan rayuwar ya karasa maganar yana kuka,yayinda suhaima ta dinga zage zage , tana cikin yi Alhaji Umar ya fito ya bada umarni a fitar daita daga gidan sannan kar sake barin ta shigo gidan ,da kuka ta bar unguwar tun daga gra har markaz tazo da kafa a jigace tashigo gidan , rashin abinci yasa suhaima ta mokade ta rame idan baka mata kyakkyawan sani ba bazaka geneta ba  cikin haka sai ga baki ta zo wai mahaifinsu yaci bashi 20  million tayi kuka tayi hauka Amman haka ta hakura tunda ga sheida haka tana ji tana gani aka saida gida 200k suka hau suka mika mata ta kama daki a kasan gwagulori  sauran canji suke cin abinci kafin wani lokaci kudi ya kare  ta nemowa mahaifiyarta sanda ta jata suka nufi oshodi bara  ko sunje bawani abun kirki suke  samowa ba saboda warin da kafar keyi duk inda sukayi korarau akeyi wasu subadu wasu su hanasu ..........

Khairat na da shekara daya menal ta haihu ta kara wayo tana yawonta koina ga surutu sai kace menal bayan wata tara ummita ta haifo d'anta namiji shima kyakkyawan ranar suna taci sunan shuaib bisa umarnin abba dan shi mah'ruf sunan abba yaso sakawa zaman lafiya da kwanciyar hankali ne ke wanzuwa a tsakanin mah'ruf da ummita
Kwance suke cikin bargo makale da juna kamar zasuyiwa juna numfashi ya gyara suman gashinta dake son rufe mata ido qauna muryarsa a sanyaye ya kai bakinsa kunneta "qauna wai ya labarin ciwon zuciya ne da alamun soyayyar mah'ruf ce ta haddasata kou tayi murmushi tana kusa fuskarta a qirjinsa "tunda dana mallaki mah'shub matsayin miji na nema na rasa yayi min maganin ciwon zuciya suka sake makalewa juna suna kallon kwayar idanunsu ", Allah sarki rayhan dina Allah ya jikansa "amern kiyi kokari ki kawo rayhan "wallahi ko yanzu a shirye nake muddin sunansa zaka sa Hajiya inna fa ta bude baki zata yi magana ya haɗe bakinsu guri daya ..

Allah yasa mu dace Allah yafe mana kurakuranmu Allah yasa muyi amfani da darasin dake ciki Aysha bagudo takuce Ina alfahari daku masoya ...

Alhamdullahi

TWO FRIENDS BSBS


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya

Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,

Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490

A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,

Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu

Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC

Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services

Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us

Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it

Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT

This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels

DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On WANNAN CE QADDARARMU
avatar
amina-4

11 months ago

Reply

Interesting novel

avatar
amina-4

11 months ago

Reply

Interesting novel

Please Login or Register in order to submit comment