Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

mutane 'bacin rai dasu goge hawaye?

Kamar jira take a tambayeta ai ko take ta ɓare baki ta soma kuka har da sheshsheka"
wallahi mama idan ma'aruf ya sake shiga sabgana sai na masa abinda ba a taɓa masa ba "

"Oho ki ce dama ke da ma'auf ne toh kun fi kusa babu ruwana, "Allah ya sauwaka min mama ina ruwana da shi qazami ma irinsa Wallahi idan ina kaunar mutuwata to ina kaunarsa, ni dai mama kiyi masa magana ya fita rayuwata ..


"Allah ya shirye ki Ummi, ta wucewarta kitchen, Tana cewa "ban san yaushe zaku daina wannan halin naku ba Kullum Kamar wasu karnuka saboda fad'a gwamma ku gyara halin ku musamma ma ke da kike mace, gidan wani Zaki,"haba mama ko yaushe bayansa kike bi, ba Kya son laifinsa ai daman ni nasan ba zaki goyi bayana ba "

"Kiy iwa mutane shiru Ba ga irin rashin kunyar nan ba Ina magana kina bani amsa Allah dai ya shiye ki"


Ɓangaren ma'aruf kuwa tsaki yaja ya nad'e hannayen rigarsa ya nufi d'akinsa kai tsaye toilet din dake cikin d'akinsu ya shiga , tap ya kunna ya tari ruwa a cikin madai-daicin bucket ya soma wanka yana tunanin iskanci da ummi ke masa,Sam ya rasa dalilin da yasa ta raina shi, abinda yayi d'azu yayi ne dan ya tsorata Kuma ta dinga jin tsoronsa ashe a banza, ba canzawa zata yi ba,amman ya san maganin abun, ya ci alwashin gyara mata zama Koda kuwa hakan zai yi sanadiyar rugujewar zumuncin da ke tsakaninsu Yana wanka Yana tuna irin abinda zai wa Ummita dan su fita rayuwar juna , yana fitowa daga wanka ya shirya, ya fito yayi hanyar ɓangaren mahaifiyarsa yana shiga ya samu kannensa jidda da meenal suna cin abinci,suna ganinsa suka had'a baki gurin masa sannu da zuwa Amma bai amsa ba ya nufi uwar dakan inda yafi tunanin ummansa take suka kama kallon kallo , Jidda tayi ƙasa da muryarta dan kar ya jiyoyata tace" yanzu haka shi da Ummita ne "
Meenal tace
"su suka sani da matsalar su ni na rasa wannan bala'i sam basa shan inuwar juna ,"ai Kuma duk Yaya ne ya soma nuna mata tsana, ko nice fa ?
"banyi maka laifin komai ba kace zaka tsane ni ai sai inda ƙarfina ya tsaya,ni fa bana ganin laifin ummita dan ko nice zan yi fiye da abinda take yi masa, kullun a gurinsa ita ce mummuna, ita ce wawiya,ita ce fat lion jidda na kawo wa nan suka kwashe da dariya".
kai yaya bai yi ba kinji wani Suna Wai fat lion, ni na taɓa ganin a ce ana son uwa ba a son 'ya ?
"Ai kuwa gashi kin gani a gurin yaya ma'aruf Kullum Yana manne da uwarta amman baya kaunar ya bud'e Idanunshi ya ga diyarta, suna cikin hirar ummansu ta fito daga d'aki Kuma duk ta saurare abinda Suke tautaunawa tace "toh ya isa magulmata sai ku yi abinda ke gabanku idan Kuma Kuka bari ya jiyo ku wannan matsalar ku ce babu ruwana dan ko hakuri bazan bayar ba ..



