Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

tashi a banza ba ,  sannan ki daina kuka dan babu rabuwa atsakaninmu har abada  muna  tare a gidan duniya har  ma aljanna kece shugaban matana aljanna ,maryam ina girmamaki ,kina da  kima da daraja  a idanun Ibrahim   ke din  yar aljanna ce , Allah ne gatana dake bazan iya rabuwa da me gatantani ba muddin ni zan d'aga miki kafa ki shiga aljanna na daga miki maryam daga yau sunanki yar aljanna  kalamai  masu sanyi da kwantar da hankali  abba ya dinga furtawa  mama  wanda ya kwantar mata da hankali har yayi nasarar yaye mummunar damuwar data kama zuciyarta ..

A can parloun'n kuwa tashi  ummita tayi  ta shigewarta  d'akinta   yana dawowa bai ganta ba dan haka    ya biyota dakin  ya zauna kusa daita "ki daina kukan nan haka  zai iya haifar miki da wani ciwo ya riko hannunta  cikin nashi ya tsarke  waje ɗaya  yana kallonta ,a hankali  ya dinga ji wani maganaɗisu sonta na shigar shi  yayinda sha'awarta   ke bijiro masa, bakinsa ya kai cikin  kunnenta yana busa mata iskar bakinsa yana  sakin numfashi "ki tashi  mu wuce gidanmu mu  fara  sabuwar rayuwar  ta fahimta  .
"kayi tafiyarka dan  babu  inda zani  bai  san lokacin daya birkitota saman  ruwan cikinsa
  ta kwanto a saman fad'ad'd'en qirjinshi  dukiyar   fulaninta suka sauka a fuskarshi  a hankali  ta furta ashiiiiiiiiiiii...
bakinsa ya kai saman dukiyar fulaninta ya manna musu  kiss   take tsigar jikinta suka mike ya ɗauki minti goma yana  kissing  brest  d'inta  yana goga mata kusaunbar  fuskarshi  ya karshe  ya  kamkameta a jikinsa ya  haɗe bakinsu guri daya ya shiga tsotsa da  kyar ta samu ta fixge  bakinta da yake aikin  sarrafawa ta sakar masa kuka "ni ka kyaleni  banaso abinda kake min  "dole ki so yarinya yanzu ma kikayi register..
"Ki  ko yarda ko karki yarda ina   sonki fatlion cikin kuka tace "you no tru love me sam bazan yarda da hakan ba duk bakin daya ki ko ya dawo yace yana so ba abun yarda bane ,"common listing to me fatlion sheshekar Kuka kawai take .......ki fahimceni fatlion  ni kome zaki ce sai dai ki faɗa amman bazan taba yarda ba ,zuciyata bazata taba yarda da bakya son mah'ruf ba in dai zuciyar mah'ruf zata soki dole kema ki soshi i will not let you down idan ma har da gaske bakya sona shijenan nima na hakura  ..

  Jikin ummita yayi mugun sanyi kunji ba ai daman tasan ba son tsakanin da Allah bane ,soyayyar karya ce taya ma zata yarda dashi  ? tashi yayi ya zauna yana shafa cikinta "bari na kawo miki abinci kici nasan ke da babyna kuna jin yunwa tayi shiru tana jin maganarsa tamkar a mafarki ta ɗan mintsi kanta dan tabbatar da shi din ne ko kuwa mafarki ne jin zafi ya ratsa jikinta ta tabbatar da gaske ne  ya cigaba da shafa cikinta "ki kwantar da hankalinki muyi zamanmu lafiya ko dan kwantar da  hankalin iyayenmu ba dole sai mun so juna ba  amman musan mahimmanci juna ya k'arasa maganar yana kai wa gefen wuyanta  kiss ta soma ƙoƙarin  janye jikinta ya sake janyota "ki dana fizge  jikinki ajikina kinsan ....
Shiru yayi sakamakon turo kofar d'akin da akayi meenal ce ta shigo sai dai da sauri ta juya "meenal ya kira sunanta da sauri ta amsa da na'am tana sake dawowa d'akin  ta tsaya "ina yini yaya ?
Bai amsa gaisuwarta  ba ya sauko daga kan gadon "ki kular min daita plz taci abinci  dan bana son wani abu ya taɓa lafiyar  babyn jikinta zanje na dawo  sauran kaɗan  dariya ta subuce mata tace "tam yaya ko dai naje na dibo abinci ne ka bata da kanka ?

