Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

tana zaune gaban mirrow tana gyara gashin kanta dan ta samu damar yin bacci mai dadi  ta cikin madubi ta hangoshi  ya  rungume hannuwansa duka a qirji yana kallonta, shiru ne ya ratsa dakin kafin daga baya ya soma takowa gareta ya tsaya abayanta ya sauke hannunta dake ƙoƙarin hada gashin,ya  cusa hannunsa cikin gashin  gabadaya ya tattara gashin , saukar hannunsa cikin gashin kanta  yasa  take taji yanayinta ya sauya tsikar jikinta suka dinga mimmikewa ta lumshe idanunta, bai yi mata magana ba haka itama bata ce masa komai ba har sanda ya haɗe su waje ɗaya tana tunani yadda zata kasance a daren yau din nan har ga Allah bata marmarin ya sake kusantarta yanzu, tana tsananin jin tsoro wannan abar tasa, a she rashin kibarshi ba komai bane kibar na gurin jijiyarsa , idan kaga jijiyarsa sam bazakace a jikinsa take ba saboda rashin kibarsa Allah yayi masa baiwa iri iri.

bata an kara ba taji ya dauketa  ya kwantar akan katifa tare da cire rigarsa ya yi mata runfa da fad'ad'd'en qirjinshi "a faɗa min tunanin me ake haka ?
Ta lumshe idanunta ta bude tare da tsurawa qirjinsa ido gashin gurin sai sheki yake da ɗaukar hankali bata san sanda ta  kai hannu ta soma shafawa tana lumshe ido , bakinsa ya sauka akan bakinta   wanda   hakan  yasa  ya  birkice mata    gabadaya tsoronta ya bayyana a sansar jikinta yana jin yadda  zuciyarta ke  dokawa    .

  murmushi yayi dan yasan abinda ya maidaita haka "I need you  qauna do you also need me ya faɗa cikin killer voice dinsa tuni jikin ummita ya mutu ya sake shigewa jikinta da mata riko mai karfi ,take ta sakar masa jiki ganin ya samu abinda yake so ya gyara mata kwanciya yana rabata da yar rigar baccin jikinta yayi filinging daita nan ya fara aikata mata da  sakoninnsa tuni ummita ta manta wani zafi data kwana sha jiya ta rungume mijinta, sun kusan awa uku  cikin duniyar ma'aurata kafin daga baya  ya dawo haiyacinsa , taji zafi sai dai ba kamar jiya ba  ,wani sanyayyen dadi ne ya lullu'be zuciyar mah'ruf  lalla'bata kawai yake yana manneta da qirjinsa yana sauke ajiyar zuciya  ya jima yana tunanin rayuwarsu ta da ,da rayuwar da suke a yanzu ya tsura mata ido yaga  tana lumlumshe idanun alamun jin bacci "karfa kiyi bacci dan ko kinyi bacci zan tasheki  tayi saurin bude idanunta a cikin nashi " anya kuwa zata cigaba da biye masa yazo yayi mata mugun sabo shi gashi ba tabbas garesa ba tamkar hawainiya yake , canzawarsa  bata da wahala ?

Batayi magana ba kawai ta soma k'ok'arin juya masa baya yayi saurin juyo daita "abinda nafi tsana kenan arayuwata a juya min baya bare kina matsayin matata karki sake ya matso daita yana shafa sansar jikinta babu yadda ta iya dashi haka ta hakura suka sake lulawa gajimare ..

********
Bayan kwana biyu aunty ta tattara ta koma gidanta dan  mah'ruf babu sauki baya kunyarta duk inda ummita tayi yana like daita ,bangaren
Suhaima    gabadaya a cikin kwanaki hakuri kawai take da mah'ruf shima ɗan tasan halinsa ne tana magana zai taso mata  , tana zaune duk abun duniya ya dameta yadda mah'ruf yake  shigowa  ya fita magana ɗaya biyu ne kawai ke  shiga tsakaninsu , gabadaya  yana nuna mata iyakarta akan ummita kiri kiri yake nuna mata yafi son ummita dan ko ranar girkinta haka zai ta rawar jiki yayinda ranar girkinta zai zauna cikin kunci da bacin rai daga karshe dai sai ya dangana da dakin ummita zai samu walwala gashi  yanayinsa sun nuna yana  zaune lafiya da ummita kuma yana  samun biyan bukatarsa enough agurinsa  tunda ko ta kawo masa uzurinta baya wani damuwa ko kiransa tayi baya ɗauka akan lokaci haka baya reply text message dinta  ta kasa hakuri ta kira hajiya rahma ta saka mata kuka "kina da matsala wallahi suhaima biyayyar karyar  nan dai zaki cigaba da yi ,kafin muga yanayin aikin zulaiha dan da alamun akwai nasara dan baki ga yadda bashir yake zariya ba duk ya haukace.