*Two friend's ( b s b s*)
💗💗💗💗💗💗
WANNAN CE
QADDARARMU
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

~TRUE LIFE STORY~

FREE NOVEL NOT FOR SELL


AL'QALUMAN



*AYSHA A BAGUDO*
*FAIZA HAMMADU*


~DEDICATED TO~
MARYAM ALHASAN D'AN IYA
(MARYAM OBAM)

YOU ARE BEST FRIEND FOREVER AND EVER, AKWAI AMANA 'KAWARMU ALLAH YA BARMU TAREN TARE SON SO FI SABILILLAH 🥰🥰

WATTPAD @HAUESH

bismillahirrahmanirrahim


PAGE 2

.....Suna cikin haka sai gashi ya fito daga d'akin mahaifiyarsa fuskarshi a d'aure tamkar hadari, suna ganin shi kowacce ta shiga hankalinta tare da shan jinin jikinta ,hatta murmushin dake kwance akan fuskarsu sai data d'auke saboda irin kallon daya dinga aiko musu dashi ..

Tsaki yaja saboda duk yaji abinda suka faɗa , Ahankali ya d'auke kyawawan idanunshi akansu Yana mai zabga masu harara, sannan ya nufi hanyar fita daga d'akin "tafiya zaka yi tun baka ci abinci ba? umma tayi masa tambayar tana dubansa .

ya ɗan tsaya tare da juyowa ya sake tsayawa yana fuskantarta kamar yace mata baya ci ,zai ci a d'akin mama ,amman yasan halinta yana faɗar haka zata ji babu dadi, dan haka yace "ki bawa meenal ta kawo min part din mama, idan na fito daga part din Abba zanci acan ya k'arasa maganar Yana juyawa ya fice daga parlour'n.

Ko bayan daya fita ma babu wacce tayi ƙoƙarin sake yin magana daga menna har jiddah, illa ƙoƙarin tattara parlour'n da meena take k'ok'arin yi ta shige kitchen, ita Kuma jidda ta nufi d'akinsu tana zancen zuci ..

Da sallama ɗauke a bakinsa ya shiga part din Abba ,Abba dake zaune sanye da shadda blue ,yayinda babbar rigarsa ke ajiye a gefe Yana duba wasu mahimman bayanai, ya
dakata da abinda yake , ya amsa sallamar ma'aruf tare da d'ago fuskarsa Yana murmushi "A'a maaruf ne ?
"Har ka shigo kenan ?
"D'azu nake tambayarka gurin mamanka akace baka shigo ba tukuna "
A ladabace ma'aruf ya fara ƙoƙarin rusunawa kanin mahaifinsa har kasa yana gaishe dashi "Abba barka da dare ?
"Barka ma'aruf ya ƙoƙarin ?
"Alhamdullahi Abba ya fama da jama'a ?
Abba ya fad'ad'a fuskarsa da murmushi "jama'a kam gasu muna fama dasu ,sai dai muce alhamdullahi " shiru ne ya ratsa d'akin yayinda Abba ya cigaba da abinda yake shi kuwa ma'aruf bai sake cewa komai ba ,sannan baka jin motsin komai sai na iskar fankar d'akin da saukar numfashin ma'aruf dake zaune har lokacin ƙwaƙwalwarsa bata daina tunanin rashin kunyar da Ummita tayi masa d'azu ba ,abubuwanta na damunsa sannan tana bashi mamaki , abu mafi muni agaresa wai akanta yau suka kusan yin dambe da rayhan ?
Rayhan fa shine mafi kusanci a garesa bayan yan'uwansa ,tun tasowarsu babu wanda ya ta'ba jin kansu , komai tare suke ,duk hargitsi da bala'in da akayi a tun lokacin ganiyar kuruciya shi da rayhan lafiya lau babu abinda ya shiga tsakaninsu ,sai akan Ummita, yarinyar da ya fi tsana arayuwarsa ....
Wannan yasa gaba-daya yaji ya sake tsanarta kuma yana jin har ya koma ga mahalincinsa ba zai taɓa kaunarta ba ..

a qalla ya kusan minti talatin zaune agurin batare da yace komai ba, har sanda Abba ya sake d'agowa yana dubansa "lafiya ma'aruf na ganka haka ko akwai abinda ke damunka ne?

