Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

, a hankali yan'uwa suka soma yi mata liki kowa na alfahari daita hatta malamai na alfahari daita ,ta samu kyaututtuka da dama sakamakon kokarinta da tsafta tayi hoto da kowa amman banda ma'aruf ko da mama tayi mata magana cewa tayi" ta gaji ta shige cikin
Agurin walima tayi samari daban daban da suka nuna suna sonta amman taki kula kowa .

Ummita bata kula samari duk wanda yace yana sonta shikennan sun raba hanya sai dai idan bai furta ba, zata iya cigaba da gaisawa da mutun amman da zarar ka furta ba ita ba kai har abada ka zama makiyinta ,manya mutane na sonta haka ya'yan manya masu arziki da kyau da manya gida da motoci amman ita ko ajikinta basa burgeta , har ake tunani ko aljannu gareta shi kuwa ma'aruf ya rigada yasan babu wani aljanu kawai tsabar iskanci ne ..
********

Back to the story

Two friend's (bsbs)
💗💗💗💗💗💗
WANNAN CE
QADDARARMU
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

~TRUE LIFE STORY~

FREE NOVEL NOT FOR SELL


AL'QALUMAN



*AYSHA A BAGUDO*
*FAIZA HAMMADU*


~DEDICATED TO~
*KHADY PINKY YA KWANA BIYU FATAN ALKHAIRI*🤝🏻

WATTPAD @HAUESH

bismillahirrahmanirrahim


PAGE 19

......Da misalin karfe uku na yamma injiniya ya shigo bangaren Abba ya same shi da baki mutun biyu , sun gaisa cikin girmama juna , bakin biyu suka mike tare da yin sallama , bayan tafiyarsu suka sake sabuwar gausuwa sannan suka fara zantawa a kan abinda ya kuno kai cikin iyalinsu wanda basa fatan ya zame musu damuwa ..
Dogon lokaci suka dauka suna shawara akan lalle bazasu bada diyarsu ga muhd Sa'id ba bisa wani dalili nasu duk da sun san mahaifin muhd Sa'id din tsohon dan canji ne a jahar lagos kasamcewa shi Abba mai yawan mutane ne yasan jama'a sosai ....
Abba yace "a bar komai a hannunsa zai san yadda zai bullowa lamarin , naunauyen ajiyar zuciya injiniya ya sauke yana duban Abba sannan suka rufe wannan babin suka shiga hirarrsu ta rayuwar duniya ..