Ya watsa mata wani mugun  harara "abinda na sakaki kenan dan ubanki da zaki miki wata irin tambaya ?
tayi saurin sunkuyar da kanta "to ai nima ba dadewa zanyi ba yanzu zamu wuce da Abdulshakur "wuce kije dan ubanki kai tsaye kuwa ta wucewarta tana murgud'a masa baki "kaji min yaya haka kawai zaka wuce akaina kai me yasa bazaka tsaya ka kula daita ni nayi mata cikin ?

Yana  fitowa  idanun mutanen gidan yayi masa caaaa dan duk sun dawo  parloun'n daga rakiyar baba sarki    ya bala'in  sha mur ya wuce d'akin  mama nan ma tare da mama rukkaya ya gansu   juyawa  yayi zai fita mama ta kirashi "baba ya juyo batare daya shigo ba "kana bukatar wani abu ne ?ya girgiza mata kanshi "kaje ka sake bawa inna hakuri kai da ummita  yace "naji atakaice   ya sake juyawa ..

Kai tsaye  kitchen ya nufa ya ɗauki plet da spoon ya buɗe  kula ,ya zuba  jollofy din shimkafa  wanda taji naman  rago ya diba ya dauki ruwan roba ya  nufi d'akin tana zaune  har lokacin ,menal na zaune  kusa daita tana tambayar yadda abun ya faru ,yana k'arasa shigowa ya tsareta da idanunsa yana watsawa menal   kallon banza ,sannan yace "dan ubanki ba tafiya kika ce zakiyi ba zaman uban me kike wa mutane ?"ummm ammmm "yi min shiru stupid  daman gulma ne ya kawoki  oya maza kafin na kirga uku ki kama gabanki tsimi tsimi ta mike ta fice  tana gunguni  ,ya  k'araso har kan gadon ya zauna ya ajiye roban ruwan akan bedside d'inta  yana kallonta   yana mata magana gabadayan jin maganar tashi take wani iri  ,ta saita zuciyarta sosai  tana son amincewa zuciyarta  abinda yake faɗa mata gaskiya ne ,  amman wani bangaren na zuciyarta yana karyata haka saukar muryarsa tayi a cikin dodon kunnenshi  "bude bakinki kici abinci yayi  maganar yana tsare gira kamar wanda bai taɓa dariya ba , ganin haka yasa ta motsa labbanta a hankali  "na koshi ,"ban gane kin koshi ba me kika ci ? yayi maganar a fusace "bake da kike d'auke   da ciki ba ko ni yunwa nake ji common ki bud'ewa mutane baki kafin raina ya ɓaci ,kin bude bakin  tayi har sai daya kai spoon bakinta sannan ta buɗe tana yatsina fuska a hankali ya dinga feeding d'inta tana amsa har sai daya tabbatar data koshi sannan ya barta  ya bata ruwa ta sha  yana kallonta yana qarasa cinye sauran abincin bayan ya gama ya  rike plet da hannu daya, dayan hannunsa ya riko hannunta "oya muje mu  bawa hajiya inna hakuri  "hakuri kuma ?ta faɗa kamar zata yi kuka "eh haka mama ta bukata kuma kinsan dole a cika umarninta shiru tayi batare da tace komai ba ta sauko ta biyo bayansa...

