Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

inna kaina zai cire yayi maganar yana dafa goshinsa dan yasan idan ba haka yayi ba bazata barshi ya huta da surutunta ba ..."
"tam ai shikenan nayi shiru , ku kuma kun wani zaunewa mutane kun tsaremu da idanuwa , barin ma wancan jairar mai idanu kamar na agolar nufawa, naso ya waske min ke da mari na huce takaicin abinda kika yiwa Ammar"

"ai sai kisa yanzu a waskeni da mari tunda jakarki ce ni daga wasa shima me yasa ya jera mana kwanuka ?
Jin abinda ya fito a bakin ummita yasa cikin rawar jiki meenal ta yunkura ta dafa kafad'ar aslamiyya muryata can kasa kamar zata yi kuka "aslamiyya bani da sauran gurin zama anan ,zan gudu wallahi idan kun tashi ku biyo ni tayi hanyar fita , ɗaya bayan ɗaya suka dinga tsilalewa suna barin d'akin kar zunubin ummita ya shafe su .
"shikenan Allah ya baki Sa'a ki cigaba ba dai takamarki maida wa mutane magana ba ?
"idan shi bai nada miki na jaki ba , zan biya sadam yayi miki dan banza dukan da zaki kasa tashi , kai kuma bari na kawo maka magani ka sha kaji babana, bana son wannan ciwon kan naka na gado ,ni bama ciwon kai ba a rayuwata bana son naji baka da lafiya ,da kayi ciwo gara ace nice bani da Lafiya .......
ummita ta kalleta a sukwane tana ta'be baki, "aikin banza idan kin isa ki cire masa ciwon ma gaba-daya tayi maganar a cikin ranta yayinda a fili taja tsaki tana motsi da bakinta yana jinta ya share dan yau baya jin kulata .

"Amar miko min mayafina dan Allah gashi can a bayanka " "Ammar na shirin mika mata , inna ta kwalla masa kira"ammar "na'am inna gani nan zuwa ya mike da sauri ya nufi uwar d'akan inna "kai wannan jara da yawa take , ina ma Allah zai kashe min ke na huta da jarabarki dan kinji zan moresa shine na kiransa Allah dai yasa nima ba gurguwa bace da kafafuna .. ..
Wani irin fad'uwar gaba ma'aruf yaji from know where ,amman still bai d'ago idanunshi ba, har sanda ta raɓa ta gefenshi zata ɗauki mayafin on-expecting taji anyi sama daita .....sai gashi
ta dawo kasa dummmmmmm kamar buhu ta baje a kasa tayi zaman 'yan bori a gabansa , gaba-daya gigicewa tayi tashiga wiki wiki da idanu , batasan ya aka yi hakan ta faru daita ba, sai dai ganinta tayi a saman kafafunsa bakinta ya bugu da kasa taji wani irin azaɓaɓɓen ciwo ya ratsa bakinta ,a hankali ta kai hannuta daidai bakinta zaro idanuwa tayi a matukar firgice tana kallonsa jini ta gani ......
shi kuwa tamkar ba shine mutumin da yayi kwallo daita ba, idanunshi na runtse tamkar mai yin bacci, ba shiri jikinta na rawa ta juya tana kallon uwar d'akar inna , tare da addu'ar Allah yasa inna da amar basu ga abinda ya faru ba , bare suyi mata dariya ,kuma tasan dole sai sun sanarwa kowa kodan ayi mata dariya . ...
" cikin wani yanayin na nuna ko in kula da jan aji tare da tsantsar miskilanci ya soma buɗe idanunshi a hankali , aiko yana gama budewa idanunshi suka sauka a kanta durkushe tana kallonsa wani irin zirrrrrrrr ... taji a gaba-daya illahirin jikinta har cikin tsakiyar kanta tamkar an jona mata wutar lantarki , zuciyar bala'i take son masa amman ta kasa bude bakinta ,a halin da take ciki ma koma tace zata yi magana bakinta bazai iya furta komai ba
daskarewa tayi agurin haɗe da zuba masa fararen idanu tana cigaba kallonsa kafin daga bisani ta samu kanta da d'aukewar numfashi ..
tunda take bata taɓa tsintar kanta cikin wannan yanayin mai wuyar misaltuwa ba da kasa aikata komai garesa ba , haka nan yau ta ke jin ta kasa ɗauke idanunta akanshi sannan ta kasa furta komai garesa ....
shi kanshi tsura mata idanunshi yayi masu matukar kyau da tsoratarwa yana kallon lumsamsun idanunta masu matukar haske da mamakin rashin ɗaukar mataki akan abinda yayi mata kusan minti biyu suna kallon juna kafin daga baya "ya watsa mata harara "
Take tsoron yanayin yadda yake kallonta ya mamaye zuciyarta da gangar jikinta wanda tasan wannan kallon da yake mata na gargadi ...
Amman tayi tamkar bata san abinda hakan yake nufi ba ,ganin taki mikewa bisa kafafunsa tana kallonsa cike da tsoro yasa muryarsa a kausashe yace " uwar me kike jira ,common get up from my .....
ai tun kafin ya K'arasa tayi zumbur ta mike jikinta na rawa ...amman hakan bai sa tsoronta ya fito fili ba dan tana isa daf da bakin kofar fita , ta tsaya tana watsa masa harara tare da cewa " aikin banza kawai idan mugunta abun yi ne mutun ya ci gaba, da sannu Allah zai yi mutun da kaidinshi ,
kuma ban yafe ba Allah yayi min bakar isar da bata da magani tana magana tana ƙoƙarin ficewa daga d'akin batayi taku ya kai biyu ba taji an fixgo hannuta ...
A tsorace ta saki wata razananniyar qara jikinta na ɗaukar rawa kamar mazari.....