Alhankali ya d'ago har lokacin fuskarsa babu Annur ,da kyar ya iya buɗe bakinsa "babu komai Abba "kai dai ka sanar min idan akwai damuwar ne ?
murmushin karfin hali ya qaqaro "babu komai Abba ya fadi haka saboda yasan abba baya son ganinsa cikin damuwa akoda yaushe yafi bukatar ganinsa cikin farin ciki, kular abincin da aka kawo masa ya turo gabansa "ga abinci nan kaci daga ni baka ci komai ba" ban ci ba amman nasa akai min bangaren mama acan zanci "to shikenan idan ka shiga kace wa mamar taka tazo ""
Har ma'aruf ya mike Abba yace "ammmmm gobe akwai takardun da zaka saka hannu kai da Rayhan ƙarshen watan nan idan Allah ya kai mu nake son ku fara fita office "
"Okay Abba mun gode Allah ya ƙara girma da nisan kwana "ameen, ma'aruf ya karasa mikewa cike da kwarin gwiwa ya nufi bangaren mama ..

Zaune ya iske mama hannunta a daidai gefen kugun Ummita tana shafa mata man zafi, yayinda ummita ta runtse ido tana kuka tana ganinsa tayi saurin tamke fuska tana sauke hijabinta hawaye na gangaro mata sallamarsa tasa mama ta fahimci abinda yasa Ummita sakin hijab dinta da sauri , mama ta amsa masa tana maida idanunta ga Ummita "wai ma garin yaya kika ji ciwo irin haka da alamun kamar kashin gurin ya goce?
Kuka ta sake sanyawa mama shi kuma ma'aruf ya k'arasa shigowa ya zauna yana ware kafafunsa ,suka gaisa da mama batare da wata damuwa ba ya janyo tiren dake ɗauke da kular abincinsa ya buɗe ya soma ci ...


Da kyar mama ta ciwo kan ummita ta gaya mata yadda akayi ta ji ciwon ,lokacin da take bayani mama ta zuba mata ido sannan tace "nasan ai haka nan ma'aruf ba zai taɓa lafiyar jikinki batare da kinyi masa wani abu ba , nasan ƙarshenta rashin gurin kunya kika ji ciwon , "ke dai ba aikin ki rashin kunya ba ai kaɗan kika gani .

Muryarta cike da shagwa'ba tace "to mama ai shine yake shiga lamarina , amman kullun sai kiyi ta ganin laifina ta k'arasa maganar wasu sabbin hawaye na gangaro mata, haka nan yau ma'aruf ya tsinci kansa da jin kunyar mama akan abinda yayi gaba-daya ya kasa ci-gaba da cin abincin da yake , yayi shiru kawai yana sauraron kukanta ,har cikin zuciyarsa yake jin babu dadi ,mama ta wuce komai agurinsa, matsayin mahaifiya ce gareta ,bata haɗa shi da komai ba ,tunda suke rigimarsu da Ummita bai taba jin kunyarta irin ta yau ba ,da zai iya ,daya kaunaci Ummita koda cikon cokali ne ko dan darajar mahaifiyarta da mahaifinta da suka ɗauki soyayyar duniya suka daura masa amman bazai iya ba ...
Bazai iya mu'amala daita ba sam baya jin zai iya aikata hakan gara dai kowa yayi lamarinsa .....

"shikenan kukan ya isa haka ,idan kuma baza kiyi shiru ba sai ki cigaba ,dan mugun halinki ne ya jawo miki ,kai kuma ma'aruf ban ce ka raga Mata ba, Sau dubu tayi maka rashin kunya ,kayi mata dukan Kawo wuka tunda ita takamarta taurin kai da rashin kunya "
mama ta fada tana ƙoƙarin mikewa zuwa uwar d'aka "na gode mama Allah ya bar min ke ,domin ke din ta dabance ,ba Kya goyon bayan karya ,mama takarasa d'akin ta d'auko hijab dinta ta fito ta bar musu d'akin ta nufi bangaren Abba ..