Da sallama suka shiga d'akin inna , shiru babu alamun  motsin kowa dan haka ya  sake sallama yana tsayuwa a tsakiyar  d'akin idanunshi an kan ummita ,  gunjin kukan hajiya inna daya ji ne  ya tabbatar masa da inda take  hankalinsa a tashe yace "ki tsaya anan bari na fara shiga, shiru tayi masa tare da lumshe masa idanunta ya kutsa cikin  uwar d'akan inna tana zaune akan gado ta jingina bayanta da abun gadon , kafarta ɗaya a kan ɗaya tana girgizawa, hannunwata duka suna kan katifa  tana kallon celling d'akin kuka take sosai kamar wacce aka sheidawa mutuwarta a lokacin ,ya k'araso ya zauna kusa daita ya riko hannunta "why hajiya inna kukan me kike yi? " komai ya rigada ya wuce  yanzu ma  zuwa muka yi mu baki hakuri  dan Allah kiyi hakuri ki yafe mana ya sake matsota "muna matukar sonki  ,shi yasa muke kyamatar wannan qabilancin dake  damun zuciyarki dan idan kika cigaba Allah zai  hukuntaki  akan haka ,ta sake rushewa da wani  kuka "akan maryam Ibrahim ke neman mutuwa ya barni kenan yafi sonta akaina ?"a'a inna ita fa  matarsa ce ,ke kuma  mahaifiyarsa ce bama za'a hada ba , muhallin uwa daban na mata daban ,zai iya rabuwa da mama ke fa kuna tare muddin rai kuma ina da tabbacin abba yafi sonki akan mama kinsan wani abu ?
Ta girgiza masa kai "idan ana zaman lafiya zaki fahimci abba yafi sonki akan komai dake cikin duniya ki duba yadda yake gudun ɓacin ranki ,duk abinda kika ce shi yake yi wannan kawai ya isa ki fahimci tasirinki garesa dan Allah kiyi hakuri kinji inna ki daina kin mama ...ta numfasawa tana sauke ajiyar zuciya ya tashi ya dawo parloun inda ummita ke tsaye " shiga ki bata hakuri  ,ta yatsina fuska alamun  bata son shiga "bana son mutsu ko  gardama kiyi abinda na saki  "kai baka bata hakuri ba ?"kina hauka ne ina baki umarni kina tambayata ?
Hanyar dakin ta nufa ta shiga tayi sallama a ciki inna dake zaune tana ganinta ta ɗauke kanta ta tsaya daidai saitin kafafunta jiki a sanyaye ta kai hannunta zata taɓa kafafunta tayi saurin janye kafarta shiru ummita tayi tana dubanta cikin haka mah'ruf ya dawo d'akin ya tsaya a bayanta tare da riko hannunta ya daura kan kafafun inna "kiyi hakuri dan girman Allah ,   muna sonki kiyiwa daraja annabi ki  sawa aurenmu albarka kamar yadda kika sawa kowa naunayen ajiyar zuciya ta sauke "Allah yasanya albarka "ameen ya cire hannunsa ya dawo kusa daita ya zauna "na gode inna Allah ya qara miki lafiya da nisan kwana ummita ta juya cike da sarewa ta koma d'akinta ta rafka tagumi "inna fa har yanzu batayi na'am daita ba ,me ye abun yi ?ta yiwa kanta tambayar sama da mintuna hamsin tana zaune tana tunani shi kuwa mah'ruf daga bangaren inna gida ya wuce saboda baba sarki ya tabbar masa da  kada ya kuskura ummita ta kwana a gidan ..

Jin ance a daren za'a raka ummita gidanta yasa  meenal  fasa wucewa ta dawo gurin Ummita tana kwashewa da  dariya "wannan love haka  daman nasan sai kun haukacewa juna "Ummita ta ta'be baki "a ina kenan ake wani love ?
"kin dai  kasa fahimta ne ni da yayanki babu wannan a tsakaninmu "na dai ji adai tausaya ma yayana dan naga ya rufta  da yawa karki wahalar min dashi  wannan rud'ewar da aka faɗa min  yayi akan za'a rabaku ya ..
"Dan Allah meenal ta daga mata hannu ,"nayi shiru oganinya kuma uwar gidan mahruuuuuuu...
Bari na kirawo wacce zata cancara miki kwaliya ummita taja tsaki .

Tun akan hanya ya kira suhaima  yace "ta tattara  komai data sanin nata dake  bangarensa ta maida part dinta ,dan nan bangarensa  Ummita   zata zauna kafin a gyara part dinta , hankalinta ya sake  bala'i tashi amman ta danne tace "to sai ka k'araso .