Two friend's (bsbs)
💗💗💗💗💗💗
WANNAN CE
QADDARARMU
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

~TRUE LIFE STORY~

FREE NOVEL NOT FOR SELL


AL'QALUMAN



*AYSHA A BAGUDO*
*FAIZA HAMMADU*


~DEDICATED TO~
MAIMUNA MATAR ABDULLAHI

BEST FRIEND FOREVER AND EVER, AKWAI AMANA 'KAWARMU ALLAH YA BARMU TAREN TARE SON SO FI SABILILLAH 🥰🥰

WATTPAD HAUESH


PAGE 11


...... ..a tsawace ya buga mata wata razananniyar tsawar data firigita zuciyarta tayi saurin kamkame shi ajikinta batare da tasan tayi hakan ba..
" rungumeshi da tayi yasa ya dinga kallonta da bayyananne tsoro a kwance saman fuskarshi take ya had'iye wani emotion daya ziyarci zuciyarsa da gangar jikinsa , fuskarshi babu walwala ya sauke naunauyen ajiyar zuciya ,kusan minti biyar tana rungume ajikinsa ,ya waiga gefen hagu da damansa bai ga alamun kowa ba ,ya ja ɗan qaramin tsaki, bai so jikinsa ya haɗu da nata ba ,yanzu idan wani ya gansu haka yace me ?
Bai ma da tabbacin duk abinda zai faɗa a yarda dashi a wannan lokacin ,bari ya hanzarta tun kafin wani ya gansu ..



Muryarsa a tsarke yace "ke kina hauka ne da zaki haɗa jikinki da nawa ,har ma da wani lefe wa ?
Yayi maganar yana bambareta ajikinshi "kin wani manne ajikina mutane yar iska banza kawai jarababbiya .....
Ta buɗe baki da niyyar magana yayi saurin daga mata

"shiiiiiiiiiii tare damke tsintsiyar hannuta cikin nashi dan sai ya azabtar daita akan Allah ya isan da tayi masa , shiru tayi tare da lumshe fararen idanunta,"kin ma rainawa kanki hankali, me zaki ce da kika wani bude wannan rubabben bakin naki da duk doyi yake ?
"Wallahi naji kince tak nan sai kinga yadda zanyi da namanki "


ta sake buɗe idanunta tana kare masa kallon tsab taga yadda yanayinsa ya sake saiyawa fiyye da dazu ,hankalinta yayi mugun tashi da rawar jiki tace "to ..ka sakar min hannu na kama gabana .
"shi kuma Allah ya isan da kika min fa?
" kina nufi ya tafi a banza ne ?

