Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

,kallon kallon suka shiga yiwa juna kafin daga baya yace  "daman inna  ce bata da  gaskiya shine da cin zali ka mari yar mutane ?
Mah'ruf ya sunkuyar da kanshi yana tsosa keyarsa alamun jin kunya   "oya shige  muje har part dinsu  ka bata hakuri, babu musu yayi hanyar part  dinsu ummita  suna shiga mama na saukowa , tana ganinsu ta saki fuskarta duk da ranta a matukar 'bace yake  "yau injiniya ne da kanshi ?
"Dole ki gani  ,ga wanda na taso gaba   nan  ya bada hakuri "hakuri kuma me ya faru ?
Injiniya ya nuna ummita dake sheshekar kuka  da yatsansa "murmushi mama tayi "kai injiniya dan yayi mata hukunci bisa ga laifinta shine har da wani ban hakuri ai ni bai kyauta min ba  mari uku  ya kamata yayi mata ba daya ba  ..
take  mah'ruf ya sake yin kasa da kanshi yana mai tsanani  jin kunyar mama "ka k'arasa gurinta  mana ka bata hakuri ka wani tsaya kana kallona  ko  sai kaima na  gaugaura maka marin  kaji yadda taji  ,injiniya yayi maganar a fusace. Mah'ruf yasan  halin injiniya zai iya  aikatawa  ya maresa agaban ummita  dan shi babu ruwansa da wani  girman mutun matsawar kayi laifi zai hukuntaka bisa abinda ka aikata ,jikinsa a sanyaye  ya soma d'aga kafafunsa  meenal  na ganin haka tayi saurin mikewa ya zauna a mazauninta data tashi  muryarsa can kasa tamkar mai koyon magana yace "kiyi ......
Sai kuma yayi shiru ya kasa karasawa baya jin zai iya bata hakuri  , injiniya yayo  kansa a fusace  zai d'aukeshi da wasu mahaukanta maruka mama tayi saurin  shiga tsakani "kayiwa  darajar Manzon Allah kada kayi haka  ,wallahi idan ka mari yarona    bazan
yafe maka ba   sauke   hannunshi yayi yana dubansa  Sannan ya juya yana huci kamar zaki "ke kuma maza ki tashi ki bar nan mara kunya kawai  ummita ta mike simi simi tayi sama,
sai dai bataji dadin abinda mama tayi ba   taso injiniya ya  rama  mata marin da yayi mata, Allah ya isa kuwa tayi masa yafi cikin kwando

Mah'ruf ya riko hannun mama cikin nashi a daidai lokacin data juya zata shiga kitchen "kiyi hakuri  mamana   ki yafe min nasan ban...
"Karka damu babu komai har ga Allah ban ji komai ba da kai da ummita ya'yana ne dan  ina jinka  kamar nice na kawoka duniya , ya saki wani bayyanane ajiyar zuciya  ta koma  ta zauna kusa dashi "mah'ruf kayi hakuri  da halin ummita dan Allah ka cigaba da kular min daita duk runtsi duk wuya kada ka dubi idanuna ka hukuntata daidai da laifinta kai din tamkar uba ne a gareta kasancewarka babban yaya  , ina alfahari da kai kanshi a sunkuye akasa yace  "na gode mama duk duniya babu mama kamarki ina sonki mamana "nima haka mah'ruf  ban haɗaka da komai ba ni dai  ka rike min ummita amana ko ina raye ko bayan bana nan  ka zame mata bango  majinginta, ka kular min da lamarinta na baka amanar rayuwarta...
  "inshallahu mama Allah yaja da nisan kwana "ameen Mah'ruf Allah yayiwa rayuwarku albarka ya nuna min ranar aurenka ....
nan suka shiga wata hirar mama kenan mamar da samun irinta sai an sha wuya ..... Allah ya bamu irinta mama
Ummita kuwa tun daga ranar take jin haushin mah'ruf  a  zuciyarta   daga karshe ma tattara ta bar gidan zuwa gidan aunty Aysha  dan idan ta cigaba da zama zasu koma gidan jiya   ....
Kusan kwana biyu bai sanyata acikin kwayar  idanunshi ,duk ya damu amman ya kasa tambayar yaji  inda taje mama na hankalce dashi amman tayi masa shiru ,shi kuwa rayhan tuni yasan inda take dan haka kullun yana can suna shan hirarsu kwasam ma'hruf yaje gidan idanunshi ya gane masa ita suna sallama da rayhan   "good bye ya rayhan, yayi murmushi yana ƙoƙarin riko hannunta  "bakiji daidai ba yarinya  anjima zan dawo wani guri zani yanzu   ..
A hankali ya dauke idanunshi akansu ya sanya kai ciki yana jin faduwar gaba ,ta gabanshi tazo ta wuce tana rausaya  ko kallonsa batayi ba dan har lokacin tana tattare da jin haushinsa shiru yayi yana satar kallonta daga karshe yaja tsaki