Karfe shida  daidai mama  ta kira     ma'hruf   ,ya zo  cikin farin yadi mai sharara tamkar wani sabon ango ya zauna kasa a gaban mama  cike da girmamawa  hannunsa d'aure da agogon fata baki ,ummita mama ta kira sunanta ta fito daga uwar d'akanta sanye cikin wata had'ad'd'en shadda gezner mai ruwan kasa cikin jikinta daya  ɗan taso  ya sake kara mata kyau ainun , hannunta d'aure da farin agogon magnet  mai bakin  fuska  mama ta  nuna mata kusa dashi da hannunta ta zauna  jikinta na fidda wani   kamshin mai sanya natsuwa da kwantar da hankali ,a hankali mama ta soma musu nasiha  tana sake tunatar da junansu hakkin kansu daya rataya a wuyansu  sosai ummita take kuka " Ummita ga amanar d'ana na baki kada ki curta min d'a , kaima baba ga Ummita nan ka riketa amana kada kaga yar'uwarka ce ka nemi take hakin suhaima akanta Allah ba zai barka ba ,ta sake duban ummita bana son azo min da wani matsala idan naji matsala kece kuma ki kuka da kanki dan nasan halin mahruf haka  nasan halin suhaima,  cikin kuka tace "inshaallahu  zan kiyayya "Allah yayi muku albarka  kana iya wucewa  "a'a mama bari kawai na wuce daita yanzu banason wani hayani ,da yake tasan halinsa ba tace masa  komai ba har sanda ya sanyata gaba suka fito zasu wuce  mutane suka masa caaaa  aikuwa  yace "babu wanda zai biyosa baya son hayaniya  a zo daga baya kamar wani biki za'a  wani kwashi jiki ,haka mutanen gidan na kallonsa ya wuce daita  tun tana kuka yana jinta har kukan ya tsaya ya kasance hawaye ne kawai ke fita  ya wuce daita part d'insa ya kwanta ya daura kanshi a kan pillow ya janyota jikinshi "wai ba zaki daina sheshekar  kukan nan ba sai na canza miki ?

Tayi masa bazan kiran  jafar  ne ya shigo wayarsa yana ɗauka yace "dan ubanka a she komai ya daidaita tsakaninka da matarka  shine ko labari babu ?
"A ina kaji ?
"Yanzu nazo  gida  sakina  ke faɗa min "ai kuwa  zan sake  canza mata  .
"Dan girman Allah ka rufa min asiri ni ne na tambayeta  ummita shine  take faɗa min abinda ya faru karka ballo min ruwa dan kulawar da nake samu adaina bani  tsaki  mah'ruf ya ja "aikin banza kai yanzu har canzawarta zai dameka   ?
"Sosai kuwa abinci wani guban wani ni ita nake so .. kit ya katse kiran bai ce mata komai ba ya janyeta a jikinsa ya fice daga dakin bata kara ganinsa ba sai dare ya shigo yace tazo taci abinci babu mutsu ta mike dan fuskarsa babu alamun wasa
Ko  gurin cin abinci Ummita bata kalli inda ma'hruf  yake ba, mamakita  a cunkushe a zuciyarsa  ya d'ago ya sanya kwayar idanunshi cikin nata cike da jin haushi taki cin abinci, suhaima na kallonsu dadi ya cikata ganin ba wani alamun tana farinciki da tarewarta .

Muryarta cike da kissa tace "haba ki saki jikinki kici abinci karki takura babynmu tunda sai kinci sannan shima zai samu yaci ummita ta galla mata harara "meye matsalarki dani karki dameni cikinki ko nawa ? Ta faɗa a fusace tana watsa mata harara ..

"Shiiiiiiiiiii karki zageta daga abun arziki ko sa'arki ce ? mah'ruf yayi magana yana tsareta da manya idanunshi "idan kika sake faɗa mata bakar magana zan..
"No habibi ka barta nifa banji komai ba kasan lamarin masu ciki sai a hankali "nata har da iskanci ki soma cin abinci tun raina bai gama ɓaci dake ba, batace komai ba ta maida hankalinta ga plet din gabanta   daga ma'hruf har ummita babu wanda yaci abincin karki sai tsakura da sukayi, bata wani ci abincin ba   ta mike ta bar gurin ta dawo part dinta ,kwanciya kawai tayi  tana juyi bacci ya kauracewa idanunta, tunaninta duk yana  kan  ma'hruf data baro tare da  suhaima a hankali nadihar mama ta shiga dawo mata ..