Ta daure fuska sosai ta soma ƙoƙarin cire hannunsa dake rike da nata tare da neman hanyar guduwa " ka sakar min hannu dan Allah ,kana min shishigi fa , bana son abinda kake min ,bana son kana shiga lamarina"


"Ni ne ma nake miki shishigi ,nake shiga lamarinki ,sannan baki son abinda nake miki ?
ya faɗa yana d'age mata girasa ɗaya cike da jan aji "ai kafi dan dako sanin kana min shishigi ..
muryarsa cike da miskilanci yace "waɗan banzayen samarin naki ne 'yan dako , muje nayi miki hukuncin Allah ya isan da kika min sannan ki faɗa min irin shishigin da nake miki albashi daga yau sai na daina ,dan idan akwai abinda ke 'bata min rai kuma na tsana bai wuce mu'amula dake ba ko shiga lamarinki"

"Kasan Allah to wallahi bazan koma cikin wancan d'akin ba ,duk abinda za'a yi sai dai ayi anan amman bazan komai ba"

......
yayi murmushin gefen baki wanda da gani na takaici ne sannan yace "kinsa Allah sai kin koma da kakafunki kuma har da guzirin izaya" ......
ya K'arasa maganar yana tsura mata idanu yana karantar yanayinta wanda da kyar ta sake fuskantarahi tayi masa kallon second biyu tare da sauke ajiyar zuciya, da alamun tsoro a tattare da ita ,dan kallo ɗaya yayi mata yasan dauriya ce kawai tattare da ita amman zuciyarta cike take fal da matsanancin tsoronsa ...
Ya ji dadin sosai acikin ransa sannan ya cafki bayan wuyanta yayi cikin d'akin inna da ita , yana K'arasa shiga d'akin ya wurgata a tsakiyar parlour'n ta zabura ta mike tsaye tana haki , "oya start frog jump"

da sauri ta ware fararen idanunta duka akanshi tana kallonshi a tsorace tare da nuna kirjinta da ɗan yatsanta "ni din ce zanyi tsallen kwado ?"

"Kwarai kuwa yarinya yau tsallen kwado nake da bukatar ganin kin yi ,ta haka ne kawai zan iya bambamceki da kwado ko fat lion , kinga ma idan aka ci sa'a sai sunanki ya tashi daga fat lion zuwa frog" ......

Ta zumburo masa karamin bakinta yayinda muryarya cike da shagwa'ba tace "gaskiya ba zan iya ba ...
"Karki yi kiga yadda zanyi dake yanzu ,"wallahi bazan yi ba dan ban ma iya ba,kuma ban san yadda ake yi ba" ....


ya girgiza kai kawai yana cizan lip's d'insa na kasa " ammar ....ya kwalla masa kira ,ammar dake kwance a uwar d'akin inna ya fito da sauri "gani yaya "
"ka iya tsallen kwado ai ?
ammar ya girgiza masa kai alamun ya iya, "ok Koya wa wannan mai fuskar zakin "
"an gama yaya "

Ahankali amar ya fuskanci ummita dake tsaye tana cika tana batsewa ,ya kunshe dariya dake ƙoƙarin subuce masa saboda ganin yadda ta cika bammmmm tana jira a taɓa ta fashe da kuka .. "kinga ummita haka zakiyi ya sakala hannuwansa duka ta karkashin kafafunsa ya kamo kunneshi sannan ya soma tsallen kwado , yayi kamar sau uku yana zuwa yana dawo wa sannan ya tsaya yana dubanta "tou hajiya ummita haka zakiyi ...
"Gwada mugani ko zaki iya" "......