*****
Ranar  wata  alhamis  mah'ruf   ya   dawo   daga aiki ,  sai mama   take faɗa masa ranar  asabar  zasu je kwatono  saka ranar  auren Usman    ,take  ma'hruf  yace shima  zashi dan  yana   son   yaje   gurin Usman  bayan kwana biyu ummita ta  dawo  gida  ta  samu labarin  zuwa  kwatono    ,take  tace itama zata , mama  tace "a'a ban  shirya tafiyar  dake  ba , dan haka bazani dake   ba da baba babba zamu kiyi hakuri idan zan sake zuwa sai muje tare ,ta fadi haka ne    saboda   tasan  muddin mah'ruf yaji daita za'a zai ce ya fasa zuwa  , ita kuwa daya fasa gara  ita tayi  zamanta ,ummta ta 'bata rai  zuciyarta na faɗa  mata kila  saboda Mah'ruf ne  yasa mama bazata  daita  ba , tama san  shine  ya zigata kartaje daita ,  ana cikin maganar  mah'ruf  din ya shigo  yana jin abinda suke tautaunawa, kai tsaye  yace  ya  fasa zuwa  aje  daita kawai shi  yaje  wani  lokaci ,itama tace ta fasa zuwa su tafi kawai  sukayi  dragging da mama datafi bukatar tafiya da mah'ruf akan ummita  ,  take  aunty  aysha  matar  yayan Mah'ruf  kuma diyar aunty salma  tace "me zai hana  mama  mutafi gabadaya     ...
Shiru  mah'ruf  yayi  bai sake cewa  komai ba saboda  mama  ,dan ya lura bata ji dadi da yace ya  fasa zuwa ba  ..
Suna  barin parlour'n ya dawo  kusa da mama ya zauna yana kiran sunanta  ta amsa masa a ciki batare  da ta kalli inda yake ba "fushi kikayi dani  mama?
"dole baba babba ,dole nayi fushi na rasa meke damun kai da ummita duk duniya nafi sonku da kowa, baka ji   yadda nake jin zuciyata ba a duk sanda naga  kuna sa'insa da junanku   ..
"To  kiyi  hakuri  mun daina  zani kinji mamana ,ta sake  yi  masa  banza  "dan Allah mama  Karki  yi fushi dani "naji  ai  dan kasan bana iya fushi da kai ne yasa   "to  kiyi hakuri  na daina yayi  maganar yana langwa'bar  mata da kai kamar wani  ƙaramin yaro , tayi  murmushi "kai ko Allah sai nayi fama gurin  bawa matarka hakuri  "hakurin me kuma  ?
"Hakuri da halin miskilancinka idan  aka kawota gidanka  musamman  zan ce akawo  min ita  na zaunar daita "nayita bata hakuri  nace  kiyi hakuri suhaima ! kiyi hakuri suhaima !! nasan bazata fahimci  irin hakurin ba, amman daga baya zata fahimta  ,yayi murmushin gefen  baki  tare da mikewa  akan doguwar kujera ya kwanta yana lumshe sexy eye's dinsa , "babu  wani  hakuri  da zaki  bata  ai ita taji ta gani  ta nace  "kai baba babba  bana sharri ka  dai nacewa yarinyar mutane   inji cewar aunty  Aysha data dawo parlour'n bayan ta gama yiwa ummita faɗa a d'aki .