Tunda sakon mahaifinta ya iso kunnuwanta ta kasa samun natsuwar zuciya ,take zazzafan zazzaɓi ya rufeta ta lullu'be jikinta kamkamewa guri ɗaya tana jin kamshin turaren jikinta, tasan muddin ta bujirewa umarnin mahaifinta akan aurenta da ya rayhan tamkar ticket ta rabawa wasu daga cikin mutanen gidan ,wanda hakan zai sa har su samu damar yin shishigi a cikin rayuwarta data mahaifiyarta wacce ba taji bata gani ba ,ita yanzu ba auren ya rayhan take ki ba illa jarababbiyar uwar mai mugun hali aurensa tamkar ta tsoma rayuwarta cikin bala'i da iftilain da mahaifiyarta ta tsinci kanta ciki tsawon shekaru wanda har yanzu tana kunsar bakinciki ,ji tayi kamar ta kurma ihu dan tashin hankali ,a bangaren ya rayhan kuwa tun lokacin da yaji ya soma murna gagara yayi bai gama abinda yake ba yazo ya sameta koda ya shigo bangarensu ya tambayi mama ita tace masa tana d'aki bata jin dadi amman tasha magani take yar fara'a daya shigo daita ta dauke ya nemi farincikinsa ya rasa .
"Da sallamarsa ya tura kofar d'akinta ya shigo, gabansa ne ya ɗan fadi saboda yanayin daya ganta ,amman ya dake ya k'araso inda take kwance tare da yaye bargon data lullu'be jikinta dashi ,ya tsaya yana kare mata kallo musamman yadda jikinta ke rawa, kusan minti biyu ya ɗauka cikin wannan yanayi yana kallonta kafin daga baya ya kira sunanta cike faduwar gaba "subai'a ......
Bata amsa ba ta lumshe fararen idanunta hawaye na kokarin zubo mata shiru yayi na yan mintina yana sake kare mata kallo " well I don't care all what you fell about our marriage as far as I still love you ya ja numfashi da kyar ya sauke sannan ya soma magana muryarsa a sanyaye tamkar wanda zai yi kuka "subaia nasan ba kya sona, amman zai iyakar kokarin naga na koyar dake yadda zaki soni a rayuwa subai'a You are so different daga cikin sauran mata ban taɓa sanyawa zuciyata soyayyar kowace diya mace ba sai ke ,da sonki na rayu na girma .
tasa hannu ta fixgo bargon dake rike a hannunsa ta rufe jikinta tana jan tsaki acikin ranta ,ya samu guri kusa da fuskarta ya zauna tare da buɗe daidai fuskarta ya tsura mata ido " my happiness my princess kada ki samu damuwa zaki so rayhan wuyarta dai su abba su kai min ke gidana nasan yadda zan ladabtar da zuciyarki ta soni yayi maganar tare da mikar daita zaune ta yatsina fuska tana runtse idanunta ,ya jingina bayanta da pillow shiru tayi tare da lulawa tunani ya riko tafukan hannuwanta sai lokacin ta ɗan dawo daga tunani ta buɗe idanunta, suka haɗa ido a lokaci guda wanda suna iya jin numfashinsu tuni hankalin ummita ya sake tashi murmushi yayi yana busa mata iskar bakinsa dan yasan kan yan kayansa yau sai yayi da gaske da duk rigimar da zatayi masa ,sannu a hankali ya dinga kwantar da kai tare da faɗa mata kalama masu sanyi har ta ɗan saki ranta ya dinga janta da hira cikin sanyayyiyar muryarsa yana mata hira yana jin tamkar ya shige jikinta domin ji yake kamar ya sameta a hankali ya jata zuwa parlour'n kasa ya zaunar daita bisa kujera yana kwantar mata da hankali tun tana sharesa har tasoma biye masa suka shiga hira har sanda meenal tashigo ya fita ya barsu tare yana damka mata amanarta tayi murmushi "karka damu yaya zan kular maka da sister ...

*****

Bayan sallar isha'i muhd Sa'id ya aiko kiranta tana jin haka tayi wata irin zabura tare da firgita ,wanda hakan yasa
ran mama yayi matukar ɓaci ganin irin yanayin kidimewar da yarta ta shiga lokacin daya ta dauke kanta daga kanta cikin rawar murya ummita take fadin ni dai mama kicewa sadiq yace masa bananan kawai Allah bazan iya zuwa ba .....
Meenal tuni ta mike ta fice daga d'akin domin bawa sadiq umarni yaje yace gata nan zuwa dan tasan dole mama ta tilastata fita ..

Hajiya mama ta girgiza kai "ummita ki natsu rashin zuwanki bashi ne mafuta ba , abbanki yace a natse zaki yi masa bayani an bayar dake a samu ku rabu lafiya dashi ta tsigar mutunci sai ku rabu a mutunce , goge idanunki maza kije ki dawo kinji diyar albarka , yayiwa rayuwarki albarka dake da zuriarki ...

