Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

acikin zuciyarta ,bata jin ko tana sonshi zata iya aurensa ,yafi cancatar ta yakice sonshi ko dan tsanar da mahaifiyarsa take wa mahaifiyarta ......

Can kasan makoshinsa ya sake cewa "zaki aure ni subai'a ?
" ki taimaka ki faɗa min abinda ke zuciyarki wallahi muddin na rasaki mutuwa zanyi, zan mutu subai'a ,idan na mutu karkiyi kukan mutuwata dan kice sila ...
daga yau zan sakawa raina takaitacciyar rayuwar da zanyi tun da baki so na ...
Cike da sanyi murya tace "ka daina cewa bana sonka ya rayhan ,kai fa d'an'uwana ne na jini, ta ya ma zance bana sonka ?

"da gaske subai'a kina sona kuma zaki aureni ?
Yayi maganar hawaye na gangaro masa,dan Allah kice zaki aureni ko ruhina zai samu salama "I will think about it ya rayhan , ka bani lokaci dan yanzu I have no idea to say anything . .......
Ta fad'i haka zuciyarta na wani irin tsalle tamkar zata fasa kirjinta ...


Bai san sanda ya rungumeta ajikinsa yana murna yana shafa bayanta, yana zuba sambatu iri iri "kiyi tunani mai kyau akaina , Allah yasa zuciyarki ta amince dani amatsayin abokin rayuwarta ,suna cikin wannan halin ne ya ma'aruf ya buɗe kofar parlour'n ya shigo idanunsa ya sauka akansu , ya tsaya turuss yana kallonsu makale da juna ga rayhan na kuka yana rokonta ta so shi ..
wani irin dogon
tsakin ya ja wanda yasa take suka dawo da hankalinsu bakin kofar da yake tsaye ,take ummita ta soma ƙoƙarin ya rayhan ya sakar mata jiki amman yaki .
"Allah ya shiryeka rayhan ,yanzu daman wannan iskanci kukeyi? "amman dai kunyi hasarar rayuwa
"Yanzu wannan ce irin taku kalar soyayyar ?
"Idan baka ji kunyar yin irin wannan kazamar soyayyar a part din mama ba ,kaji kunyar aikata hakan a matsayinka na suruki ga muhalin ,ka wani zo ka tasa yarinya qarama gaba kana kuka saboda baka san ci....

"Dakata malam babu ruwanka da shiga lamarin mata da miji, ina ma ruwanka da kuka na ?
"Idonka ko nawa da zaka dinga gayawa mutane son ranka kamar kai da kaninka ?
" idan kaji haushi kai ma kaje kayiwa taka ......
Jikin ummita na rawa tayi ta ƙoƙarin zame wa daga jikin ya rayhan dan wata irin azaɓaɓɓiya kunya ce ta kamata a lokacin kasancewar wannan shine karo na farko da jikin wani namiji ya rabi nata irin haka "aikin banza aikin wofi kawai ,ni ina naga wannan stupid time din yaja tsaki tare da juyawa zuciyarsa na tafarfasa ya nufi d'akinsa .. ..


Hannuwansa duka yasa ya kamo fuskarta dashi yana kallon cikin kwayar idanunta , ban da godiya babu abinda ya rayhan ke yiwa ummita ita kuma tana kuka "ki daina kuka ummita ni ina sonki koda kuwa bakya sona ,zan rayu dake muddin rai mutuwa ce kawai zata rabani dake ,zan koyar dake yadda zaki soni muddin muna tare ,zanyi komai dan ki soni zan zamo tamkar bawanki ....