Ta kasan idanunshi yake Kallonta tana goge hawaye batare da yace mata komai ba ,yayinda ita kuma ta cigaba da kukanta ,suna cikin haka yaya rayhan ya shigo d'akin da sauri ya karaso gareta tare da riko tafukan hannunta duka cikin nashi " wayyo my ummita me ya sameki ? Waye ya 'bata miki rai ?
"Waye yayi silar zubar hawayenki ?
Yayi mata tambayar ajere.
"Ki fada min bana son ganin digar hawayenki, ina jin zafi acikin araina a duk sanda naga kina kuka , ki taimkeni ki faɗa min nayi miki alqawarin zan rama miki kinji yar kanwata ya k'arasa maganar yana matse hannayenta cikin nashi haɗe da kai su daidai saitin bakinsa ya dumbata .

ganin yadda ya rud'e ya gigice yasa ta kirkiro dariya dole "babu komai fa yaya "ke dai faɗa min gsky ko ma'aruf ne yanzu na zubar masa da hakoran gaban bakinsa ? ya fadi maganar yana jan kumatunta ...

Kallon inda ma'aruf yake zaune tayi, taga ko kallon inda suke bai yi ba bare yasan da zamansu agurin , asalima kwanciya yayi rigingine akan kujera idanunsa na kan tv..

"shi ne ko inji cewar yaya rayhan ?
Muryarta Ahankali tace "kuguna ke min ciwo inda ya tureni ,shine yanzu mama ta shafa min man zafi ,wai dan na faɗa mats dalilin ciwon shine ta daura min laifi ,yaya ban san me yasa mama take yin haka ba ,kwatanta kwata bata sona, ta karasa maganar idanunta na ciccikowa da ruwan hawaye "no ki daina cewa haka mama na sonki fiyye da komai dake cikin duniyar nan ,kece fa duniyarta bata da wacce ta fiki , duk wanda zata so karere ne kece gold agurinta ,karki sake 'bata ranki kinji baby nah...

Ahankali ya dinga rarrashinta yana kwantar mata da hankali, yana goge mata hawaye yana janta da hira ,ita kuma sai murna take tana farin ciki ,dariyar ta yaya rayhan yake tayi acikin zuciyarsa batare da tasani ba ,Ahankali hirar tasu ta canza salo zuwa bangaren soyayyar su kuma har lokacin ma'aruf na zaune yana kallon first match din da'ake bugawa tsakanin bacerlona da arsenal sosai yayi zurfi a kallonsa , rayhan ya ɗan kai hankalinsa garesa ya lura gaba-daya hankalinsa baya gare su dan haka yayi kasa da Muryarsa sosai yana fuskantar Ummita sosai "my baby har yanzu fa ban ji gamsashiyar amsa daga gareki ba ?
Cikin karyar da murya Ummita tace "gamsashiyar amsar me ?
"Ni fa yaya rayhan banason abinda kake min da kuka ta qarasa maganar "subuhanallahi !"meye kuma abun kuka ana daga tamabayar amsar soyayya?
"kuka Ummita take sosai ganin haka hankalinsa yayi matukar tashi "shikenan kukan ya isa haka, yana taɓa min zuciya hanky d'insa ya ciro ya mika mata "oya goge hawayenki bana son ganinsu suna bugar min da zuciya ..

Kin amsa tayi tana sake matso ruwa daga idanunta ,ganin bata da niyyar amsa ,ya soma goge mata "ki daina min asarar hawayenki Please , a daidai wannan lokacin ma'aruf ya mike idanunsa na kallon kofar fita "idan ka gama wannan banzar shirmen naka kaje Abba na neman ka ,yana gama faɗar haka ya sa kai yana ƙoƙarin fita, fuskar rayhan a daure yace "naji amman ka sani idan wannan abun da nake yi ne shirmen ashe bani kaɗai nake yi ba ,wasu suma suna yi ya fad'i hk yana ɗauke kanshi zuwa ga ummita yayinda tuni shi ma'aruf ya fice daga d'akin.