A sanyaye ta fito zuwa inda yake wani irin mahaukacin ajiyar zuciya ya sauke fuskarsshi da zuciyar na cike da tsantsar farinciki mara misaltuwa amman sai da gabansa ya fad'i saboda kallon yanayinta kaɗai ya isa ya fahimci dole akayi mata ta fito muryarsa sanyaye yace "Barka da fitowa gimbiya kyakkyawa acikin matan duniya , tayi shiru taki cewa komai ,yau ko yar gaisuwar da yake samu daga gurinta bai samu ba ,ya tsura mata idanunshi yana nazarinta cike da tsantsar kulawa da soyayya kafin daga bisani yace "lafiyarki kuwa subai'a?
Ya tambayeta yana leka idanunta taja da baya da sauri saboda hucin Numfashina dake ƙoƙarin kawo mata ziyara ", lafiya me ka gani tayi maganar cike da dakiya da miskilanci ?
Yayi murmushi "haka dai na ganiki wata iri , kiyi hakuri idan na takuraki ne wallahi duk kwanakin nan na rasa gane kaina kowa ma ya rasa gane kaina hatta iyayena sun rasa sukuni saboda ganina cikin damuwa dan Allah subai'a karki barni , har cikin zuciyarta tsoronshi take ji saboda yadda yake yi kamar zai ɗauketa ..
Ya sake matsowa sosai ta sake ja baya da sauri yayi murmushin " kwana biyu dai da alamun laifi nayiwa gimbiya ..
Ta dan sake zuciyarta "ba kayi laifin komai ba muhd Sa'id gani nayi a matsayinmu na muslimai bai dace mu dinga yin irin wannan tsayuwar ba kusa da kusa gsky abun bai dace ba kasancewar mu ba jinsi daya ba...
Ya tsotsa keyarsa alamun jin kunya duk da ya fuskanci alkibilarta yaja baya yana fadin "kinfink gsky saurauniya matan duniya , matso ki zauna nan sai na koma kan mota ni na rasa gane abinda yake damu sarauniyyata yau ko bakya jin dadi ne ?
Taja tsaki cikin sirriyar muryarta ta yatsina fuska kamar taga kashi "kawai dai ina jin bacci ne yayi dariya " barci shalelena lallai kina jin dadi subai'a" yau ina mutumina saifullahi ne bangashi ba ?
"Yana tare da baba sun fita tare "wayyohlly gashi kuwa yau har da tsarabarsa nazo Allah yasa su dawo da ina nan ,bata san lokacin data buɗe idanunta sosai ba ta kalleshi "mafoluku suka je fa yayi murmushi ",Ni har kin bani dariya ina mafoluku ina nan ,nasan zasu bazasu wuce shad'aya ba ina nan har su dawo tayi saurin zaro ido "dawa zaka kai shad'aya "tare da matata subaia abar Sona mana kalamanshi suka daki zuciyarta taji ranta ya sake ɓaci cikin muryarta daya fi kauna da son ji tace "muhd Sa'id zan so ka sauraren i da kyau kuma ka fahimci Ni zan sanar da kai mahimayyar magana wanda tsantsar gaskiya ce "ina souraronki Sweet heart ta kara hassala "kasan hadisin nan da yake magana akan cika alkawari wanda annabinmu mai tsarki ya faɗa cewa alamomin munafuki guda uku ne bansani ba ko kasan shi ..?
"Akwai idan mutun zai yi magana yayi karya ko rashin cika alkawari ko mutun ya amince maka kayi masa ha'incin "haka ne malama subai'a nasani ,iza hadasa kazaba....."alhamdullahi daman nasan kasani tayi saurin katse masa hanzari kuma gaskiya hausawa sunce ɗaya ce daga kinta sai bata a zahiri gsky Sa'id batun yanzu ba muke tare da yayana rayhan zuwa yanzu har magabata sun shiga cikin maganar bazan yaudareka ba muhd Sa'id a jiya nayiwa rayhan alkawarin bazan sake sauraron kowa ba,shi kuma alkawari abin tambaya ne bancika sai nace zan cigaba da sauraronka koda gaisuwar mutunci ne mu dinga yi na gode matuka da irin kaunar daka min ina mai yi maka fatan alkhairi Allah ya hadata mai kaunarka fiyye da yadda kasoni na gode da dinbin alkhairinka gareni ina mai sake baka hakuri yanzu zan shiga na kawo maka kayanka ga mamakinta sai taga ya bushe da dariya ..
A matukar tsorace take kallonsa zuciyarta na wani irin dokawa "Muhd Sa'id ka fahimceni kuwa ?
Ya fuskamceta sosai zuciyar tana wani irin tsalle tamakar zata fasa kirjinshi tayo waje har lokacin dariya yake "fahimtar kalamanshi ne suka sani dariya subai'a"ai duk wanda kika yiwa wannan alkwarin kuma ya amince ya tabbata wawa ai ita budurwa ta mai rabo ce yadda na ɗauki soyayayarki a zuciyata ruwa da iska wuta da dukkanin tsanani bazasu sani in janye ba wallahi ko dan shugaban kasa ne yake sonki zan iya takara dashi koda zai yi amfani da karfin mulki ya tureni in har Kinga na hakura dake ki tabbatar da kin zama matar wani abinda bana fata kenan mutukar ina numfashi baki fahimci girman sonki a zuciyata ba shi yasa kike tunanin wannan kalamanshi zasu iya sawa na janye kudiruna akanki ..
Sheshekar kukanta ne ya dakatar dashi cikin Muryar kuka ",tace shikennan muhd Sa'id Allah ya gani ban yaudareka ba tunda na faɗa maka gaskiya kaki yarda shikennan Allah ya bamu alkhairi ta juya da sauri dan tana cikin damuwa kashi da kashi ga rashin son AUREN ya rayhan ga muhd sa'id ..cikin matsanancin tashin hankali yake kiran sunanta subai'a subai'a amman ina ko juyowa batayi ba illa kara sauri da wani irin gudu ya sha gabanta "dan girman Allah ki saurareni bai kamata ki dinga yiwa matsoyinki na hakika korar kare ba kisani girman sonki a zuciyata ya kai ko kara kika saka bazan ja baya ba bani nayi zuciyata ba gani nayi zuciyata ta aminta dake kaɗai zata iya rayuwa sonki shine rayuwata ina sonki subai'a ta galla masa wata ƙatuwar harara "gashi ni kuma bana sonka ba "
Yayi wani malalacin murmushi "tun farkon zuwa na fahimci hakan banason takuraki dan nasan kina jin bacci sai dai ina son kisawa ranki inshaallahu sai kin zamo mallakina ...
Ranta a matukar bace da maganarsa taja kafa ta shige cikin gida ya samo yaro ya tura shi da ƙatuwar jaka mai dauke da tambarin M.S STORE
Yayi gaggawar barin gurin gudun ko zata koro yaron da kaya ..