Mikewa tayi jikinta na rawa ta nufi hanyar d'akinta tana kuka har da shesheka "me yasa na amince masa da zanyi tunani akansa alhalin bana sonsa ?
"why why subai'a me yasa kika yi haka ?"kamata yayi ki fahimtar dashi matsayinsa ba wai ki daurawa kanki nauyi ba ..
Ta dade kwance tana kuka tana bleming kanta, har kusan magariba tana daki kwance a d'akinta taki saukowa kasa , shigowar mama uku tana tambayarta ko lafiya take.."Tace lafiya lau.. daren ranar ma kasa runtsawa ,yadda taga rana haka taga dare cike da tunane tunane tana assessing maganarsa ta runtse idanunta tana lissafin yadda zata goce masa batare da wata matsala ba ....
Washegari ma shigowarsu meenal da sa'ada ne yasa ta ɗan warware ta saki ranta .

******
Tun karfe tara na rana Sa'id da jafar har ma da tahir abokansa suka kawo masa ziyara kamar yadda suka sheida masa ,
hayaniyarsu ce ta cika d'akin haɗe da sautin music ,sai dai duk abinda suke ,ban da Ma'aruf dan hankalinsa baya garesu yana ga sakonnin da suhaima ke turo masa .

_slm fatan kana cikin koshin lafiya ?me nayi maka ?ka share ni ka daina daukar kirana gashi Ina kewarka habibi, ka manta da rayuwar suhaima kou? kana can kana harkokin gabanka ko ?ni ina nan ina fama da tunaninka, duk motsi duk second kana cikin raina ,duk yini yau kana makale a zuciyata na kasa samun sukuni _

Yana gama karantawa wani sakon na shigowa

_help me with happiness ma'aruf Na rasa gane kaina ka taimaka bana cikin natsuwarta ,if not zaka ganni a unguwarku_

Wannan sakon nata yasa ya gyara kwanciyarsa ya tura mata text .

_ki hutawa rayuwarki suhaima .. Cool ur maind temper and remind d good things in your life na tabbata zaki sami natsuwa ba sai kinzo inda nake ba, dan zuwanki babu abinda zai kareki dashi sai zallar damuwa, idan na samu dama zan shigo kina raina_

Sai yamma sosai su jafar suka fito wajen gidan inda suka saba zama , yayinda Ma'aruf ke cikin part dinsa yana shirya kansa cikin riga t shirt mai ruwan haske da wando baki ,turare mai sanyi dadi ya ɗauka ya fesa a ilahirin jikinsa ya fito yana ƙoƙarin daura agogo a tsintsiyar hannunsa, ɗaya fito sai daya zarta dukkanin abokansa a kyau da komai ,Jafar ne yayi masa gurin zama ..