"yanzu yayyarmu  a saki ukun zata koma a ganina ta samu ta auri wani mai karamin karfi ko three days ne ya sakota sai ta koma ",ke rufe mana baki  yanzu mata nawa suke kome da saki goma ma ba uku ba wadan nan kanuna yan iskan basa sakin mutun idan mutun yayi kuskuren aurensu kawai dai ayi sha'ani "shike nan zan jira ranar lahadi zanzo na duba jikin hajiya zamu haɗu "Allah ya kai mu sukayi sallama ....

Ummita na zaune  a parloun'nta na sama taji sallamar meenal  da gudunta ta  kwaso ta soma  sauko biyu biyu suka rungume juna "wayyo matar yayana wannan kyau haka  suka zube kan kujera "kinsa Allah tun jiya dana tambaya my d ya barni na kasa bacci kirki sai naga garin ma ya dade bai waye ba ,suka sake rungume juna "nayi kewarki yar'uwa "nima  ya labari kwana dayawa fatan yayana ya sake bamu sabon baby dan wannan fresh din akwai ayar tambaya ?

"Kai menal ke fa  naga aure ma wani sabon lasisin iskanci ya baki ,"wallahi haka my d ya faɗa   saboda abubuwan da nake masa ke mazan sai da iskanci ake gane kansu fatan dai Kema baki tsaya tsanya wacan tsohuwar guzumar ta sha gabanki agurin yaya ba  ?

Ummita ta sauke numfashi tana riko hannun menal "kinsa   Allah idan kika ga  yadda yayanki yake ji dani sai kin sha mamaki ke a halin yanzu ko mutuwa nace yayi zai yi "ke kiyayye kanki karki kashewa mama d'a ,dan sai tayi gunduwa gunduwa da namanki , dariya suka kwashe dashi "to ai shine yace zai iya mutuwa akaina "ke mu ajiya wannan maganar ya labari muna zuba ido fa munji shiru amman duk wanda ya kyalleki yasan da magana wannan yayan nawa yayi durin madarar soya beans.

"Allah ya shiryeki menal  Wai yaushe kika dawo haka ne ?
"Aure ne ya canzani  Kema zaki canza ne idan wannan mijin naki mai ra'ayin rikau ya canzaki  , kinsa ko last week mun haɗu dashi a gida ina gaishe shi yana min d'acin rai  wallahi kiyi masa magana tunda dai muma ana morar jikinmu  "kai menal baki da mutunci wallahi ,can tayi  kasa  da muryarta"ke nifa ciki ne dani na wata uku  yanzu haka daga asibiti muke na saka masa kuka sai ya kawoni na ganki ?"Allah yar'uwa ummita ta rungumeta ajikinta tana murna "shine dan wulakaci kika wani kwaso da gudu haka kina son wahalar mana da baby  ,to  allah ya raba lafiya Allah ya nuna mana wannan rana ,sun kulle kansu suna hira tare suka shiga kitchen suka girka abincin rana  ..

wuni  zur menal tayi mata tace bari na tashi na wuce kafin wannan mijin naki ya dawo ya ishi mutune da miskilanci da d'acin  rai "ke wallahi ba haka yake ba yana da saukin kai fa sai dai idan ranshi a bace yake "lallai jijiya dadi kece yau kike wani tare masa, ko ki yarda ko karki yarda halinsa na nan har yanzu baki kai shi sammajannati ba bare ya canza wallahi bari na gudu kar yazo ya koreni "Allah ki kiyayi zagar min miji a gabana ta faɗa tana hararta dariya menal tayi har da rike ciki .

