Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ya fara dialing din number suhaima domin sanar daita zuwansa , ba'a ɗauki wani lokaci ba, ta ɗauka cike da shagwa'ba da kashe murya "hello my habibi ,my baby ,my love, my everything .


Ma'aruf yayi tsadadden murmushinsa wanda ke sake bayyana kyawunsa yana saka phone din a speaker sannan ya cigaba da driving "Allah ya qarawa gimbiyata lafiya duk ni kaɗai godiya nake , murmushi tayi tamkar tana gabanshi wanda har sautin muryarta ya bayyana "matsayinka ya zarta haka a gurina "zaka zo ɗin ne ko ka fasa zuwa? tayi maganar muryarta can kasa tamkar wacce ke koyan magana dan bata san abinda zai ce mata ba , dan tasan halinsa baqaramin aikinsa bane yace mata ba zai zo ba ....

"Ran gimbiya suhaima ya dade gani nan hanyar qarasowa ,me kika tanadar min ?maganarsa ta kashe mata sansar jiki har tsigar jikinta suka mike ta lumshe idanunta , sake fad'ad'a fuskarta tayi da fara'a tace "mai habibi nah yake bukata daga gareni ?
"Kar ya damu ya fad'i duk abinda yake so ,a shirye suhaima take data mallaka masa ...


Kad'a kai yayi yana murmushin jin dadi haɗe da shafa sitiyarin motar sannan yace "Karki damu ba na bukata komai sama da ganin kyawawar fuskarki.....
koda yake yau zuwan ba naki bane na dady ne fatan zan same shi ?

murmushin farinciki ta saki tana kamkame wayar a kunnenta " yana nan yana zaman jiranka babu in da yaje ,yace yau sai yayi 4 eye's da wanda yayi nasarar sace rayuwar suhaimar sa .


Murmushin gefen baki yayi sannan yace "Okay ai ta kwana gidan sauki yau zai ganni , ba ganinna ba har kunne da kunne zamu yi dashi ,
sai na qaraso ya fad'i hk yana katse Kiran tare da shafa sajensa,wani irin juyin farinciki suhaima tayi har da tsalle , take ta shiga rawar jikin tarban masoyinta ..

Lokacin ɗaya isa suhaima ta gama shirya masa komai na tarbanshi cikin girmama wani irin mayataccen kallo ma'aruf ke binta da shi saboda kyawun da tayi masa , ya taso daga inda yake zaune ya zauna kusa daita har cibiyoyin su na zozan juna take suka ji wani irin zirrrrrrrr a gaba-daya ilahirin jikinsu ,hannunta daya ya kamo cikin nashi yana murza Ahankali tare da sanya kwayar idanunshi cikin nata "kinyi kyau sosai my suhaima kamar na cinyeki ,kullun na kalleki qara kyau kike min meye sirrin ne ?
"Kai habibi ai duk kyawuna ban kai ka ba ..
"Shiiiiiiiiiii ya d'aura hannunsa kan lip's dinta "Karki fadi son ranki Mana ,nifa tsintar dame nayi ,bancin soyayya babu ta yadda za'a yi na ....
"Zaka fara kou ?
"Ai gaskiya ne ....
Matso da fuskarta tayi daf da nashi suna shaƙar numfashin juna kusan minti goma ma'aruf bai ɗauke kwayar idanunsa cikin nata ba har sanda ta lumshe idanunta
,murmushi yayi yana cizan lip's dinta na kasa ,ya san yadda soyayyarsa tayi tasiri a zuciyarta, ba zata iya jurar kallon kwayar idanunsa na tsawon lokaci ba muryarta a matukar sanyaye "am missing you habibi do you also miss me ? Tayi maganar muryarta a raunane tamkar zata shige jikinsa ,tuni jikin ma'aruf yayi mutu yanayinsa ya soma canzawa
Yayi baya ya jingina jikinsa da kujerar da yake zaune yana sakin numfashi "abinda kika rigada kika sani ne suhaima kullun cikin missing ɗinkin nake "ta kwanto ta shige jikinsa ta rungume shi tsam ajikinta tana fidda numfashi "nasani habibi ,nasan kana sona sosai ,sai dai nawa yafi naka tayi maganar tana sake shige masa tamkar wanda za'a kwacewa ,jin tudun dukiyar fulaninta yasa komai ya soma kwace masa numfashi ma da kyar yake fitarwa , Ahankali ya sanyawa jikinsa dakiya ,dan baya so ya dara daga rike tsintsiyar hannunta, saboda ita din matar da yake buƙatar killace wa ce a gidansa ba wai shashanci ba ,ya kuma san halin rigimarta bata iya jurewa kusancinsu , sau tari shine ke control if not da tunin an wuce gurin , mikewa yayi tare daita ya tsaida ita bisa kafafunta "ya kamata kiyi min iso gurin dady kou?
Hannunsa ta riko cikin nata tana murzawa "kaci wani abu mana kafin nan tayi Maganar tana sake shigewa jikinsa " bana buƙatar cin komai suhaima asalima bana tare da kishi ko yunwa ,"na sani ai kullun haka ne , bansa lokacin da zaka fara cin abun hanuna ba "share wannan maganar muyi abinda ya kawo ni kema kin san ba wani cin komai zanyi ba .
"muje ta faɗa cikin killer voice dinta ..
Tafiya ɗaya biyu ya zare hannunsa dake cikin nata batare daya ce mata komai ba hakan nan yake jin tsoronta yau .