ma'aruf tare da abokansa a majalisar kofar gidansu suna shapter wanda hirar duk akan kwallo ne ,yayinda a hankali su ummita suka sanyo kai suna fuskantar get din gidansu dawowarsu kenan daga makaranta yamma, kowace sanye take da uniform din mahad ,tunda suka dosu idanun Sa'id ke kan ummita gaba-daya ya bar abinda yake ya tattara natsuwarsa kacokan akanta har suka qaraso daf dasu , dukkaninsu babu wacce bata yi gaisuwa ba saɓanin ummita da ko kallon inda suke batayi ba, ta ɗauke kanta daga jafar har Sa'id da tahir ita suka bi da kallo a natse take takunta kamar koda yaushe wanda rashin kibarta ne ke sake bata damar rausaya jikinta .....
har lokacin muhd Sa'id gaba-daya ya tattara hankalinsa akanta yana binta da wani mayataccen kallo kamar tsohon maye....jin duk sunyi dip a hankali ma'aruf ya maida hankalinsa kansu ,gani yayi muhd Sa'id ya shagalar ga kallon ummita ,da saurin ya ta'ba kafarsa muryarsa can kasa tamkar ta me koyan magana yace "kai meye haka ka wani zama kamar wawa ?
Firgigib muhd Sa'id yayi saurin dawo hankalinsa yana shafa sumar kanshi sannan ya sauke ajiyar zuciya "gaskiya yarinyar nan masha Allah ,Allah yayi halitta,duk sanda zan ganta gaba-daya sai na rasa kuzarina da natsuwata ma'aruf ya ta'be baki yana dubansa a kaikauce tamkar bai ji abinda yace ba , jafar yace "ummita ko ?
Muhd Sa'id ya lumshe masa ido alamun "eh "
"Ai gaskiya yarinyar tayi sai ka fara neman fada a gurin yayanta ..
Ma'aruf yayi shiru yayi tamkar ba dashi suke ba "aboki kaji abinda jafar yace ka taimaka ka....
"Dan Allah dan Annabi ban son shirmen banza anan wannan yarinyar ma ka cireta aranka dan rayhan ne yake sonta ,ko ma ba haka ba wallahil azim ban saka bakina ko mutuwa zakayi sai da ka mutu.......
Jafar ya kwashe da wata uwar dariya "ai nasani... "nima wallahi tsokana ce kawai , kai Sa'id idan har da gaske kana sonta ka nemi Sa'a agurin Allah sannan ka tunkareta ba tsoro , Sa'a ce soyayya sai kaga kayi nasara akanta , maganar ummita suka cigaba da yi, hakan yasa ran ma'aruf ya dinga ɓaci zuciyarsa ta cure guri daya ya rasa abinda ke damunsa ....
tsam ya mike a cikinsu ya soma takawa a gefen titin unguwarsu hannanuwa duka zube cikin aljihunsa wandonsa, bayansa suka bi da kallo cike da mamaki a hankali jafar ya biyosa "ya zaka barmu zaune ?"dan Allah ka daina nuna zallar qiyayyar yarinyar nan agaban kowa ko babu komai jininka ce ita dole idan an tsaga jinin ummita aga naka haka kaima "stop telling me this nonsense i don't want hear anything from you just go ......
"Ka barni karka cigaba da bina bana son damuwa cak Jafar ya tsaya yana dubansa ,shi kuma ya cigaba da takawa ko ina zashi oho jafar ya furta haka a ranshi ...

********
Da misalin ƙarfe takwas na washegarin ranar ummita tana zaune a parlour'n ita da sa'ada tana yiwa Ahmed dan big sister lesson kasancewar yazo musu hutu ,saifullahi kanin ya rayhan ya shigo parlour'n a guje wanda bai wuce shekara bakwai ba yana haki "aunty ummita wai kizo kin yi bako..

daga mama har ita ummita suka bishi da kallo ummita ce tayi karfin halin cewa " waye bakon ?
"Wani mai kyau ne bansan shi ba , ummita ta kalli mama wacce daman ita take kallo "kaje kace masa bana nan..

"dan Allah kinje mana baki san ko waye ba inji cewar sa'ada "karki 'bata bakinki gurin cewa naje dan babu inda zani kin sani .......
"kinga Malama maza dan Allah ki tashi kije mama ta faɗa tana harararta ummita tayi shiru kuma taki mikewa "ba da ke nake magana ba kina jin
Mutane wallahi ki yi ahankali da ...

Da sauri ummita ta mike tun kafin mama ta sake furta wani abu ta fito saifullahi na biye daita .....


Hannunta rike dana saifullahi suka nufo harabar gidan kamshi turarensa mai sanyi ya ziyarci hancinta, wadataccen hasken fitilun daya Wadaci harabar gidan shi ya hasko mata farar luxus dinsa dake parke da alamar bakon ne mammakinta ,domin matashin ne jingi a jiki motar ya rungume hannunsa sam bata gane ko waye ba ,bata son yawon samari ba dan abbanta baya so ba, sai dan raayinta ne rashin son kulasu ...