Muryarta na rawa tace " baza'a yi ba gara kawai a harbeni gabad'aya nasan ba'a kaunata a gidan nan da dai nayi wannan abun mai azabar tsiya , ni dama ba'a danginku na fito ba" ta K'arasa maganara hawaye na gangaro mata "amar yi tafiyarka ai ka gama mai wuyar idan ta isa kar tayi" ....ya fad'i haka ya koma ya zauna akan kujera ya daura ƙafarsa daya kan daya yana jijjigawa batare daya kalli inda take ba , Ummita ta kalleshi zuciyarta na wani irin tsalle tasan tunda ya dage sai tayi dole tayi dan tasan halinsa bashi da kyau a kowane fanni kuma baya ya fiya komai kankantar mutun idan yayi masa abu sai ya rama ko ya hukunta mutun da azaba mai rad'ad'i shiyasa gaba-daya tun tasowarsa ake jin tsoronsa ita kaɗai ce a duk cikin family dinsu take ramawa da rashin nuna jin tsoronsa ,sai duk wannan mugun halin nasa Allah yayi shi da nasibi da kwarjin jama'a duk inda ya shiga sai ya tara mutane ....

Ta sauke naunauyen ajiyar zuciya
a daidai lokacin da inna ke fitowa daga uwar d'akanta hannunta rike da magani da ruwa ta miko masa "ungo ka sha ,ka daina biyewa wannan yar banzar... hawan jini kawai zata daura maka kamar yadda ta daurawa uwarta, wannan ja'irar cutar ce ta kama ka bata da arasa dadi ma zata ji yar mai mugun halin tsiya ....
"Inna ki bar magani nan naji sauki , ni doguwar magana ce kawai ban so ...
Ta zauna kusa dashi tana ajiye cup din ruwa matsalata da kai kenan ba'a maka gwaninta babansa" tayi maganar tana sake maida hankalinta kan ummita,


"ke zaman me kike wa mutane ?" maza tashi ki bar min daki na sarara"

"Ga wanda ya tsaidani nan , kice ya sallameni na kama gabana dan ni ba iya abinda ya sani zanyi ba"

... " me zaki yi masa ?"



"Wai tsallen kwado zanyi..... gashi ni kuma tunda nake a rayuwata ban taba yi ba, sai dai naga ana yi ..
ta K'arasa maganar kamar tana matso hawaye "inna ta kwashe da dariya tana tafa hannu .

" kai babana kasan ta kan sharri , wallahi har ka wanke min zuciya , bari na kawo maka dorina mai baki shida , tana tsallen kwadon kana tsallawa ja'ira"
........
"kai inna saboda kin tsane ni Kou , shine zaki kawo masa dorina har mai baki shida kamar wata diyar cikinsa ko wata jaka , wai ma inna me na tsare muku ne a gidan ke da shi"

"Baki tsare min komai ba sannan baki min laifin komai ba , laifin ki daya ne da kika zo duniya ta tsatson mairo ...
"Yadda gaba-daya uwarki bata da muhalli a cikin zuciyata, haka ne yasa kema bana jinki a cikin raina ,sai dai kiyi hakuri bazan iya haɗa soyayyar jikokina da naki ba"


idanun ummita suka sake kadawa suka cicciko da ruwan hawaye ,tana janyo numfashi da kyar ta fesarwa tana sauke ajiyar zuciya har makoshinta na lotsawa tsabar bakinciki , ma'aruf yayi shiru bai san sanda ya juya ya kalli inda ummita take ba, ya tsura mata ido yana karantar yanayinta , da kyar ta sake d'agowa ta masa kallon minti biyu ta sake sauke ajiyar zuciya ........

ya ɗauke idanunshi akanta "kiyi abinda na sakaki ki kama gabanki dan ban son ganin wannan banzar fuskartaki"

"ke kuma inna ki daina abinda kike bai da kyau , wannan tamkar sabo ne , da Ummita da sauran jikikokin ai duk abu daya ne tunda ta rigada tazo ta tsatson d'anki "a'a ma'aruf da bambamci sosai ,idan kana min irin haka zamu samu matsala da kai "
"Mun dade ba'a samu matsala dake ba ....
"Kayi shiru kar wancan yar banza taji ta ɗauka ka damu daita ne barin taji zamuyi faɗa ai dadi zata ji ,kai dai kayi shiru kawai"