"yau dai da nima bani da aure da nasha bakinciki  lokacin da zata wuce ne ta shiga ta leka aunty jidda,  babu  yadda ummita batayi daita ta shiga su gaisa da suhaima   tace bazata shiga ba "ke rabani da wannan matar mai shegen iyayin tsiya da mugun hali  "wallahi yayanki bazai ji dadi ba "kar Allah yasa yaji wallahi idan kina damuna akanta zan daina zuwa "yi hakuri yar'uwa ni bana zuwa ke bakya zuwa ai abu ya lalace  ki saki  ranki dan Allah nice fa ta hannun damarki "naji sai munyi waya sukayi sallama cike da kewar juna ..

*******

Bayan wata daya

Kwance take ajikinsa bayan ya  matsa mata  sunyi sex , suna  gamawa ta kwasa  aguje  tayi hanyar  bayi ta  sugunna  ta shiga  kyaleya amai  ya biyota aguje  ya dafata "am sorry qauna  yana  daya sanin  takurata da yayi, dan tunda ya shigo yaga alamun kamar bata jin dadi ,yana tsaye ta gama kyalaya amanta  .
ya wanke mata baki suka fito  ya canza mata kaya "bari na wanke jikinta muje asibiti cikin sauri ya shiga ya wanke jikinsa ya fito ya zira jallabiya ya zira mata hijabinta ya ɗauketa cak bai direta akoina ba sai acikin mota ya kwantar mata da  kujera "sorry qauna har suka isa asibiti sannu yake jero mata suna isa ya fito da sauri ya sake d'aukarta wannan karon rungumeta yayi sosai ajikinsa  yana lalla'bata  Tamkar ya wata baby hatta numfashi yana jin da yana da hali da yayi mata dan karta wahala .

batare da bata lokaci ba likita ya soma dubata sai dai  gwajin farko Dr husain ya fahimci shigar ciki gareta   ya d'ago yana duban mah'ruf  tare da mika masa hannun "congratulations  madam fa ciki ne daita "ciki doctor ?
"Ka daina mamaki da ikon Allah Allah yasa wannan karo  ma mu samu twints."ammen doctor amman naji dadin wannan magana , magungana doctor ya rubuta masa ya mika masa, farincikinsa ya kasa boyuwa ya riko hannunwata " Allah ka gama min komai a rayuwata you give me  everything  ka bani   abubuwa masu mahimmanci arayuwata "alhamdullahi Allah ka inganta min wannan baby "qauna kinga ikon Allah ko ashe da wuri haka zamu sake samun wani baby ta rungumeshi ajikinta "am so happy  ya mah'ruf shima rungumeta yayi sosai tun acikin mota ya kira suhaima ya  sheida mata sannan ya kira gida ya faɗa musu .

Kai  tsaye  gidan mama suka wuto  basu sameta  a parloun'n kasa ba suka zarce d'akinta tana ganinsu ta saki murmushi "kai baba sai dai abarka to meye abun tasota gaba kuzo ,? "mama wannan abun fariciki  ai dole muzo ki sanyawa shaleleki  albarka, mama tayi murmushi "Allah kyauta duk  ka canza wallahi kamar ba kai ba, aranshi yace bazaki gane ba mama wannan yartaki  ta wuce yadda kike tunani suna tare da mama har kusan shadaya  sannan suka dawo gida ..
*****
wannan samun cikin  da ummita  tayi ya  balain d'agawa suhaima hankali dan haka ta dinga shirya yadda zata zubar dashi tun bai je ko'ina ba nan suka bazama gurin   bokan da yayiwa zulaihat  shima ya tabbatar  musu asiri bazai   tasiri ajikin mahru da ummita ba  saboda ana tsaye da addu'a a  akan mah'ruf da ummita " amman  karku  damu  zan  kokarta  ,  zamuyi aiki ajikinki   kije ki  nemi wani namijin daban  byn mijinki   kuyi auratayya dashi  idan kun gama  ki  kawo mana  spam dinku dashi zamu hada aikin , ya mika mata  wani farin kyale, idan kuma hakan bata samu ba ki  kawo mana  kayan  jikinsa wanda   kukayi auratayya dashi a lokacin  ko  da kuwa boxcer dinsa   ne muddin kika  kawo magana ta kare zamu  kona abu ya zama gari zamu hada miki garin hoda dashi  da man shafawarki duk sanda tayi ciki zaki gani koda kuwa na kwana ɗaya ne matukar kin haɗu daita ,sannan  zan baki aseje ki ciki  wanda zaki dinga zuwa mata cikin  baccinta yanzu dai  kije ki nemo   wanda zakuyi autarraya dashi kafin na faɗa miki shatadin aikin .