Naunauyen ajiyar zuciya ta sauke lokacin da idanunta gane ko waye tsaye tun daga sama har ƙasa take kare masa kallo
Takalmin karfashi baki ne wuluk sai shadda jikinsa fara sol agogon dake d'aure a hannunsa yafi komai daukar hankalinta yadda yake kyalli kiyasaninta ya tafi ne akan diomond ko gold ne, fari ne tasss dogo yana da hanci mai kyau a fuskarshi, bakinsa wawakeke , kallo daya tayi masa ta tabbatar ilimi da natsuwa haɗe da jin dadi sun gama ratsashi fuskarta babu yabo babu fallasa ta isa inda yake ,fuskarshi kunshe da murmushi shima ya nufota "Barka da fitowa ranki ya dade muryarta aciki tace ",Barka da zuwa ya hanya ?
"Lafiya lau gimbiya ya kamo hannun saifullahi "abokina yaya sunanka ?
Yaron ya rusunawa ya cire glass din idanunshi yace abbanmu yace "sunana saifullahi ,yace aunty ummita ta daina ce min saif kaima idan kace saif sai na faɗawa Abba ,muhd Sa'id yayi murmushin jin dadi "karka damu ni ma saifullahi zance maka kaji ,kawo glass din na saka maka naga ka kasa sakawa ..
Da sauri ummita tace "no karka saka masa ",kai aunty ki bari a saka min bayan kinsa ina so "maza cireshi ko na mareka saif me yasa baka jin magana ?
"ayi masa hakuri aunty kar amaresa yaro ne bai san komai ba tukuna yaja saifullahi jikinsa "yi hakuri abokina zan siyo maka dan karami yanzu ga na Sweet Kai da sauran yan'uwanka "sababbin kudi masu yawa ya mika masa ai kuwa saifullahi yayi cikin gida da gudu yana murna suka bishi da kallo ya saki wani kyakkyawan murmushi daya kawata fuskarshi ", Hajiya subai'a ya gari ya jin dadi?
Daure fuska tayi sosai tace "alhamdullahi ya zauna akan motarsa yana fuskantata "nasan zakiyi mamakin jin na kira sunanki alhalin ke baki Sanni ba ,amman idan kika kwatanta da kalmar malam bahaushe yace mai son d'an tsuntsu ......
Yayi shiru yaki garasawa yana Kallonta ta ɗauke kanta gefe tare da furta "amman dai da zaka min karin haske akan abinda yasa ka kirani zai fi ko ..?

Ya gyara zama "amman dai kinsa karin maganar nan da'ake cewa soyayya gamon jini ni kam na dade ina ji sai dai ban amincewa ba sai a yammacin jiya na dada tabbatarwa kaina jiya nazo kun wuceni zaune tare da yayanki ma'aruf gaba-daya kika ta fi da imanina na kasa fahimtar a wani hali nake dole na maida hankalina zuwa ga neman alfarma agurin yayanki ya ban wahala dan cewa yayi kar damu kaina akaina akwai wanda ke sonki , ba wai yau ne karo na farko dana taɓa ganinki a gidan nan ba , duk zuwa sai na ganki amman sam ke baki kallon inda nake asalima wani bangare kike kallo, ki taimkeni karki ga ina surutu kiji haushina ba laifina bane laifi zuciyata ce da tace subai'a kawai take so, atakaice dai na kamu da matsanancin soyayyarki mai girma a zuciyata yadda har nake jin ba zan iya cigaba da rayuwa ba matukar babu ke sai dai ina neman alfarma amincewar ki ki so ni koda cikin chokali ne ..