..."ni dai karki sake zagin mama anan gaskiya "kar muyi haka da kai Ma'aru sau tari sunan da take Kiransa dashi kenan "bari na shiga na dauko maka dorinan"
.....
da kyar ummita ta yunkura ta mike zuciyarta na dokawa kamar zata fasa kirjinta jikinta a matukar sanyaye ta kama kunnuwanta duka zata fara sai ga ya rayhan da ya Abdurrahaman sun shigo bakinsu ɗauke da sallama ,da idanu ya rayhan bi ummita dashi yana kallonta da tsantsar mamaki a saman fuskarshi da sauri ya k'araso gareta a dai-dai lokacin da har ta fara, ya kamo hannayenta duka biyu ya mikar daita tsaye yana cigaba da kallonta tana zubda hawaye gani yadda hawayen ke gangarowa bisa kuncinta yasa gaba-daya ya rud'e hankalinsa ya tashi ko ba'a faɗa masa ba yasan ita da ma'aruf ne tunda gashi zaune cikin saurin yace "no my princess karki min hasarar hawayenki ta runtse idanunta gam hawaye suka K'arasa zubowa , ya saki hannunta daya yana goge mata hawaye" karki yi kuka waye ya taɓa min gimbiyata ?
"Gaskiya za mu samu matsala da ko waye fa a gidan ina dalili a dinga wahalar min da Mata"

alhankali ya zaunar daita shima ya zauna" plz karki bata fuskarki da hawaye I don't want see your tears"ya faɗa yana ciro hanky da sauri ya cigaba da goge mata,
"ma'aruf ne Kou ?
Barni dashi nasan yadda zanyi dashi ,ƙarin girma zanyi miki ta yadda dole ya girmamaki ,ya ɗan kalli inda ya Abdurrahaman yake tsaye " wa me yasa Maaruf baya min kara ?
" abinda bazan taba masa ba shi yake min akan ummita" ..
Ya Abdurrahaman yayi murmushin takaici sannan ranshi a bace ya zauna yana fuskantar Ma'aruf "gaskiya baya kyautawa, ni kaina ina jin haushin haka "kullun sai na samu labarin abinda yake mata ,dan Allah ka kyale yarinyar mutane haka ta huta"

ya rayhan ya dubi ya Abdurrahaman "Ni dai yaya ka faɗa masa babu ruwansa da ita" ,duk ma abinda tayi masa ya dinga faɗa min tunda ni zan aureta zan san abun yi"
yayi maganar yana juyowa inda Maaruf yake zaune " dan Allah ka bar min lafiyarta haka ta huta bana son ganinta cikin damuwa da tashin hankali idan wani abu ya sameta baka da hasara, idan ma ya zama dole sai ka hukuntata ni ka dinga hukunta ni ba sai kaci zalinta ba ya K'arasa maganar yana mikar daita tashi mu bar d'akin kafin inna ta fito suyi miki taron dangi"
Bai d'ago idanunshi ya dubesu ba har suka bar parlourn ya ja tsaki a fili sannan ya gaida ya Abdurrahaman aciki ya mike sambal akan doguwar kujerar mai zaman mutun uku ya kwanta ya dafe goshinsa da hannunsa ɗaya ,dayan hannun ya daura a saman cikinsa . ..
Su ummita basu K'arasa fita daga d'akin ba Inna ta fito daga daki tana washe baki "ungo ka zane min ja'ira yarinya mara kunya?
" babana karka barta ka lallasa mini ita" ,

"da sauri ummita ta dawo ai ba sai kinsa ba , idan zaki iya ai sai kiyi da kanki ta bata amsa tana sake yin gaba " ai kuwu Ma'aruf najin haka yayi wata irin super sai gashi abakin kofa ya damki kunkurunta " me kika ce munafuka? Ta saki ƙara "Ni wallahi ba ba munafuka bace ya rayhan yayi saurin rike hannunsa "dan girman Allah ka rabu daita ka rama akaina "
Maaruf yace " baka isa ba ita da tayi laifi ita zan hukunta ,ka duba duk yaran gidan nan babu wanda ke min irin abinda take min ,",kayi hakuri dan bazata sake ba saketa "kar ya sake ni ya kashe ni kawai kowa ya hutu ai kuwa tana gama faɗar haka ya yarfa mata mari ..
ya sake daga hannun zai kara mata ya Abdurrahaman ya tare sa "
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On WANNAN CE QADDARARMU
avatar
amina-4

11 months ago

Reply

Interesting novel

avatar
amina-4

11 months ago

Reply

Interesting novel

Please Login or Register in order to submit comment