Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

special name kike bukata daga gareni an ready for it "bare ma bana bukata tayi maganar atakaice.

murmushi ya sake yi "shikenan gimbiya bari na kyale ki haka nasan kin gaji sosai ya mika hannu gaban motarsa ya dauko envelope fari ya dawo gabanta ya tsaya "ga wannan kya sha ice cream , ta makale hannunta taki amsa ,shi kuwa yaki janye hannunsa ya tsareta da idanunshi gaba-daya ya makance akanta , a sanyaye tace "bana bukatar haka na gode "haba kyautar soyayya ce fa menene abun kin amsa ,nima fa wata rana zan fanshe dan ko tunanina akayi acikin kwana ɗaya na gode bare aka haɗa da mafarkina ....

Ta sake haɗe fuskarta sosai tamkar wacce aka aikowa da sakon mutuwa ,iya gaskiya ta gaji dashi , shi da kanshi ya fuskanci haka, "subai .....amm ummita zan wuce ba dan na gaji da ganinki ba sai dan nasan kina buƙatar hutu na gode sosai da lokacinki da kika bani sai jibi idan Allah ya kai mu ..
Taji dadi sosai da zai tafi a ranta "haba mutun kamar aku bai gajiya da magana "Allah ya bamu alkhairi " ko na rakaki zuwa kofar shiga cikin gida ..?
Ta d'ago da niyyar cewa a'a idanunta ya sauka akan ma'aruf , sanye cikin riga mai ruwan zuma da wando baki , kunnenshi makale da waya yana magana a hankali idanuwansu ya tsarke cikin juna ,ganin su yasa ya kasa cigaba da wayar da yake, yayi sororo yana kallonsu , kallo ɗaya tayi masa ta ɗauke idanunta akanshi tana jan tsarki a ranta , tayi tamkar bata ganshi ba , shi kuwa kasa cigaba da wayar da yake yayi ya tsura musu ido ko kiftawa ya kasa yi , ba wai mamakin ganinsu tare yake ba , a'a karfin halin muhd Sa'id din ya gani alhalin ya sheida masa wanda ke da muradin aurenta ,yanzu idan rayhan ya gansu tare bazai taba yarda babu hannunsa a ciki ba asalima haushinsa zai ji .....

Ɗan karamin tsaki ummita taja a cikin ranta dan ita kanta bata so ya fito ya ganta tare da muhd Sa'id ba , sai dai babu yadda zatayi ,a hankali ya ma'aruf ya
tsuke bakinsa tare da ɗauke idanunshi akansu zuwa wani bangare ya cigaba da wayarsa ..

Ganin ya ma'aruf yasa ta sake tamke fuskarta tamau dan kar yaji dadin a cikin ransa ,dan tasan dole zai yi farinciki ganin ta sausari daya daga cikin abokinsa dan burinsa kenan ya ganta tsaye da kowaye a matsayin tana zance , shi kansa muhd Sa'id yayi matukar farinciki da ganin da ma'aruf din yayi musu tare.

ya ma'aruf yana gurin tsaye yana waya sukayi bankwana ,lokacin ne wasu friend's dinsa suka fito daga bangarensa suna magana dashi suna shirin shiga mota har shi, amman gaba-daya hankalinsa yana kan Muhd Sa'id da ummita dake tsaye ...

"Kamar muhd Sa'id idanuna suke gani Kou ?
Inji cewar alkasim "shine mana me nene son yarinyar yake ko akwai wani abu ne ?
"Babu komai wallahi mamaki dai nayi dan ban taɓa ganin yarinyar tsaye tare da wani namiji ba, gsky zanyi farinciki matukar ya samu karɓuwa a gurinta, dan gaskiya ummita tayi ,irin matan da'ake yayi ce ,matar fita wacce za'a a jiye a gaban mota ce ,duk wanda yayi sa'ar mallakarta ya more..
"babu ma wanda zai sameta sai abokina inshaallahu dashi za'a yi , zan bawa abokina shawara tunda har yayi nasarar da aka tsaya dashi ya kula sosai da duk wani motsinta saboda yarinya ce da wani zai iya yin wuf daita , kai acikin gidan nan ma akwai masu hari ,dan haka zan faɗa masa ya nuna mata so iya so da kulawa fiyye da kansa sannan ya nace da iyakacin karfinshi duk wuya duk runtsi ya K'arasa maganar yana ƙoƙarin kunna mota ...
"Wannan gaskiya ne ,ni kaina nayi mamakin kula shi da tayi "ba abun mamaki bane alkasim ikon Allah yafi gaban haka , sai kaga idan rabonshi ce komai ya daidaita a tsakaninsu,"ai dana san za'a iya kula kamar muhd Sa'id ,da tuni nima na sanyo kai ,dan ko ni yarinyar tayi min fuska ne ban samu ba shiyasa na tsaya matsayina ," wannan kuma bahagon zance ne ,karka zowa mutane da karys ka maida miyonka kawai dan abokinka ya rigaka..
duk maganar da suke ma'aruf bai yi ƙoƙarin cewa komai ba, illa maida hankalinsa da yayi akan suhaima dake zuba masa shagwa'ba ta cikin waya..