Suhaima kuwa  kamar ta zuba ruwa a kasa ta sha dan dadi musamman ta bugawa Hajiya rahma  waya ta fada mata komai, dadi ya cikata tace "kin gani ko  makirci ma kawai ya isheki da haka zamuyi nasara akan shegiya daga karshe ki fitar daita  ,wani irin ihun dadi suhaima ta saki sakamakon wata mugun  kirsa da hajiya rahma  ta faɗa mata "kai yayarmu Allah ya bar min ke ai kuwa zanyi tunda asiri yaki cin tsinannu  ai mayi maganinsu ta hanyar  makirci  nan suka cigaba da hirarsu ta mugunta  ....

*****
Tsawon sati guda  Ummita bata wani sakewa da mahruf   zai shigo d'akinta ya kwanta idan ranar kwanta ne ranar da ba kwanta ba  zai shigo ya duba lafiyar  jikinta amman har lokacin zuciyarta bata gama amincewa dashi ba  duk abinda yake mata da ido kawai take binshi  shima bangarensa bai damu haka bai matsa ba yana son ta fahimci sonta yake ba wai jikinta yake bukata ba   ..

Ranar asabar da misalin karfe  tara na safe   yana zaune akan kujera mai zaman  biyu  system ne  a gabansa yana aikin tura sakonin  yayinda ummita  ke tsaye a bakin dres mirrow sanye da dogon  wando da riga  iya gwiwa tana  gyara gashin kanta daya zubo bayanta  tana ƙoƙarin bude  kwalbar kwallacca murfin  ya caki  farcenta ta saka ƙara tana yarfan da hannunta ,ya  d'ago a gigice  ya tashi jikinsa na rawa ya k'araso gareta ya rike hannuta yana kallon yadda  gurin yayi  ja "sorry ya saki hannu da sauri ya nufi inda man zafi yake ya d'auko ya dawo gareta ya lakato zai shafa mata tayi saurin ɗauke hannunta  .
"Karka damu ba wani abu bane  fa zanyi manage ,ta wuce shi  yayi shiru tare da cilla da man akan gado  yana jan tsaki  ,ya koma gurin zamansa zuciyarsa na dokawa da matsanancin karfin gaske ..

yana  tsaka da aiki   ya soma tarin  karya da sauri ta dawo kusa da shi  ta zauna " sannu me ya same ka bari na kawo maka ruwa tayi saurin mikewa  jikinta na wani irin  rawa sauran kaɗan ta  tunsura ta  tsiyayo  ruwa a cikin glass   cup ta miko  masa ya kalleta  yana girgiza mata "karki damu  ba sai na sha ba zanyi manage  tayi shiru tare da tsura masa fararen idanunta  tana kallonsa kirjinta na wani irin mahaukacin bugu ..  "wannan kawai alama ce ta  muna tsananin son juna , idan ma za'a iya bincikar zuciyarki  za'a iya samun  soyayyarki ta  dara tawa yana gama maganar ya dauke kanshi  ya cigaba da aikinsa .
Jikinta a sanyaye ta fice daga d'akin gabadaya  tana sauke numfashi "wayyo Allah nah Allah ka taimakeni  bana son ya fahimci irin son da nake masa ranar menal ta kawo mata ziyara sun dade a parlou suna hira har sanda mah'ruf ya fito ta gaishe cike da girmamawa ya amsa atakaice ya wucesu suka koma daki suka cigaba da hirarsu a hankali suhaima tazo ta la'be tana nad'e abinda suke cewa  .....

Ranar monday da misalin karfe shida na yamma   Ummita ta fito daga d'akinta tana sha'awar cin indomi  gabad'aya jikinta a mace yake   taku daya biyu  tayi  akan step  kawai    taji  tayi kasa gabad'aya an hantsilata  take ta saki  wani  razananniyar    ƙara ta soma mulmula  daidai lokacin da ma'hruf ya shigo  yana ƙoƙarin kulle motarsa ya jiyo 'kararta ya shigo  gidan aguje    hangota  yayi kwance a karshen matattakala dafe  da cikinta da mararta   ya saki wata gigitaccen ƙara tare da kiran sunanta a matukar firgice"  fatlion karar da yayi yasa suhaima fahimtar ya dawo gidan .