Kai tsaye parlour'n mahaifinta Alhaji Muhammadu canji ta nufa dashi ,tare suka jero tana karairaya tamkar zata balle ,a adaidai bakin kofar parlour'n ya ja ya tsaya al'amun tayi masa iso, ta shiga ko cikakken minti goma bata yi ba ta fito "bismillah habibi ta faɗa ahankali cike da sanyi jiki saboda ganin irin kallon da yake mata ,
Ahankali ya sanya kanshi cikin had'ad'd'en parlour'n da ya qawatu da kayan more rayuwar duniya , babu abinda babu acikinsa,sannan babu parlour'n yake sai kamshin turaren dana room freshener dake gauraye da sanyi ac ,ya qarasa har gaban mahaifinta tare da rusunawa kansa a ɗan sunkuye a kasa "Abba Barka da warhaka ?


Tsura masa ido mahaifin suhaima yayi na wani lokaci yana kallonsa , sannan ya amsa yana mika masa hannu, amman ma'aruf yaki mika masa hannu illa cigaba da rusunawa da yayi , abinda ya ƙara burge mahaifin suhaima kenan ,wannan shine karo na farko daya sanya yaron a idanunshi, amman lokaci ɗaya yaji ya tafi da hankalinsa, akwai natsuwa da hankali a tattare da yaron, uwa uba tarbiyya, duk inda ya fito ya samu wadatacciyar tarbiya ,irin wanda yake buƙatar a tattare da ya'yansa , gaba-daya sai bai ga aibun da mutane suke kawo masa akan yaron ba ko da yake ai ba'a sanin halin mutun a fuskarsa ..

Bayan sun gaisa , mahaifin suhaima yayi wa ma'aruf umarnin da ya tashi ya koma kan kujera ,yana ƙoƙarin mikewa suhaima ta qaraso cike da shagwa'ba ta riko hannunsa zuwa kan kujera dake fuskantar mahaifinta , jimmmm kaɗan mahaifinta ya kalleshi "daman ni nace suhaima ta turo min kai saboda tun fara zuwanka gurinta na kasa sukuni da samun natsuwa ,inata zullumi da fargaba akan batunka da ita, sakamakon zantuttukan mutane daban daban da nake samu akanka waɗan da suke ganin kamar ba aurenta zaka yi ba ,yaudara ce kawai dan haka ina son sanin abinda ke kawoka gurin suhaima, neman auren suhaima ko akasin haka?


Ma'aruf ya ɗan yi murmushi "karka ji komai dady da gaske ina son suhaima Kuma so irin na aure , sannan bani da tunanin komai akanta sai alkhairi ,ina son suhaima Kuma ina son ta zamo uwar ya'yana , ni kaina ina son manya su shigo cikin maganar ,sai dai zuwa yanzu ina neman alfarma zuwa lokacin da zan soma aiki, inshallahu zan turo manyana.