nan suka baro gurin boka hankalinta a tashe  tana tunani" ina zata samu wanda zasuyi sex dashi  gashi duk  ta sallami samarinta a tun farkon haduwarta da mah'ruf  ?
"Ya naga duk kin damu kanki inji cewar hajiya rahma ?"dole  na damu  yayarmu wa zan samu da zai kusanceni  " dan wannan zaki damu ai bai kamata ki  damu kina dani ba   akwai yaron     da zan nemo miki mai suna  *mus'ab*  kanin hajiya adama kawata ne ance min ya kware a harkan bin matan aure ,musamman ma suke nemansa ya biya musu bukata su kuma su biyashi    sai na  haɗaki dashi  "*mus'ab* suhaima ta furta sunan a kasan ranta ..

TWO FRIENDS BSBS

💗💗💗💗💗💗
     WANNAN CE
   QADDARARMU
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

~TRUE LIFE STORY~

FREE NOVEL
            
      
AL'QALUMA

*AYSHA  A BAGUDO*           
*FAIZA  HAMMADU*

SUBSCRIBE TO MY YOUTUBE CHANNEL *HAUSA BAKWAI*

~DEDICATED TO~
*MOMY ASMA'U MADUGU (MRS LAWAN ATNAL)*

WATTPAD @HAUESH

bismillahirrahmanirrahim

PAGE 61

Shiru  tayi    ta kasa furta komai  har sanda  hajiya  rahma  ta  k'araso  bakin  tafkeken  get din gidan      ta  sauketa  taja  motarta  ,gabanta  na wani irin  dokawa   ta soma  buga karamin   get  ,mai gadi  dake zaune ya  mike ya buɗe mata,  tana shigowa  haraban gidan idanunta suka  sauka akan mah'ruf  dake   tsaye  cikin kayan  shan  iska wando da  riga farare sol  , ya zuba hannunsa  ɗaya  cikin aljihun wandonsa  yayinda  d'ayan   hannunsa ke fuskarshi  yana  shafawa zuwa   ha'barsa   tare da tsurawa  get din  ido, yana  son  sanin  lokacin da  zata shiga  gidan dan  tun  karfe biyu  ya dawo gidan  bai isketa ba, shi daya bata awa uku kacal ......

gabanta  yayi mummunar  fad'uwa  a dalilin   idanunsa  dake yawo a sansar jikinta  ,ya dade  yana  kallonta ,sai daya  gama  hukuntata da sexy eye's d'insa sannan ya furzar da iska mai zafi ya ɗauke kanshi yayi kamar bai ganta ba ya  soma  tafiya a hankali  zuwa runfar shakawarsa  ya ja  kujera ya zauna  ya da'ura kafarsa daya a kan daya ..

Cike da matsanamcin tashin hankali  ta shiga    tunani abinda zata kare kanta a gurinsa  bata san sanda  mah'ruf ya bar gurin ba , a hankali ta sauke  naunauyen ajiyar  zuciya  hantar cikinta na  kad'awa , ta  waigo gefen hannunta na  dama  nan ta hangosa zaune rike da waya  yana daddawa , ta  karaso gabansa ta durkusa har kasa ta buɗe bakinta  cike da sanyi jiki ta soma magana  "habibi dan girman Allah kayi hakuri  nasan na wuce kaidar  lokacin daka  bani wallahi na tsa.....

Yayi saurin d'aga mata hannu " ban son jin  long talk  "karfe nawa yanzu ?
"after  4  ta bashi amsa gabanta na fad'uwa , "karfe nawa nace ki dawa gida  ?"Karfe biyu  "shine kika dawo yanzu saboda baki ɗauki  dokata  da daraja ba   ..?