ranar  juma'a  suka  shirya tun da asubar fari   suka d'auki hanyar kwatono   , suna cikin tafiya costom  din farko suka  taresu  sukace  mama  ba yar kasa Nigeria  bace ina zata?
Tace aure  zasu nan zango  basu yarda ba ,  da kyar dai aka samu aka shawo  kansu suka barsu suka  wuce  ,kafin su kawo  costom na biyar dake  tsaye  tsayen yayi yawa  sai mama tace "kai  nifa na gaji da wannan tsayuwar  da costom suke mana ,zaku ga  yadda zan  shigar daku kasata lafiya babu costom  din daya isa ya  tuhumeku har mu  shige,   amman  kalli yadda na kasarku suke  min  ,tayi maganar  kamar  zatayi kuka , ni dai yanzu abinda  za'a yi kawai ke ummita  koma  kusa da mah'ruf  ki  zauna daman ita  mama tana gaba kusa  da direba mah'ruf da  ummita  suna  sit  din baya  shi  yana gefe ummita  na gefe  matar yaya  a tsakiyarsu ,  mama tace " matar yaya ta  koma  d'ayan   gefe ummita ta dawo kusa da ma'hruf ta  zauna duk costom din  daya sake taremu   kuce amarya da ango ne  ku ,an d'auro muku aure  za'a kai ku   nan zango  idan suka ce  ina a zango " kuce   zango gidan ashiru .
take  ummita  ta bata rai  tana yatsina fuska da  zunzuburo  baki  ,mama tace "ke zanci ubanki wallahi  maza ki  matsa  kusa dashi   nace  ,shima ma'hruf ranshi  bai  so haka ba  amman babu  yadda zai yi da  mama  ,gashi  ya matso  yaga sun  isa  ,  dan hk ya kawar da kai , suna  cikin  magana direba  yana  tuki  maganar  mama na bashi  dariya ,matar yaya kuwa har da rike ciki saboda dariyar mama, cikin haka   sai  costom suka  ƙara  tsaida motarsu, yace "ku kuma fa daga ina ?
"ina zaku  haka ? Ke kamar  ma  ba yar kasar Nigeria ba suka tambayi mama" ina zaku take mama tace waɗan mata da miji ne jiya aka d'aura musu aure ko ba matarka bace mama ta juyo  tana  kallon ma'hruf zuciyarsa na  dokawa da matsanancin karfi  yace "ma..matatace  "to  ka nuna musu  mana cewar matarka ce  nan zango zamu  "ke ummita ba zaki  nuna musu mijinki bane    kike  kallon mutane  tare da haɗa mata  da  zagi  ,tana cika tana  batsewa  ta  kwanto  saman  qirjinsa shima ya kai hannunsa gadon   bayanta  yana shafa kanta zuwa bayanta tare da rufe mata fuska da qirjinshi  yana kirkiro  murmushin dole "aunty Aysha tace "kasan mu a gurinmu ba'a ganin fuskar amarya tayi maganar tana zolayar mah'ruf  ..
  take  dariya  ta subucewa costom sai da yayi  mai isarshi  sannan  ya basu hannu  suka wuce a haka har suka isa kasar  kwatono tana  manne a qirjinshi gabad'aya sun manta da sun gama wuce costom da imgration  sun mannewa juna suna shaƙar numfashin juna da kamshin turaren juna .
Mota na tsayawa a harabar gidan su mama, suka fita ya kai hannunsa ya shafa gefen  fuskarta yana magana kasa wanda ita kadai taji abinda yace     da  sauri  ta tashi  a gigice  ta fito da sauri daga motar tana hada hanya sai dai tana jin gangar jikinta ce ta fito, ta bar zuciyarta a cikin motar , tayi kokarin  sanyawa  jikinta natsuwa kafin ta isa inda aunty Aysha ke tsaye  tana jiran karasowarta  ..
Gidan ne ya hargitse da hayaniyar yan sannu da zuwa , Kai tsaye Usman ya zo ya dauki mahruf zuwa gidan mahaifinsa  , ranar  da suka sauka a ranar su mama suka tafi kai kayan saka ranar auren Usman   ..

TWO FRIENDS (BSBS)


💗💗💗💗💗💗
WANNAN CE
QADDARARMU
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

https://youtu.be/-Xy64PJiHiQ
domin sauraron abinda muka daura a YouTube danna blue rubutun dake sama. 👆🏻


~TRUE LIFE STORY~

FREE NOVEL


AL'QALUMAN



*AYSHA A BAGUDO*
*FAIZA HAMMADU*

~DEDICATED TO~
*MAMAN AYMAN*


WATTPAD @HAUESH

bismillahirrahmanirrahim


PAGE 28

.... Daren ranar kasa bacci ummita tayi sai faman juyi take akan makeken gadon kakarta , gabadaya ta rasa abinda ke damun zuciyarta gashi dai bacci take ji kamar tayi hauka amman da zarar ta runtse idanunta sai kwakwalwarta ta shiga harhaɗo mata hoton mah'ruf da yanayin character's d'insa, jin kanshi , yanayin miskilincisa , tausayinsa akan mutane , hakurinsa da rashin ɗaukar raini , rashin jin tsoro akan komai ,wayewa ta kowani bangare uwa uba kyau da kamewa tare da nagartaccen ilimin addinin dana boko .
wani irin yaji idanunta ke mata da zugi yayinda zuciyarta ke tsalle akanshi duk tunaninsa sai qirjinta ya buga ,
A hankali ta zuro kafafunta kasa ta sanya silifas ta sauko ta shiga zagaye d'akin , kafin ta soma zance zuci " ya mah'ruf ........
ta kira sunanshi a fili qirjinta na tsananta bugawa da matsanancin karfi " dan girman Allah ka bar zuciyata ta huta haka ,ka daina zuwa kana damun tunanina , me ma yasa kake yawon zuwa cikin tunanina ba kai yakamata na dinga tunawa ba adaidai wannan lokacin ya rayhan yafi cancanci da haka,to me yasa sai kai ne zaka zo kayi kanekane a ruhina ?
" dan Allah ka fita rayuwata ta k'arasa maganar tana sauke
naunayen ajiyar zuciya tare da yin shiru ta koma ta kwanta akan katifa tana juyi .