"ke kuma ba zaki bar kukan nan ba gashi kinsa ana mana wani kallo ko?
Cikin sheshekar kuka tace "ka manta da wannan banza ,amman yaya rayhan bana so abin.....",tam naji nima na bari shikenan ?

Murmushi ta sakar masa yayinda shi kuma yake cigaba da share mata hawaye "kullun na ganki qara kyau kike min "kai ma haka yaya rayhan "a haka Ummita ina wani kyau anan ",Yes of course ai duk kafi mazan family's d'in nan kyau da natsuwa da haiba, yaya rayhan kasan me ?
Idanunshi kawai ya zuba mata yana kallon yadda take motsa labbanta da yadda take wasa da yatsun hannunta "sai kin faɗa my quenn tayi shiru tare da tsura masa idanunta ,jin tayi shiru yace "ina sauraron ki beauty ,kasa cewa komai tayi tana cigaba da wasa da yatsun hannunta saboda idanunshi "ki fada min abinda kike son fad'a zuciyata ta soma rawa ?"just tell me beauty ina sauraronki "ganin yadda ya rud'e yaji damuwarta kuma ita gskya take son ta fada masa, ya daina damun kansa akanta ,dan ita babu soyayya acikin tsarinta ,tsarinta ta samu wadataccen ilimi tayi zurfi a karatu har sai taga karshen biro amman ayanzu da yake zaune yayi bake bake agabanta tamkar zai maida ita jikinsa, kunyarsa ce ta kamata har taji bazata iya kallon idanunshi ta faɗa masa haka ba "dan haka tace masa "yaya rayhan ka kwantar da hankalinka babu komai fa "karki min haka mana Ummita idan kika boye min abinda zuciyar ki take son Fadi kinsa kin cutar da zuciyar yaya rayhan ɗinkin ?
"Subai'a tun randa aka haifo ki duniya na daura idanuna akanki Allah ya jarabeni da matsanancin soyayayarki ta d'ago cikin sauri ta tsura masa ido " haka ne subai'a kinsa wannan ba tun yanzu ba, tun daga wannan lokacin tunanina da hankalinka da komai nawa ya tattara akanki da lamarinki ,ina qaunarki zan so ki kaunace ni ,zan so na zama zabin zuciyarki ,zan so ki soni fiyye da kowa da komai dake cikin duniyarki,ki kaunace dan Allah ki sakani aranki kada ki sakani a zuciyarki ...

Narkar da fuskarta tayi "kai yaya rayhan duk ni kaɗai ai soyayyar tayi min yawa "no no batayi ba abinda ke cikin zuciyata kenan, zan so da zarar iyayenmu sun tambaye ki zabinki na zamo nine sawun farko "kai yaya rayhan tayi maganar tana murmushi sun dade a parlour'n suna hira yana lalla'bata har sai daya ga alamun tasoma gyangyadi sannan ya barta ya wuce ...


Washegari


bayan ma'aruf ya dawo daga gurin suhaima yarinyar da yake jin duk duniya babu wanda ya isa ya shiga tsakaninsu sai Allah daya haliccesa , a kofar gida suka haɗu da Abba, daya fito daga cikin gida jikinsa sanye da shadda fari da babbar riga , fuskarsa kwance da ruwa alwala da alamar masallaci zashi ma'aruf cikin hanzarin ya ƙara so garesa, Abba ya zuba masa ido yana murmushi lokacin da yake ƙoƙarin karasowa garesa , rage tsawonsa yayi gurin gaisheshi Abba ya amsa tare da cewa " shiga kayi alwala kazo mu wuce masallaci tare " da hanzarin ya shiga a harabar gidan ya tsaya daga can bangaren dama ya isa ya kunna fonfo yayi alwala ya fito suka wuce masallaci tare .