Ta ɗan tsaya tana kallona ina assessing maganarsa cikin zuciyarta tace" kai wannan mutumin ba dai surutu ba ,shima kallonta yake fuskarsa shimfide da murmushi ta ɗauke kanta gefe tana jin yadda zuciyarta ke dokawa saboda irin kallon da yake jifanta dashi


Two friend's (bsbs)
💗💗💗💗💗💗
WANNAN CE
QADDARARMU
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

~TRUE LIFE STORY~

FREE NOVEL NOT FOR SELL


AL'QALUMAN



*AYSHA A BAGUDO*
*FAIZA HAMMADU*


~DEDICATED TO~
MAIMUNA MATAR ABDULLAHI

BEST FRIEND FOREVER AND EVER, AKWAI AMANA 'KAWARMU ALLAH YA BARMU TAREN TARE SON SO FI SABILILLAH 🥰🥰

WATTPAD @HAUESH

bismillahirrahmanirrahim


PAGE 9


..........a qalla sun ɗauki sama da minti goma a tsaye bai sake yunkurin furta mata komai ba , illa kwayar idanunshi dake yawo a sansar jikinta wanda hakan ke sake harzuka zuciyarta, gaba-daya ta rasa hanyar da zata bi domin kufce masa , sosai ƙwaƙwalwarta ta shiga tunanin neman mafuta , dan dole tasan abun yi tun kafin ya qarar mata da ruwan jiki da waɗan nan mugayen idanuwan nashi masu bugar mata da zuciyata , bugu da qari bata son wan can kinibabben ya fito yayi mata shishigi , a hankali ta kamo lip's dinta na kasa ta soma ciccizawa ba tare da ta kalli inda yake zaune ba ...

Shi kuwa zuba mata idanunshi yayi sosai yana jin wani zallar farinciki mara misaltuwa na ratsa ko wani shashi na gangar jikinsa , ji yake tamkar ya sureta ya gudu gidansa daita so that daga baya an daura musu aure ...

"Kinyi shiru subai'a kin ki cewa komai, kin barni ni kaɗai ina ta faman zuba kamar ruwa ,a ranta tace "ai kama fi ruwan zuba dama shiru kayi zai fiyye maka alkhairi da wannan zubar da kake ....
ya shafa gaban goshinsa "shikenan tun da ba zaki yi magana ba a hakan ma na gode da lokacin da kika bani ,da farko dai subai'a sunana muhd Sa'id idris, mu huɗu ne a gurin mahaifinmu wanda ya kasance ɗan
Beru de change , nayi karatuna daga primary school zuwa jami'a, da farko dai nayi irin business din mahaifina kasancewar shine abinda na taso na tarar ana yi a gidanmu kafin daga baya na koma makaranta inda anan muka haɗu da yayanki mar'shub a halin yanzu dai nafi karfi a harka canji saboda yanayin yadda ƙasar tamu take , ban taɓa aure ba sannan bani da budurwa sai yanzu zuciyata ta kamu da matsanancin soyayayarki , wannan shine ta'kaiccen tarihina subai'a ina fatan za'a amshi bukatata mu dunkule mu zama abu ɗaya ....


Still dai shiru tayi masa tana wasa da yatsun hannunta , sai da suka sake kwasar minti goma kan ummita na kasa batare da tace masa komai ba , shi kuma yana aikin kallonta ko kifta ido baya son yi , komai nata yayi masa babu makusa ajikinta idan Allah ya taimake shi ya aureta zai ji dadin rayuwarsa da ita , yayinda ita kuwa ummita tunanin kalma ɗaya data dace ta faɗa masa wanda zasu rabu lafiya take , dan har ga Allah sam bai burgeta da komai ba asalima haushi yake bata .