Ahankali ummita ta juya ta soma tafiya taji sautin muryar muhd Sa'id " dan Allah ki bari na rakaki mana Wallahi ban gaji da ganin wannan kyakkyawar fuskartaki ba karaf maganarsa ta shiga cikin kunnuwan ma'aruf ......
Ya ɗan yi shiru yaji amsar da zata bashi ,
ba tare data juyo ba tace "a'a na gode sai da safe ,tsayawa muhd Sa'id yayi yana Kallon yadda take d'aga kafafunta tamkar bata son takawa aranshi yace , " wannan yarinyar ba dai yanga ba ..yana tsaye har sai daya daina hangota sannan yayi murmushi ya qarasa inda su ma'aruf suke,ya mika musu hannu har ma'aruf suka gaisa , "abokina daga yau fa sunanka mai nasara dan da alamun kasamu karɓuwa inji cewar jafar "ina fa na samu karɓuwa sai zuwa jibi zan san matsayina nasara ko akasin haka ," Allah ya daura ka akanta ai da alamun zakayi nasara tunda har an saurareka ,"Allah yasa jafar ,kaga da yadda na samu ma ta min magana ,wannan yarinyar ba dai yanga ba, komai nata sai tayi yanga, maganarta kallonta kai komai ma nata ,har wani gumin wahala na haɗa tsabar firgici gaba-daya suka kwashe da dariya ban da ma'aruf " abokina ai kayi jarumta daman irin waɗan nan mata firgita mata suke nan dai suka cigaba da hirar ummita ....

kai tsaye ta zarce ɓangaren su gaba-daya mutanen dake zaune a parlour'n sun tattara hankalinsu akan kallo ,sai data yi sallama sau biyu sannan mama ta amsa mata ,ta zauna kusa da kujerar da maman take "mamana na bi umarninki naje na dawo ...."ko ke fa mamana sannu da zuwa ?Sannan ta mayar da hankalinta kan wasan da suke kallo challenge daga tashar kasar India..

Shad'aya daidai aka gama shirin gaba-daya yaran dake zaune suna kallo sun soma gyangyadi a gaban tv, ya rage daga mama sai sa'ada da ummita ,mama ta kallesu "ku tashi yaran nan suje su kwanta dare yayi kuma ku kwanta karku kasa tashi da asuba kusan gobe muna da baki , maza ummita kashe tv ki taimakawa Sa'adatu da yaran nan ...
"Tam mamana "

ummita ta K'arasa gaban tv ta kashe, sannan ta dawo ta taimakawa sa'ada tashin yaran tare da rakasu bangarensu, sannan ta dawo ta wuce d'akinta ta d'auro alwala tayi gado ta kwanta lamo tana tunanin ,"me zata cewa Muhd Sa'id idan ya dawo jibi ?
"me kuwa zaki ce masa da ya wuce baki son shi ya ƙara gaba ko zai dace...zuciyarta ta bata wannan shawara, take ta amince ,shawarar ta samu kyakkyawan mazauni a cikin ƙwaƙwalwarta , da wannan shawarar ta samu bacci yayi awon gaba daita ..