Bayan sun idar da Sallah tare suka jero suna hira Ahankali Ahankali tamkar wasu aminai har suka karaso gida,kai tsaye suka wuce zuwa bangaren Abba in da ma'aruf ya samu guri ya zauna akan kujerar mutun ɗaya ,Abba na matsanancin son ma'aruf a duk cikin ya'yan yan'uwansa babu wanda yake so kamar sa , tun da aka haifeshi ya dasawa zuciyarsa kaunarsa har ila yau , bai taɓa haɗa shi da komai ba, ko ƴaƴan cikinsa baya jinsu kamar yadda yake jin ma'aruf a cikin zuciyarsa , shima haka ne a ɓangaren ma'aruf din baya wasa da al'amarin mama da Abba yana son su fiyye da komai na rayuwarsa baya wasa da al'amarin su, document Abba ya mika masa "gashi ka sanya hannun, ka cike duk inda Yakamata, idan kaga rayhan ka min shi yazo ya cike nasa " ma'aruf ya amsa da "tam Abba, Ahankali ya fara ƙoƙarin cike komai da'ake bukata ya ajiye a saman madaidaicin center table din dake parlour'n , "har ka gama Abba ya amsa yana dubawa tare da tsurawa rubutunsa ido "eh ya bashi amsa yana shafa sumar kansa ,sosai Abba yake kallon rubutun nasa sam bakace hannu ne ya rabauta shi ba saboda daidaituwar rubutun, bayan ya gama kallon rubutun yace "kana iya tafiya "Ma'aruf ya yuya a natse yana yiwa Abba sallama ya fita daga part din zuwa bangaresa .

*******
Yau ta kama lahadi ma'aruf ne ya fito cikin kananan kaya wandon jeans baki da riga fly amirates baki da ratsin yellow ajiki, kansa sanye da facing cap kafafunsa wasu haddadun takalmin canvers ne mai ɗauke tambarin Gucci ,Yayinda kunnensa ke manne da eipice hannunsa rike da wayarsa iphone x sai kamshin turaren viso dake tashi ajikinsa yayi kyau sosai tamkar ka suresa ka gudu, Ahankali yake taku kamar wani mace ,a daidai harabar gidan suka haɗu da himaya kawar Ummita kallo daya yayi mata ya ɗauke idanunsa akanta ya cigaba da tafiya,

Da wani irin mayataccen kallo tabi shi kafin daga baya bakinta na rawa tace "yaya ma'aruf ina yini ?banza yayi mata a daidai lokacin daya k'arasa jikin motarsa ya buɗe shige ya bar gidan ..

jijinta a matukar sanyaya ta nufi bangaren su ummita tana mita aranta ,Ummita na ganinta ta saki fuska tana murnar ganinta ta taso ta runguneta "kai himaya kamar kinsa ina son ganin ki wallahi dazu na gama cewa zanje gidanku .

"ayya ai shikenan na hutar dake tunda gashi nazo ,ke wai meke damun yayanki
Yanzu muka haɗu dashi ?
" wanne kenan a cikinsu "wannan mai mugun girman kai da d'acin rai har yaushe zai daina wannan d'acin ran nasa?
" na gaida shi ko amsa min bai yi ba bare ya kalli inda nake sai ma fizgar motarsa da yayi ya fice" shiru Ummita ta ɗan yi tana yatsina fuska sannan tace "wannan ai kullum haka yake bashi da wani aiki sai fushi da girman tsiya idan Kinga hakoransa waje to Yana tare da wancan tsohuwar kilakin budurwar tasa ne "ke ma meye abun damuwa dan bai amsa ki ba ,nan gaba ko kingansa karki sake kallonsa bare ki gaisheshi, idan kuma kinsa zaki dinga gaida shi ne idan kinzo karki sake zuwa gurina ta karasa faɗar hk tana hararar himaya ,dariya himaya ta saki da karfi "ikon Allah ke kuwa me yayi zafi shi ba wuta ba naga yayanki ne?