tun daga kyan shi, kwaliyarsa , zuwa tsararrun takalmansa, kamshin turarensa ya ɗan bata sha'awa , abu uku ne kawai yasa taji a ranta ba zata iya sauraron kalaman soyayyarsa ba , ko bashi wani muhimmin abinda yake so daga gareta daidai da cikin cokali ba taji zata kaunace shi a cikin zuciyarta ba kasancewarsa abokin ma'aruf .....
"mutumin data fi tsana a duniya ,mutumin da take jin har ta koma ga mahalincinta ba zata taɓa barin wata mu'amula tashi ga tsakaninsu ba , mutumin daya tsaneta ya kuma tabbatarwa duniya da haka , ai ko ta rasa wanda zata so ba zata so Muhd Sa'id ba har abada uwa uba aikinsa daya ambata a yanzu shine mafi munin Sana'r data fi tsana arayuwarta , yayinda mafi yawa daga cikin yammata jahar Lagos suka fi bukatar auren 'yan canji saɓanin ita da ko burgeta basa yi , gaba-daya atsarinta bata da ra'ayin auren mai sana'ar canji ,sai kuma lura da tayi da yanayin tsarin maganarsa wanda sam ba taji abinda ya burgeta acikin maganganunsa ba , ya cika surutun tsiya kamar aku turu , yana magana bakinsa na yauki kamar ana kad'a miyar kubewa ....

"subai'a ya sake kira sunanta muryarsa a kasalance kamar zai yi mata kuka "ki taimaka kice min wani abu mana ko zan ji dadi ..
"baki ji yadda zuciyata ke cike da matsanancin tsoro da firgicin jin abinda ke kunshe a cikin zuciyarki ba " duk da ina cike da fargaba zan so naji wani abu daga bakinki ,ina jin tsoro subai'a gaba-daya yanayinki ya firgitani har cikin zuciyata nake jin komai ..
ta d'ago kanta a hankali murmushin maganarsa na ƙoƙarin subce mata akan fuskarta amman tayi saurin dannewa , sosai tayi ƙoƙarin boye sirrin zuciyarta dan su rabu lafiya ..
Shima murmushi yayi wanda daga ni na karfin hali ne " kin yi shiru dogon lokaci tunanin me kike yi subai'a ?
Muryarta a matukar sanyaye tace "ina tunanin kalma ɗaya da zan sanar maka ta gaskiya sai dai na rasa , amman zan so ka hakura dani ka nemi wata ....
"akan wani dalili subai'a ?
Tayi shiru taki cewa komai "dan Allah karki min haka na rigada na gama ruftawa akan 'kaunarki bazan iya son wata ba , kiyi hakuri kiyi tunani akaina mana ,har ga Allah. ina sonki kuma aurenki nake da buri yi " "shikenan naji zanyi tunani ....

Wani had'ad'd'en murmushi ya sakar mata kamar wanda aka yiwa bushara da gidan aljanna ,"na gode !na gode !! subai'a zan baki zuwa jibi idan kuma sun miki kaɗan na qara kimi " sunyi Allah ya kai mu "na gode sosai zan so ki sanar dani makarantar da kike yi . runtse fararen idanunta tayi saboda ya kusan kaita makura da surutu da kyar ta buɗe baki tace "a halin yanzu zan iya cewa bana karatu kasancewar mun zana jarabawar wannan shekarar amman zan cigaba da zarar sakamakon ya fito..

"cigaba fa kika ce auren fa sai yaushe subai'a ?
zaro idanun da yayi a firgice da maganarta da sauri , yasa ta ta'be baki tare da cewa "za'a yi idan lokaci yayi "kowane lokaci a cikin lokacinsa kike tunda aure baya hana karatu haka karatu baya hana aure ..

"Gashi ni kuma bana son haɗa abu biyu a lokaci ɗaya "shikenan Allah ya nuna mana lokacin ,Allah yasa dani za'a yi " Allah ya kiyaye ya tsareni da mugun abu ta faɗa acikin ranta ,"ba kice ameen ba subai'a "ikon Allah ko kai ka rada min sunan nan iyakar kiran da zaka min kenan ,me zai hana ka kirani da sunan da kowa ke kirana da dashi ...
tayi maganar tana shan kamshi tare da hura hanci ..
"To to shikenan na daina zan kiraki da duk wanda kike so, ko wani
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On WANNAN CE QADDARARMU
avatar
amina-4

11 months ago

Reply

Interesting novel

avatar
amina-4

11 months ago

Reply

Interesting novel

Please Login or Register in order to submit comment