******
Washe gari

bangaren hajiya inna cike yake da jikokinta ciki kuwa har da ummita .. yaran aunty sha'awa ne suka kawo musu ziyara , sosai parlour'n ya hargitse da hayanirsu , hirar yaushe gamo suke sosai, kowacce ka kalli fuskarta kunshe take da murmushi da farinciki " ni kam ummita ina ya Ma'aruf ne ?Tunda muka zo ban sanya shi a idona ba ?
Ummita tayi mata banza kamar bata jita ba sai
Meenal ce tayi magana " ina ganin kamar ya fita "
ayya ya ma'aruf kenan akwai natsuwa wallahi ,kun san me wallahi ina addua Allah ya bani miji irinsa mai kyau da tsafta , ga fashion na ɗaukar hankali uwa uba miskilancinsa ....
ummita najin inda maganar ta dosa ta sake haɗe rai batare da ta tofa bakinta ba , Maryam tayi tsigil tace "ina ma ya ce .....
"Ina ma yace me ?
"Yarinya rufawa kanki asiri damu kanmu kafin yaji ki ya haɗa har mu yaci kaniyarmu inji cewar meenal ..
Khadeeja ta kwashe da dariya "gaya mata dai dan wallahi ba zai duba bakuntarku ba, dan haka ki canza maganarki tun wuri , ki dai fadi wani abu ban da wannan da kike shirin faɗa "
" ummita kinyi shiru ba kice komai ba "uhmmmm naji abun na kune shirme zalla ...
a ganina idan ba kaddara ba me za'a yi da wannan mugun kinibabben ?
"ni wallahi ban taɓa jin ya burgeni ba ,ku ko a kafa aka d'aura min shi wallahi kama shi zan yi na kunce na gudu uwa duniya bare inshaallahu hakan ma ba zai taɓa faruwa ba ," wani kyau ne dashi da har za ki wa kanki fatan Allah ya baki miji irinsa ?
Gaba-daya suka zaro idanu waje cike da mamakinta "eh wani kyau garesa kun wani kafe ni da idanuwa kuna kallona bayan gaskiya na faɗa ?
"Ni ban ga komai ajikinsa na kyau ba ,sam idanuna basa ganin kyaunsa idan ma yana dashi kenan "kai ummita wannan kuma karya ne kice ya ma'aruf bai da ..... "dakata maryam faɗa min abu daya mai kyau ajkinsa ?
"Bafa zaki gane ba tun da kullun kallon tsoro kike masa ,mu dai mun san yana dashi kuma dole mu yaba baiwar da Allah yayi masa " aslamiyya tayi tsigil tace ",,haba ummita meye haka ?
"wai me ya ma'aruf ya miki haka ne kika tsaneshi ?
"Dadin abun dai babu abinda zaki nuna masa sai dai ma ya nuna miki yarinya ?
Ummita ta ta'be baki "wannan kuma karyarki yarinya ,karki fad'i son zuciyarki "ba zan yi karya ba, mu ajiye maganar akwai yar tsama a tsakaninmu "me yake dashi idan ba zallar muni ba ?
' Karki sake cewa yana da muni idan bakya son shi, mu muna son shi a duk yadda yake tun da jininmu ne, ai ba haka kike wa ya usman ba ko dan shi dangin mahaifiyarki ne ?
"to an faɗa yana da muni yana da muni sai kiyi abinda zakiyi.... aslamiyya ta bude baki zata rama meenal tayi saurin toshe mata baki "dan Allah mu canza hira abar maganar yaya haka ,kema ummita plz Kar abun ya zama faɗa ......
daga ummita har aslamiyya sun shaka sosai sai hura hancin suke kafin daga baya ummita tace "usman daban kinibabbe daban bama matsayinsu daya ba dan haka kar a sake haɗa ya usaman da wani banza can mai kirar samudawa .....
Tana gama faɗar haka ta gyara zamanta tare da maida hankalinta kan amar daya shigo yanzu , cikin haka inna ta fito a dudduke daga uwar d'aga tana gyara d'aurin dankwalinta "ihun me kuke yi haka duk kun cikawa mutane kunne?
ta fad'i tana ƙoƙarin zama akan daddumarta tare da janyo wani ƙaramin gwangwani ta ciro goro ta soma gogawa ..
Meenal tayi saurin cewa "babu komai inna kawai dai hirar duniya ce, ta fad'i haka ne saboda sanin halin innar da tayi, dan tana jin akan me ake maganar sai ta maida abun bala'i karshe laifin ya koma kan ummita ..