numfashi ta dinga saukewa a hankali kamar wacce tayi gudu ceton rai ,hannu ta kai cikin suman kanta ta dinga yamutsawa kafin daga bisani ta dinga sakin murmushin da ita kadai ta bawar kanta sanin ma'anarsa, lokaci ɗaya kuma ta sake sauke ajiyar tana cikin tunaninsa bacci barawo ya d'auketa .

bangaren mah'ruf shima raba dare yayi zaune yana tunaninta abinda yafi tsana kenan ya zauna yana tunaninta a karon banza alhalin yasan hakan bai da faida agurinsa , ganin tunanin banza da iska ya saka shi a tsakiya yana kawowa zuciyarsa farmaki ya janyo system dinsa ya shiga aiki kafin daga baya bacci ya fara fixgarshi ya janyo bargo ya lullu'be jikinsa yana fidda numfashi mai gyaraye da jin dumin jikinta a nashi ,yana son sanin abinda yasa yake yawon tunaninta , amman zai bari har sanda zasu koma nigeria ya tambayi jafar amininsa dan sosai yake son sani dalili wannan banzan tunanin , daren rana haka ya kwana yana tunaninta da bukatar son Jin dumin jikinta a nashi ..

Tun bayan da suka sauka a kasar cotonou bata sake saka mah'ruf a cikin kwayar idanunta ba , tun tana basarwa har ta tsinci kanta cikin tsananin damuwa dashi tana son tambayar auty Aysha ammn jin kai da miskilanci ya hanata ...
a hankali ta lumshe fararen idanunta sakamakon tuno abinda ya faru a tsakaninsu a sanda zasu zo , babu abinda yasa zuciyarta sake makance akan tunaninsa bai wuce yadda ya dinga cusa fuskarta a tsakankanin fad'ad'd'en kirjinshi daya waddatu da sihirtaccen kamshi turarensa mai tsuma zuciya .
sosai zuciyata ta tsinci kanta da jin matsanancin kewarsa , ta dinga jin zuciyarta na harbawa akanshi tana bukatar d'aura kwayar idanunta akanshi wanda ta rasa dalilin faruwar haka "bai dace ki dinga tunaninsa ba ummita zuciyarta ta fahimtar daita haka "i really has to do that meye ciki dan nayi tunaninsa a matsayinsa na d'an'uwana ?
kuma ya damu da lamarina dana mahaifiyata kyakkyawar zuciyarta ta faɗa mata haka ,yayin da wani bangaren na zuciyarta tace "ya dai kamata ki daina zurfafa tunaninsa haka idan ma yin tunani ya zame miki dole to kiyi tunanin mijin da zaki aura ba wannan mugun ba ...