Bakinta na rawa tace  "ba haka  bane habibi  hajiya ce "shiiiiiiiiiii yayi saurin katseta ta hanyar daga mata yatsansa daya  ,take   tayi shiru tana  sauke naunayen ajiyar zuciya a bayyane "  abinda nake so dake  karki  ƙara tambayata  zuwa gidanku  , duk mai son ganinki yazo nan ya sameki   tunda abun naki ya zama iskanci da rainin hankali ,  duba daraja mahaifiya ba zai sa nayi sakaci da aurena ba  at lest Ina  iyakacin bakin kokarina akanki   tunda bakya  gani shikenan ,daga yau  na kashe zuwa ko'ina tun da   ya fara magana bai d'ago  ya kyalleta ba har sanda ya dasa aya kusan minti goma tana durkushe  gabansa  tana  bashi hakuri  yayi mata banza saboda ranshi yayi  bala'in ɓaci  ,tun 7 na safe  ya sauketa a gidansu shine sai yanzu take dawo masa gida tana kallonsa  ya manna waya a kunensa  "idan kin gama ki fito ina jiranki  abinda ya faɗa kenan ya katse kiran yana cizan lip's d'insa na kasa .

ganin yadda yayi  banza daita yasa  ta mike jiki babu kwari  ta nufi bangarenta  ta tsaya gurin window parlounta ta ciro wayarta ta kira hajiya rahma kira ɗaya ta ɗauka"ya akay suhaima ?"ina  one  chance yayarmu  mah'ruf fa yayi Cancer din fitata ko'ina wai duk mai son ganina yazo to yanzu damuwata  yadda abun nan zai kasance.

"wannan miji naki akwai dan durin uwa,  dan iska mai taurin kai da bakar zuciyar wahala   ,bancin ma kin nacewa aurensa   da kin  rabu dashi  mu huta da jaraba ,mutun ba'a karuwa dashi ga shegen miskilanci da iko  dukkaninsu suka yi shiru na second biyu sannan hajiya rahma tace "  babu komai  bar dan iska a gidan nashi za'a yi komai  ki kwantar da hankalinki da zarar ya fita gobe zanzo da mus'ab kuyi abinda zaku yi  "okay yayyarmu  na gode Allah dai ya bar mana ke "ameen ta fadi  tana ƙoƙarin kashe wayar a daidai lokacin da ta hango  fitowar  ummita  sanye cikin hijab brown  har kasa  .

Mah'ruf dake zaune yana ganinta  ya tsura mata ido yana kallonta har ta kusan  yin  tuntube ya zabura da sauri ya nufeta  tun bata  kai  kasa ba, ya  tarota jikinsa  haɗe da furta   "oh my Goodness  qauna ki dinga bi a hankali plz kinsa fa bake kad'ai bace  ,  ta shagwa'be masa fuska "ai wadan idanun naka ne ,idan kana kallon mutun dole jikinsa ya kama  rawa  "to ai ke dince duk kingama da zuciyar maza , ba kiji abinda mama ta faɗa ba wai    na  canza,  bata san ke kika  canzani da salonki  ba.

  gaba-daya ta kasa  motsi  dan maganganunsa kunya suke  bata fuskanta ya d'ago ya sanya kwayar idanunshi cikin nata   "kema kinsan  kin canza mahruf , shi ne dai ya kasa canzaki , ta kawar da fuskarta  tana murmushi dan tasan halinsa ba ƙaramin aikinsa bane  ya kai bakinsa cikin nata ,"muje lokaci na tafiya dan kaci   minti ashirin daga  cikin  lokacinka da ka bani , ka duba lokaci karfe   nawa yanzu ?

Yayi   murmushin gefe baki  "kinsa Allah idan kika yi wasa za'a  fasa zuwa, cikin shagwa'ba tace  "kai ma kuwa  yau da ka kwana a  d'akinka kai kadai  ya zaro ido  "what ? ta lumshe masa narkakkun idanunta ,
"ai daman abinda kike so kenan matsoraciya kawai ,ban ta'ba ganin matar dake  jin  tsoron mijinta     irinki  ba, ya k'araso ya buɗe mata gaban mota ta shiga ta zauna,  shima ya zagaya ya shiga ya zauna yayi wa motar key suka bar gidan.