Babu ko sallama ta kutsa cikin part dinsu tayi jifa da hijabinta akan doguwar kujera ta zube akan kujera ta fashe da kuka bata saurari maganar da meenal take faɗa mata ba "menene ummita kina jina sai kuka kike ta dawo kusa daita ga a raunane tace ",me ya saki kuka ko yayi miki wani abu ne ?cikin kuka tace ",na shiga uku meenal mutumin nan ko maye ne ?
Tsananin tausayin yaruwarta daya gama karya mata zuciya ya sata kuma itama tarasa dalilin duk sanda zata ganta cikin damuwa hankalinta ke tashi fiyye da kowa kodan su kenan Allah ya bawa mahaifinsu a hannu kujera ta daura kanta mama ta sauko da hanzarinta ta tsaya turus tana kallonsu zuciyarta cike da ta bayoyi .
"Lafiyarku kuke kuka kamar an aiko muku da sakon mutuwa ?
Shiru sukayi kowace ta kasa furta komai "ke Amina ba magana nake muku ba ?
Cikin kuka meenal tace "mama nima gani nayi kawai tashi tana kuma bata faɗa min komai ba ..
Mama ta watsa musu harara ",shine dan shashanci baki san dalilin kukan ba sai kema ki kama " to yaya zanyi mata nima hakan na tsinci kaina da kukan "ke ummita kiyi magana kina jin mutane "cikin sheshekar kuka tace"wallahi mama wannan muhd Sa'id din bazai rabu dani ba kuka ya sake kufce mata "kiyi hakuri ummita shi kuka baya magani matsala Abba ya daga labule yashigo parlourn tare da sallama ,bazan iya hana rayhan aurenki ba ummita tunda yana sonki so kuma mai girma da din dadawa so nake ayi aurensa tare dana maaruf ni ya zauna akan kujera yana fuskantarta "ni kaina akwai wanda nake da burin yazamo miji gareki amman maganar rayhan ya dakushe wannan cikar burin nawa ...
"Bama kukan auren rayhan take ba wannan yaron abokin ma'aruf ne yazo shine tunda taje ta dawo da kuka taki yin wani bayani sai kuka Abba yayi murmushin "to kina sonshi ne ?
Abba yayi mata tambayar yana fuskantarta da sauri ta d'ago tana dubansa sannan ta shiga girgiza masa kai " to ita Amina meye nata na kika ?
Mama ta kalleta "wai nan yaruwarta take tayawa kuka "kunga kuyi shiru lokacin da yake gyara zamansa akan kujera "Amina subai'a dukkanku ku tashi kuje ku kwanta kunsa bana shiri da mai kuka aikiwa nan take suka shiga goge hawayensu "yauwa ko kufa yan albarka Allah ya albarkaci rayuwarku "sanar dani ya kikayi da bakonki baki sanar dashi abinda mamanki ta faɗa miki bane?