ta fito a gigice ta tarar dashi ya daura hannunsa duka a saman kanshi  tsabar rudewar  jinin daya gani  a kasa ,ta  karasa inda ummita take jujjuya kai , wani irin azaɓaɓɓen dadi ne ya kamata ,aranta tace" magana takare Allah kasa cikin ya zube  daga nan  ita da samun wani cikin sai dai taga ana yi dan duk abinda zatayi zatayi amman bazata yarda har ta samu cikin da zata haifa ba ita tana zaune  ,amman dan  tsanani makirci sai tayi  kan Ummita da sauri ta dagota ta rungumeta ajikinta  tana  kiran sunanta" Ummita Ummita garin yaya haka ta faru? idan ma wani abu kike so ai sai ki faɗa min  Inna lillahi wa Inna ilaihi rajiun, sannan ta waigo tana kallon inda ma'hruf yake ga mamakinta sai taga hawaye yake zubarwa haushi da takaicinsa  ya kamata, zuciyarta ta dinga tuttukin bakincikin mara misaltuwa amman haka ta waske tace "habibi ka taimaka mu kaita hospital tun wani abu bai samu cikin ba.

hankalinsa a tashe ya k'araso ya ɗauketa ajikinsa ya rungume yana kallon fuskarta  "shikena na rasa babyna "sakacinki ya janyo zanyi hasarar  babyna  ya sanyata a bayan  mota har lokacin idanunta na runtse sai dai bakinta bai daina salati ba da sauri suhaima ta shige bayan motar ta zauna tare da daga kan Ummita ta daura saman cinyarta tana Mata sannu .

gudu kawai yake akan titi  ita kuma suhaima tana yadda zata dannewa ummita makoshi ta rabata da rayuwarta gbdy  ikon Allah ne kawai ke tafe dashi dan  bai san inda yake wulla motar ba har suka  kawo asibiti ..

Nan da nan aka dauko gadon marasa lafiya aka daurata aka shiga daita ciki ya biyosu agigice shi da suhaima gaba-daya ya gama sadaukarwa dansa ko yarsa ya zama tarihi ,qirjinsa har dagawa yaje tsabar tashin hankali da yake ciki ya kasa zaune ya kasa tsaye sai safa da marwa yake a tsakanin dakin daaka shiga daita yayinda suhaima ta zauna akan jerin kujerun dake ajiye agurin tayi tagumi munafurci,cikin ranta  tana addu'ar Allah yasa cikin ya zube ..

Tsawon lokaci babu wanda ya cewa d'an'uwansa komai kowa da kalar tunanin da yake, zuwa lokacin zuciyarsa ta shiga sake sake da faduwarta, sama da awa daya doctor husain ya fito  suka rufeshi da tambaya "yaya dai doctor cikin ya zube ne ?
  Tausayinsa ya kama doctor ganin yadda ya dawo yace "ana bukatar jini amman dai zai fi kyau ...
"cikin jikinta fa ? mahruf yayi saurin  katseshi ta hanyar fadar haka "bamu gama gano matsayinsa ba tukun jini dai muka fi bukata kafin mu karasa bincikenmu  amman ka kwantar da hankalinka  ...

TWO FRIEND'S BSBS

💗💗💗💗💗💗
     WANNAN CE
   QADDARARMU
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

~TRUE LIFE STORY~

FREE NOVEL
            
      
AL'QALUMAN

*AYSHA  A BAGUDO*           
*FAIZA  HAMMADU*

~DEDICATED TO~
*NURATU IBRAHIM YAURI YAR KWANA NAYI MISSING DINKI*

WATTPAD @HAUESH

bismillahirrahmanirrahim

PAGE 56

"Inshallahu  babu  wata matsala , jikinsa duk a sanyaye  ya  rufawa likita baya  zuwa wani d'aki inda  za'a  ɗibi  jininsa , cikin  kankanin lokaci aka    gwada jinin  ,koda  likita ya  faɗa masa  jininsu ɗaya da ummita  bai  yi  mamaki ba  ,dan  a  yadda kamanninsu  yake zai wuya  hakan bata kasance ba .