sai daya hau titi sosai sannan ya cigaba da magana  "wai me yasa kike jin tsorona? muryarta a sanyaye kamar wacce aka wa dole   "bafa haka bane kawai dai ni dai ina jin... tayi shiru ta kasa karasa mgnr, ya lulu'bo  tafin hannunta cikin nashi  yana murzawa a hankali  "gaskiya ban yarda ba a  fada min  dalili    ? tayi masa shiru  tana murmushi shima dole yayi shiru har suka kai  gidan   menal  dake  ore meji    ya tsaya a daidai bakin get din gida"sauka naje na dawo minti talatin na baki . "Kai bazaka shiga ba  ?"Uhmmmmm ya faɗa yana  tsare  gida  "why tayi masa tambayar kamar zatayi kuka "me zan shiga nayi a gidan sister dina ?

"wannan ai lalura ce dan Allah ka d'aure  mu shiga tare  "ba fa zan shi ...tayi saurin  katse shi ta hanyar haɗe bakinsu guri  ya tsurawa kwayar  idanunta nashi idon ,a hankali ya kai hannunsa gefen fuskarta ya shafa  yana ƙoƙarin cafko laulausan  harshenta tayi saurin zare  bakinta da sauri  dan muddin yayi nasarar cafko harshenta   anan zasu saura suna abu daya "am sorry muje ko  ,guri ya samu gaba kadan da gidan yayi parking  ya fito ya rike  tafin hannunta suka  shiga ...

a haraban gidan  suka  haɗu  da    abdulshakur ya k'araso gurinsu yana
murmushi ya mikawa mah'ruf hannu suka gaisa   "sannuku da zuwa  "yauwa ya mai jiki ? "Alhamdullahi taji sauki auntymu sai yau kika zo gsky munyi fushi kullun sai baby ta min complain ?

Mahruf  ya tabe baki "wai baby kamar wani shasha , ummita tace "wayyo mijin  yar'uwa wallahi ba laifina bane , mah'ruf ya watsa  mata  wani   kallo  mai haɗe da harara dole tayi shiru ,abdulshakur yayi gaba suka biyo  shi a baya a babban parloun'nsa yayi musu masauki sannan ya fita .

ummita ta kwanto  jikinsa "me kuma nayi kake   hararata ? "a yaushe kenan ? ya karasa  maganar ya furzar da iska "Ai daman nasan waskewa zakayi "  tunda   kin san waskewa zanyi  kema  sai ki waske  ya k'arasa maganar tare da kai wa bakinta  ligth kiss   .

ummita  tayi saurin gyarawa daga kwanciyar da tayi ajikinsa   saboda jin  motsin bud'e kofa  abdulshakur da menal  ne suka shigo , ya taimaka mata ta  zauna shima ya zauna kusa daita "yaya ina yini?Ya gida ya aiki ?"lafiya ya jikinki  yace a takaice ta amsa tana  kallon ummita  tana harararta "Am sorry  yar'uwa  ya jiki ?"bazan amsa ba ,ai  da kin bari kin zo zaman makoki , ummita tayi murmushi "Allah ba zai sa ba , wallahi ba  laifina bane Kema kinsani   ki fahimceni dan Allah  .

abdulshakur ne ya tashi ya kawo musu  abun sha sannan suka cigaba hira ,yayinda lokaci zuwa lokaci mah'ruf ke duba agogonsa a karo na karshe yaga  minti tallatin tayi  ya mike tsaye  tare da sanya hannunsa cikin aljihun ya ciro 20k ya  ajiye mata akan center table  ,   itama  ummita ta mike  "to yar'uwa sai wani lokaci Allah ya raba lafiya "ameen har dake  ummita tayi murmushi suka musu sallama  suna juna  murmushi, har haraban gidan menal da Abdulshakur suka rakasu sai da suka ga  wucersu sannan suka koma ciki  .

Kai tsaye   hanyar  family house d'insu taga sun dauka take murna ya rufe ummita ta kasa boye murnarta ,ya waigo ya kalleta  bata san sanda ta had'eye farincikinta ba dan tasan zai iya fasa zuwa,  dariya ta bashi amman ya waske ,bangaren hajiya inna suka fara bakinsu dauke da sallama, suka shiga parlou'n ta a lokacin da take ƙoƙarin zama da kyar  tana rike kafarta ɗaya data rike mata , ganin mah'ruf yasa  ta fadada fuskarta da murmushi "babana kai ne da yamman nan ? 