Ta sake goge hawayenta ",duk nasanar masa Abba cewa yayi ba zai rabu dani ba wai dole sai ya aureni ni kuma bana son shi takarasa maganar tana kuma "kai ummita wani lokacin kamar jaruma Amman kuka baya miki wuya in Banda abinki cewa akayi an bashi ke shi ba igiya zai sa yajaki ba to ina damuwa take ?
"Kin bi kin daga hankalinki kin daga na yar'uwarki to duk ku kwantar da hankalinku gobe zamu dauki matakin daya dace har shi Ma'aruf dan haka shine karfin zuwansa gidan har ya ganki ya ciro hancky a aljihunsa ya fara goge musu hawaye yana zolayarsu sai gasu suna murmushi Abba kenan mutun mai saukin kai ...




Two friend's (bsbs)
💗💗💗💗💗💗
WANNAN CE
QADDARARMU
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

~TRUE LIFE STORY~

FREE NOVEL NOT FOR SELL


AL'QALUMAN



*AYSHA A BAGUDO*
*FAIZA HAMMADU*


~DEDICATED TO~
*AYSHA JB ,IYA RIGIMA , INA YINKI SOSAI ,INA SONKI SABODA SAUKIN KANKI INA SONKI DAN KIN IYA RIGIMA , INA YINKI DAN BAKYA FUSHI DAMAN KUMA AYSHA AKWAI SAUKIN KAI*