ya  kwanta   akan  wani madaidaicin gado aka  dibi  jininsa leda  biyu ana gama diba likita  yace " ka huta  bayan ya   bashi  maltina  likita, yayi  shiru  a kwance yana  tunanin  ummita  da cikinsa  , zuciyarsa cike  take  da matsanancin  fargaban game   da halin da  cikinsa  yake ciki , ya lumshe idanunshi tamkar  mai bacci  alhalin  ba baccin  yake ba, a hankali gefen kansa  ya dinga sarawa   dan  shi  kanshi jin jikinsa  yake tamkar mara lafiya   saboda tashin hankali  da yake ciki ,suhaiman  ta shigo in da  yake  kwance  zuciyarta fal da  bakinciki adalilin  jininsa  da yayi daidai dana  ummita , taso a sha  wahala  gurin samu jinin  ko  kafin  a dawo ta  karasa  barzahu .

ta  zauna   kusa dashi ta riko  hannunsa  cikin nata  tana  taya shi jimami  tare  da kwantar masa  da hankali yayinda a zahiri  kuma addu'a take  Allah yasa cikin ya bare   ..

Kusan  awa  biyu likitoci na  tsaye akan ummita  sannan    doctor   husain  ya dawo d'akin suhaima  na  ganinsa ta mike  tsaye daga zaunen da take a gaban mahruf  ya  zauna  akan kujerar data mike  ya  fuskanci mahruf  yana mai tausaya masa ganin yadda hankalinsa ya tashi , cike  da rawar  jiki  mahruf ya mike  zaune  yana duban doctor  "Yaya  take  doctor ya cikin jikinta ?
"Bana  son  mu rasa cikin nan , wannan  cikin sanyi idaniyan  mama ne dani kaina ,  tunda mama   tasan  da cikin nan  farincikinta  ya karu , bama  ita  ba duk  wani masoyinta  yana farinciki da tayata  murna dan Allah karka faɗa min cewar mun rasa babynmu .......

"mahruf  doctor  husain ya kirashi  bai amsa ba illa idanu daya bishi dashi   "mu muslimai  ne masu imani , sannan  imaninmu  bazai cika ba har  sai  mun yarda da kaddara mai kyau ko akasin haka,  take wani sanyi ya lullu'be  mahruf sai dai  hankalinsa ya sake kololuwar tashi  "shikenan da alamun na rasa cikina yayi maganar a kasan zuciyarsa .

Dor'ctor  husain ya cigaba da magana bayan ya sauke naunayen ajiyar zuciya "mama  mai ilimi ce  bazata  ji babu dadi aranta  ba  sannan ba zataji  haushi  bisa hukunci  ubangijita ba.
Allah kan  jarabi  bawansa da kaddara  na  bakincikin dana  farinciki domin ya jaraba  imaninsa  ya gani ko  bawansa zai amshi jarabawarsa  da hannu biyu  biyu  ,ina son ka ɗauki   abinda  zan faɗa maka  amatsayin kaddararku  yayi saurin cewa "karka ce na rasa babyna na  wata  biyar going  to  sex  mouth dake jikin ummita ......?

Doctor husain ya tsura masa ido yana had'iye wani miyau daya tsaya masa a makoshi  Karo na farko  kenan da  doctor Husain  yaji mah'ruf  ya ambaci sunan ummita a hankali ya d'aga masa  kanshi   alamun "eh  yana kallonsa "cikin   jikinta  ya fita ko ince  tayi nakuda ta haifi abinda  ke cikinta wanda ya  kasance  twins Kuma duk  maza ,  wani irin ƙara mahruf  ya  saki yana ƙoƙarin durowa daga kan  gadon a gigice suhaima tayi saurin dafe kafadarsa  tana bashi hakuri  gaba-daya ya dimauce jin maza har biyu yayi hasara   "kayi   hakuri habibi,  haka  Allah ya kaddaro  mana wallahi ummita  ce bata jin magana  ,tana  da d'aurin kai tunda  ta dawo kullum  sai  nayi mata magana  akan  tsalle  tsallen  da take da cikin  gashi ta janyo  munyi hasarar  baby  har biyu  ta k'arasa maganar tana kuka wanda da gani na munafurci ne .

  "kayi  hakuri  ka  kwantar  hankalinka  ka mika  lamurranka ga Allah  sai ya sake bamu wasu 
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On WANNAN CE QADDARARMU
avatar
amina-4

11 months ago

Reply

Interesting novel

avatar
amina-4

11 months ago

Reply

Interesting novel

Please Login or Register in order to submit comment