Murmushi yayi "ai  har nayi fushi nace  kusan sati ina fama da ciwon kafa amman  ko sakon gaisuwa  ?bai kai ga amsawa ba ta ga ummita na kokarin shigowa ta yatsina fuska tana mamula baki,guri ya samu  kusa daita ya zauna yana gaisheta ta amsa tana dubansa ,"ya karfin jikin inna wallahi jiya malik yake faɗa min  bakiji dadi ba ? "Uhmmmmmmm kafafuwana ne wallahi  yanzu ma haka lalle nake son d'aurawa  " maganin meye shi ? "Maganin ciwon kafa "Allah yayi afuwa yasa zakkan jiki ne "ameen ya Allah ya aikin naka da suhaima itama kwana biyu ta ɗauke kafa ?" Alhamdullahi komai lafiya "

ummita ta karaso tana dari dari tana jin tsoron karta koreta, ta  zauna nesa da mah'ruf  tana gaisheta  "hajiya inna ina yini ya karfin jiki ? Shiru tayi taki amsawa gabad'aya jikin ummita yayi sanyi ta kasa motsi mah'ruf ne yace " Hajiya ana gaisheki fa    " ammmmm lafiya ta faɗa atakaice tana dauko wani hira ,shi kuwa zuba mata ido kawai yayi yana jin zallar bacin rai dan ba haka takewa suhaima idan sun zo daita ba , basu dade ba saboda matsuwar daya lura ummita tayi  da shi kanshi ,itama 20k ya ajiye  mata tare da sallama jiki a sanyaye ummita ta fito daga dakin inna sai lokacin natsuwarta ta dawo jikinta haɗe da sauke naunayen ajiyar zuciya , suka shiga part din  mama da hajiya umma sannan    suka dauki hanyar dawowa gida akan hanyarsu yake kwantar mata da hankali da nuna mata komai yana da lokaci sannu komai zai wuce ,ta kamo hannunsa cikin nata tana murzawa cikin salon jan hankali "zan yi hakuri da komai akanka, ni dai tayi hakuri ta barni da kai dan ka rigada ka zama wani bangare na rayuwata bazan iya rayuwa babu kai ba ,ya harareta "kamar gaske tayi murmushi "Allah kuwa ta bashi amsa tana sake damke hannunsa ,  a haraban gidansu  sukayi branch  suka cigaba da maganar hajiya inna gefe guda kuma suna murza  soyayyarsu  ...

A karo na barkatai da suhaima  take  jan tsaki tare  da kara kai idanunta kansu  suna zaune   akan fararen kujeru da aka tanada domin shan iska ,sun bala'in tsurawa junansu ido  kusan minti goma  suna kallon juna daga karshe  ya ciro wayarsa ya matso kusa  daita kamar zai shige jikinta  ya  manna fuskarshi da nata ya d'aukesu  hoto  sai da yayi musu kusan guda biyar  sannan ya ajiye wayar akan table din dake gabansu  kuma duk akan  idanun suhaima abinda bai taɓa faruwa a tsakaninsu ba kenan rabon da suyi hoto tun na dinner din aurensu .

mah'ruf ya riko laulausan tafin hannunta cikin nashi yana kissing suhaima tayi saurin runtse idanunta zuciyarta na kuna da rad'ad'i mai tattare da bakinciki ,  tana binsu da wani irin kallon tsana  tana jin  kamar ta shiga kitchen ta dauko  tafasheshn ruwan zafi ta kwara wa ummita  ajiki , a hankali ta fito daga part dinta idanunta na kansu sai data k'araso daf dasu  sannan ta tsaya tana sauke numfashi da kyar qirjinta na dokawa da karfi kamar wacce ake bugawa guduma  a daidai lokacin da mah'ruf ya bude  bakinsa ya cigaba da  magana "qauna .........

Ya
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On WANNAN CE QADDARARMU
avatar
amina-4

11 months ago

Reply

Interesting novel

avatar
amina-4

11 months ago

Reply

Interesting novel

Please Login or Register in order to submit comment