abinda bata sani ba zuwan ma'hruf biyu gidan ita din ce baya bukatar gani saboda ganinta na haifar masa da kasala da jin sanyi a sansar jikinsa ,
haka zuciyarta ta dinga tunaninsa duk hirar da Badar cousin dinta ke mata baya shiga kunnuwanta saboda hankalinta yana wani bagire , ganin tunaninsa yaki barin zuciyarta da gangar jikinta yasa ta yunkura a hankali ta mike sanye da doguwar rigar abaya baka wanda akayiwa adon orenge stone tun daga samansa har kasa ta d'auki mayafin abayar ta rufe kanta dashi wanda ya fidda shape din fuskarta da sirrin kyawunta tare da zurawa kafafunta bakin silipas na roba a wannan zuwan da sukayi ne kakarta ta bata , ta soma ƙoƙarin bin kofar baya wacce zata sadata da harabar gidan ..
badar ta kalleta tana nazarinta "ina kuma zaki ko kina bukatar wani abu ne ?
A hankali ta girgiza mata kai "na gaji da wayon kwanciyar nan ne zan dan fita harabar gidan nan da lambu na sha iska "to ko bakin ruwa za'a rakaki ?
"No kinsa bana son kallon ruwa bari dai na tsaya iya nan din tayi maganar tana sanya kai, Badar ta biyo bayanta suna tafiya tana yi mata hira har suka wuce kofa biyu ta bangaren kakarta inda suka iske yan aiki kusan guda goma kowa na aikin dake gabansa .
"Ummita tunda kika zo nake especting naji kince wani abu akaina amman naji kinyi min shiru alhalin duk wanda ya gani tsawon wata biyar zuwa yanzu zai fahimci na canza sosai .
ummita ta juyo a hankali ta tsaya a gabanta tana kare mata kallo da nazarinta domin son gano abinda take son ta tofa albarkacin bakinta akai
, jiki a sanyaye ummita ta dafa kafad'arta haɗe da kiran sunanta "badar .....
Badar ta tsura mata ido tana sauraronta "a gaskiya banga abinda kike son nayi magana akai ba, gaki nan kin kara kyau kinyi fresh .
"baki dai kalleni da kyau ba amman babu wanda zai ganin da ba zai fahimci yadda na dawo ba "to ke meke damunki gara kawai ki faɗa min dan ban fahimci komai ba ?
Badar ta sauke naunayen ajiyar zuciya "wallahi asiri , anata min asiri ta nan data nan bakiga yadda duk na lalace ba na rame, baki ga idanuna duk sun kunbura ba ..?
Ummita tayi saurin dafe goshinta "kai badar me yasa maganarki kullum bata wuce wannan dan girman Allah ki daina ire iren wadan nan magangun bashi da amfani wallahi babu abinda wani ya isa yayiwa bawa sai abinda Allah ya kaddarowa bawansa tana gama fadan haka tayi gaba bunta.
da sauri Badar ta biyo bayanta
bai fi taku biyu su k'arasa lambun gidan ba ummita ta tsaya cak sakamakon kamshin turaren mah'ruf data soma jiyowa , a hankali qirjinta ya shiga luguden bugu , ta cigaba da tafiya qirjinta na dokawa da sauri badar na biye daita a baya tana cigaba da magana akan abu ɗaya da Ummita ta kasa fahimta .
a tsakiyar lambun suka iskeshi zaune shi kaɗai akan daya daga cikin fararen kujerun dake ajiye agurin domin shakatawa hannunsa rike da waya sanye cikin kananan kaya farar riga da blue jean gabansa farin table ne dake dauke da ruwa da lemu da snaks naunayen ajiyar zuciya ta sauke tana jin wani irin yanayi mai wuyar misaltuwa a jikinta , yayinda kyakkyawan murmushi ya bayyana akan fuskan badar gabadaya ta maida hankalinta akan mah'ruf cikin rawar jiki badar ta dafa kafadun Ummita da karfi "Ummita wannan yayan naki ya haɗu matuka kalleshi saboda Allah ina son yanayin kamewarsa , bana son nayi aure a wata kasa amman da yayan nan naki zai soni ya aureta wallahi da babu abinda zai hana na aureshi , amman wannan asirce asirce da ake bina dashi bazai bari wani namiji yaga haskena bare har yace yana sona ....
a matukar fusace ummita ta zabga mata ƙatuwar harara kana tace "wai ke wake miki asiri da kika damu mutane da asiri ake miki "wallahi zuwa nake ana duba min .
"amman dai kinyi hasara rayuwa wallahi kina ta zuwa gurin malamai da bokaye suna amshe miki kudi suna faɗa miki karya kou ?
"to wallahi ana min asiri gashi an hanani cigaba ba'a son cigabana ,abarni jiya iyau a shekaruna ya kamata ace ina da aure har da yara biyu shekarata ashirin fa yanzu amman kalli yadda aka barni duk na susuce na lalace "kinga malama ni dai gaskiya kin dameni gaskiya da maganar asiri asiri nan ni dai babu ruwana idan ma ana miki can ki karata ,ni dai karki kara min maganar asiri "
",okay dan na faɗa miki matsalata shine zaki dinga min haka ba laifinki bane ni da tattaro nazo gidan saboda ke ,bazan ƙara zuwa ba har kubar kasar nan ,"dan girman Allah karki ƙara zuwa "ai daman bazan ƙara zuwa ba.
"oya kama gabanki tun yanzu "bazan wuce ba sai lokacin dana ga dama tafiya zan tafi tunda gidan ba naki ba hasalima nafiki karfi da gidan "koma dai menene ni dai karki kara min maganar asiri ko yaushe ko yaushe
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On WANNAN CE QADDARARMU
avatar
amina-4

11 months ago

Reply

Interesting novel

avatar
amina-4

11 months ago

Reply

Interesting novel

Please Login or Register in order to submit comment