"a'a ni yayyena guda biyar ne kacal ,yaya Usman ,yaya rayhan ,yaya sadam ,yaya Abdurrahaman sai yaya Malik Amman Banda wannan ɗan girman tsiya ,dan haka daga yau idan dole ne gaisuwar taki waɗan nan dana lissafa miki su zaki gaisar ,idan ba haka ba mu raba hanya tuni wuri, dan bana son shishigi da neman suna ta juya tana ƙoƙarin zama akan kujerar mutun daya.

himaya ta biyo bayanta tana mamakin mulkin da mallaka irina Ummita, ita lallai sai abinda take so za'a ,yayinda ita mutun bai isa ya sata yin abu dole ba, guri ta samu kusa da kujerar da take zaune ta zauna "shikenan Ummita bazan sake gaishe shi dashi ba daman saboda ke nake gaisheshi amman tunda baki so shikenan , anyi na farko anyi na karshe ,"better Ummi ta fad'a tana tamke fuska .

"amman ke ummita mai yasa kike nuna masa kiyaye irin haka alhalin dan'uwa ki ne na jini "babu ruwanki da wannan tsakaninmu kuma ba dole sai kin sani ba ,ke dai kawai kiyi abinda nace "
"Anki Allah sai kin gaya min ,nice fa "ko kece fa sai akayi yaya ?
ta karasa mgnr daga fuskarta sama....
Murmushi himaya tayi "ki fada min tunda nice ta hannun damanki Ahankali ta kamo hannunta cikinta "Ummita zanyi wata magana amman karki ji haushi na Please "uhnmmm ina jinki tayi saurin katseta still fuskarta a haɗe "sai naga kamar kina son ma'a....."dakata dan Malama karki kawo min wannan banzar maganar nan ,wallahi idan aka jera min dubun su yaya ma'aruf babu abinda zanyi dasu .
"duk kyawun nan nashi Ummita ?
"Kwarai kuwa babu abinda zanyi dashi saboda ba kyau akewa ba hali a akewa ,wallahi idan nace miki ma'aruf yayi min karya ne" ke bancin gidan nan gidan mahaifina ne wallahi da zan iya barin gidan nan naje gaba nayi rayuwata saboda bana qaunarsa ,ke nifa sam bana jinsa tamkar dan'uwa ....
"Bani ba ko wata yace yana so wallahi matukar ina da yadda zanyi to zan faɗa mata gaskiya "haka suka ci gaba da hirarsu wanda duk sama sama ummita take amsa mata har daf magariba suna tare sannan himaya ta wuce ....



Two friend's bsbs

💗💗💗💗💗💗
WANNAN CE
QADDARARMU
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

~TRUE LIFE STORY~

FREE NOVEL NOT FOR SELL


AL'QALUMAN



*AYSHA A BAGUDO*
*FAIZA HAMMADU*


~DEDICATED TO~
MARYAM ALHASAN D'AN IYA
(MARYAM OBAM)

BEST FRIEND FOREVER AND EVER, AKWAI AMANA 'KAWARMU ALLAH YA BARMU TAREN TARE SON SO FI SABILILLAH 🥰🥰

WATTPAD @HAUESH

bismillahirrahmanirrahim


PAGE 3

.....barin ma'aruf gida ,bai zarce ko'ina ba sai unguwarsu suhaima sakamakon kiran da tayi masa akan mahaifinta na son ganinsa .

tun kafin ya qarasa, ya ciro phone d'insa
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On WANNAN CE QADDARARMU
avatar
amina-4

11 months ago

Reply

Interesting novel

avatar
amina-4

11 months ago

Reply

Interesting novel

Please Login or Register in order to submit comment