"ke aminatuwa karki min karya fa naji an ambaci sunan babana ta karasa maganar tana watsa garin goro a bakinta "a ina inna ?
"gsky babu wanda ya kira sunan ya ma'aruf anan "ai shikenan "ke Khadeeja maza tashi kije bangaren mairo ki tambayo ko an gama ,ace har yanzu alkubus din bai yi ba gashi har yara sun fara jin yunwa, shiyasa tun safe nace aje kwakwa uku gidan hajiya rabi a siyo musu , dan kinibibi akace za'a yi"

"Kai inna me yasa kike yi haka ne ?
" mu bama jin yunwa yanzu duk sanda aka gama zamu ci "un go nan jaira na sake jin bakinki sai na cireki acikin jikokina ,ke kuma tsayuwar uwar me kike yi Khadeeja ba ai ken ki nayi ba kika tsaya min aka ?
Khadeeja ta fita tana gunguni, ta bar inna tana minta zagin mama ..


Bayan kamar minti goma saifullahi da Ahmad da Khadeeja suka shigo parlour'n hannunsu rike da manya kuloli guda uku , suka k'araso inda suka saba ajiyewa inna kular abincinta suka ajiye ,inna ta buɗe kulolin tana ta'be baki sai data kirge naman cikin miyar sannan ta soma da zubawa jikokinta na bangaren diyar macce , sai data zuba musu enough sannan ta zubawa kanta ta turawa meenal kular gabanta, ummita ta mike ta isa gaban meenal ta zauna har ta tsoma hannu inna tace "kai kai karki kuskura ki saka mata hannu kije gurin uwarki, nasan naki na can ta ajiye miki, dan kibibi shine zaki wani tsoma hannu cikin wanda na tsakurar mata"

Tsaki ummita ta ja " to wannan na ga damar ci dan haka karki takurawa rayuwata, idan kuma kikace zaki takura min bismillah sai abamu fili mu bawa hammata iska yanzu ,daman cike nake dake ..
aiko gama maganar ummita ke da wuya gaba-daya suka kwashe da dariya da ihu "kai ummita Allah barmana ke kina maganin inna wallahi ..
shi yasa nake son zuwa gidan nan ko dan chapter nan taku inji cewar maryam ....
Ammar yace "ai sai mu baku fali mu ga wanda zai yi nasara tsakanin ke da inna "kai ma kasan ko waye zai yi nasara inji cewar ummita "
"Bana son cika ba fa "kai raba ni da zance wannan tsohuwar da bata ajiye komai ba sai rikicin gangan "un go yar banza uwarki ce mai rikicin ganga bani ba .....

Two friend's (bsbs)
💗💗💗💗💗💗
WANNAN CE
QADDARARMU
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

~TRUE LIFE STORY~

FREE NOVEL NOT FOR SELL


AL'QALUMAN



*AYSHA A BAGUDO*
*FAIZA HAMMADU*


~DEDICATED TO~
MAIMUNA MATAR ABDULLAHI

BEST FRIEND FOREVER AND EVER, AKWAI AMANA 'KAWARMU ALLAH YA BARMU TAREN TARE SON SO FI SABILILLAH 🥰🥰

WATTPAD HAUESH


PAGE 10


......Ummita ta maida hankalinta gurin cin alkubus batare da ta sake yin magana ba , parlour'n ya ɗauki shiru na wani lokaci can meenal tace " hajiya inna dan Allah man shanu baya cikin sinadarin masu karin lafiya bayan dadin abinci da yake sawa?
ta faɗa tana kallon face din hajiya inna ,ummita ta riga hajiya inna magana "amman dai alkama tana cikin abinci mai gina jiki da inganci ko inna?
Hajiya inna da ammar suka kwashe da dariya tare da fadin "ai kuwa meenal man shanu har kusan zautar da wasu yake lokacin da suke cinsa, ita kuwa alqama karfi take sawa kamar doki dan idan ba'a yi Sa'a ba sai kiga mai ci ya haɗa har da tukunya alkubus din ,ke har ma da wacce ta yi alkubus din Idan bata kauce ba..
" uhmmmm bari kuga na mike kafin ku tashi kuyi kaina gaba-daya suka sake kwashe da dariya , ai ko take ummita ta haɗe rai "ba fa santi muke ba hajiya inna da zaki fad'i haka har da wasan zagin uwa ...
"Ke ni rufe min baki daman wa yace ku na santi ?
"Ba kuyi sanyi ba tun da gashi nan ammar ya tareku dan karku fadi, take suka kalli bayansu da gefensu duk kwanuka da kofina ne ya jera musu ummita ta jefa mishi gutun kashin da yake hannunta aiko kashin ya sauka akan goshinsa ,ya saki ƙara tare da rike gurin yana juya kai "dan wulakanci ce maka akayi santi muke ?
"Kunga muguwar yarinya da mugutar tsiya irin ta gado shine kika jefa masa bkashi
a idanu salon ki nakkasa min shi , ammar miko min kashin na rama maka, ai ko ummi ta mike da gudu tayi bayan kujera dan tasan halin hajiya inna zata aikata, ta rama masa, duk da wasa take masa saboda tafi son sauran jikokinta akanta, hajiya inna tayo kanta gadan gadan zata kwad'ata mata kashin ummita tace "kai hajiya inna karki jefa min wallahi da wasa nake masa ban san zai samesa a ido ba"