WATTPAD @HAUESH

bismillahirrahmanirrahim


PAGE 20

....kwance ummita take lamo akan gadon mama , sosai tayi zurfi cikin tunanin rayuwa yayinda idanunta dake kallon celling d'akin ke tsiyayar da ruwan hawaye , a hankali furuncin muhd Sa'id ke sake dawo mata daki daki har zuwa kan hukuncin abbanta akan aurenta da ya rayhan , zuciyarta ne ya cigaba da dokawar da yake kamar zai fito daga qirjinta , da kyar taja numfashi ta tsayar bayan ta lumshe fararen idanunta "yaya zanyi da rayuwata ?"
Ta yiwa zuciyarta wannan tambayar hawaye na sake gangaro ta gefen Idanunta " hakika auren ya rayhan shine babban kuskuren abinda zan yi a rayuwata....
"zan tafka kuskuren da har na koma ga mahalincina bazan daina nadama a rayuwata ba ..
"Hakika idan na aureshi zan dangwama cikin damuwa da bakinciki tattare da kunci mara misaltuwa ," bana sonka ya rayhan me yasa kake son dole sai ka aureni ...?
" matsawar ka aureni wallahi wallahi zamu dangwama cikin kunci da bakinciki dan ba zamu taɓa ji dad'in junanmu ba muddin rai ..
Tana cikin wannan damuwar ne mama ta buɗe kofar d'akin ta shigo tana ganin halin da take ciki zuciyarta ta harba amman sai ta girgiza kai tare da tsaida idanunta akanta tana jin matsanancin tausayin d'iyarta , ƙoƙarin had'iye nata damuwar tayi domin ta kwantar mata da hankali tace " ba zaki raba kanki da wannan damuwar ba sai ta illataki kou?
"Mama tayi maganar tana zama a gefen gadon tare da d'aga kan ummita ta d'aura akan cinyarta tana shafa sumar kanta.
" ki taimaki rayuwata ummita ki samawar zuciyarki salama, bazan iya jurar ganinki cikin damuwar nan ba ..."
kuka ummita take sosai har da shesheka tamkar wacce akayi mata wahayin mutuwar mama muryarta cike sheshekar kuka tace "bazan iya ba mama gara nayi kuka ko zan ji zuciyata ta rage rad'ad'in da take .... "
"kiyi hakuri mamana damuwarki na karyar min da zuciya ,kece farincikina nayi hakuri na tsawon shekaru amman bazan iya hakurin ganinki cikin damuwar nan ba" ta K'arasa maganar hawaye na zubo mata sharrrrrrr.........
"kwana biyun nan da kika sarkafi damuwa da tunani nima gaba-daya damuwa ta sarkafeni ki tausaya min mamana bana son ki shiga tashin hankali ...."
Suna cikin haka ma'aruf ya shigo d'akin bakinsa ɗauke da sallama jikinsa sanye cikin wando jeans da riga nevy blue mai dogon hannu sai dai ya nad'e hannu rigar zuwa gwiwar hannunsa yayinda kamshi turarensa na white aud ya mamaye d'akin ,turus yayi tsaye yana kallonsu cike da matsanancin mamaki "to me ya samesu haka suke kuka tamkar waɗan da aka aikowa da sakon mutuwa ? "
Take hankalinsa ya tashi saboda ganin hawayen mama a matukar sanyaye ya soma ƙoƙarin k'arasowa zuwa inda suke, sai lokacin mama ta lura da shigowarsa d'akin kasancewar kofar a bude take lokacin da tashigo ganin halin da ummita take ciki yasa bata maida Kofar ta rufe ba .
Mama tayi saurin goge hawayenta tana had'iye kukanta har sanda ma'aruf ya k'araso ya janyo kujera mirrow dinta ya zauna tare da tsura mata manyan idanunshi kana ya riko tafin hannun mama cikin nashi "mamana me ya saki kuka haka ?"
"Meye damuwarki dan Allah ki faɗa min bana son ganinki kina zubda hawaye banason damuwarki yayi mata tambayar ajere hankalinsa a matukar tashe , duk da yasan kukanta bazai rasa nasaba da ummita ba dan yasa itace dukk'annin damuwar mama .
mama tayi shiru ta kasa furta masa komai saboda bata son fallasa damuwarta har sanda ya sake magana sannan tace "babu komai ma'aruf damuwar ummita ce ta haddasa tawa banason ganinta cikin damuwa da tashin hankali , itace karfin gwiwata idan tana damun kanta da yawan tunani yaya take son nayi ....?"
Sai lokacin idanunshi ya sauka akan ummita dake kwance jikin mama ,tsaki ya ja acikin ranshi yana maida idanunshi kan mama dan bazai iya cigaba da kallonta ba , yayinda mama ke cigaba da shafa sumar kanta "to meye damuwar ? Ya faɗa yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa .
"wai akan aurenta da
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On WANNAN CE QADDARARMU
avatar
amina-4

11 months ago

Reply

Interesting novel

avatar
amina-4

11 months ago

Reply

Interesting novel

Please Login or Register in order to submit comment