"dan uwarki haka ake yin wasa a garin tsohuwarki ?
"ki ɗauki kashin da kika gama tsotsewa ki jefa masa a goshi amman kice wasa kike masa ,kinsa Allah sai na rama masa ko mutuwa zakiyi ,ummita najin haka ta nufi kofar fita , ai ko daga ammar har su meenal dariya suka kwashe dashi har da rike ciki dan shi ma wasa nake bawai kashin ya same shi a ido bane .

ummita na ƙoƙarin fita daga parlour'n ba zato ta faɗa a kirjin mutun wanda bata san ko waye yake ƙoƙarin shigowa ba , a hankali dukiyar fulaninta ya sauka akan fuskarsa sannan ya zarce zuwa faffad'an kirjinshi , wani sabon bakon alamari ne ya bakunci tsokar dake makale da kirjinsa most especia daya ji tudun brest dinta a saman qirjishi take ya ɗauke numfashi tare da runtse idanunshi da sauri, yana jin zallar takaicinta kamar ya hankad'eta daga jikinshi , tuno mama yasa ya kasa aikata hakan .
Gaba-daya ahlin dake cikin dakin babu wanda zuciyarsa bata buga ba tsabar tsoro da firgici duk suka baza idanuwansu suna jiran ganin abinda zai faru , a hankali ya soma ƙoƙarin janye jikinshi daga gareta yana sauke boyayyiyar ajiyar zuciya ..
Ita kuwa ummita Kamshin turarensa daya kaiwa hancinta farmaki ne ya an karar daita da wanda sukayi karo , lumshe fararen idanunta tayi,take gabanta ya shiga dukan uku uku hankalinta yayi mugun tashi ,a hankali ilahirin jikinta ya ɗauki kyarma... ta soma furta kalmar "inna lillahi wa inna lillahi raji'un a kasan ranta yayin kirjinta ke dokawa da karfin gaske , ya ɗan tsaya yana kallonta fuskarshi kunshe da matsanancin 'bacin rai da takaicin haɗa jikin da sukayi daita ,yana jin tamkar ya shakota ya rufeta da dukan mutuwa amman darajan mama bazai iya aikata hakan ba dan haka ya ja tsaki yana watsa mata harara,
ita kuwa jira kawai take taji saukar mari a saman kuncinta amman taji shiru ....
kamshin turarensa da takunsa yasa bugun da zuciyarki yake Karu hakan ya sake bata damar fahimtar kusantota yake dan haka ta sake runtse idanunta gam tana ɗauke numfashi tare da qamewa guri ɗaya har sanda ya zo ya wuce ta inda take tsaye sannan ta sauke naunauyen ajiyar zuciya tana buɗe idanunta a hankali.......

kallon juna suka shiga yi da su meenal yayinda kowacce a cikinsu tashiga hankalinta ta kame kanta tare da yin godiya da bai mata komai ba .
A hankali ya samu guri kusa da Hajiya inna ya zauna yana sauke numfashi ,sai dai har lokacin zuciyarsa ita yake kallo wasu wurare daban daban na bud'ewa a cikin zuciyarsa mai tattare da tsantsar tsanarta "gaskiya babana baka kyauta min ba wallahi ,ai daka naɗawa jairar yarinyar nan duka..
" wai daga .. ..."dan Allah inna banason damuwa kaina ciwo .. "kai kuma matsalarka kenan da an d'auko magana kace kanka na ciwo , bakinka jikinka duk ciwo suke mutun kamar bayahude ,kai dai wallahi matarka na da aiki ja "plz
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On WANNAN CE QADDARARMU
avatar
amina-4

11 months ago

Reply

Interesting novel

avatar
amina-4

11 months ago

Reply

Interesting novel

Please Login or Register in order to submit comment