Dady yayi shiru kafin daga baya yace "alhamdullahi naji dadi sosai da wannan albashir ,baka da matsala Allah ya nuna mana lokaci, sai abu na gaba waye mahaifinka ?"
Mahaifina Alhaji shu'abu ya rasu shekaru goma da suka wuce ina tare da kanin mahaifina ne Alhaji abdulhamid mai oil & gas , "Masha Allah ba dai hamid mai oil &gas ba?
" shine kanin mahaifina
Ma'aruf ya fad'i yana shafa sumar kansa ,mahaifin
suhaim ya jina kai" lallai da alamun suhaima zata fi sauran yan'uwanta mata samun ingantaccen gidan aure" a qalla sun kusan awa ɗaya suna tautaunawa kafin suyi sallama ya wuce ....
Tun daga wannan lokacin idan ma'aruf yazo gurin suhaima , kai tsaye ake barinsa shiga da motarsa cikin gidansu sabanin da dayake parking a waje ..

*****
Da misalin ƙarfe tara na dare ma'aruf ya sanyo hancin motarsa cikin unguwarsu bayan ya dawo daga yawonsa, a daidai kofar gidansu ya tsaya batare daya kashe motar ba, yayi hon
jikinsa tattare da gajiya.

Mai gadi ya k'arasa cikin sauri ya buɗe masa tafkeken get din gidan ya sanya hancin motarsa ya shigo harabar gidan yayi parking sannan ya shiga gida.

kai tsaye ɓangaren mama ya nufa ,ya isketa zaune a parlour hannunta rike da plet tana cin farfesun naman kai , suna zaune tare da ummita suna hira ya k'arasa shigowa tare da sallama .

mama ce kawai ta d'ago ta kalleshi haɗe da amsa masa sallamar da yayi, amman Ummi ko kallon inda yake batayi ba bare tasan da zaman mutun agurin sai ma maida hankalinta da tayi zuwa ga tv ..

Guri ya samu ya zauna yana kiran "washhhhh Allah na gaji mamana...... "
Mama tayi murmushi tana yi masa sannu "ga ruwa ka ɗan sha ta kai hannu ta dauko robar ruwan faro dake ajiye a gefenta ta mika masa ya amsa "yauwa Mamana kamar kinsa ina tattare da kishi "ai jiya ba yau ba ma'aruf kai ma kasan nasani ,ta k'arasa maganar tana sake fad'ad'a fuskarta ..

Kusan minti biyar ya ɗauka zaune yana Kallon mama sannan yace
"Mama .....
Ta waigo Ahankali ta zuba masa idanunta "ya'akayi ma'aruf ko kana son wani abu ne ?
" a zuba min abinci tun karin safe ban sake cin komai ba ......
shiru Ummita tayi batare da ta kalleshi ba ta soma wasa da yatsun hannunta ranta a matuƙar 'bace ganin yadda ya wani narke fuska , tsaki taja a kasan zuciyarta "aikin banza kawai mutun taje ga uwarsa masa mana yayi mata shagwa'ba tana cikin zance zuci taji sautin muryar mama
"ummita tashi ki zubawa yayanki abinci, sosai taji zuciyarta ta buga ,kamar ba zata tashi ba saboda sanin halinsa dan zai iya cewa baya ci tare da disgata ,ko bama haka ba ita kanta mama yanzu zata iya mata fada a gabanshi abinda tafi tsana kenan , duk da haka sai data dan jira kaɗan taji mai zai ce ko ita mama ,sannan ta tashi taje ta zubo masa tana yatsine yatsine fuskar shi kuwa ma'aruf ko kallon inda take bai yi ba , lokacin da take miko masa abincin ne mama tace "ina kaje ne yau, sakina tazo ne manka ?

Tsigil ummita ta ca'bi bakin mama
" wacce sakina ta gidan iyanmu ko ta nan ?
"ta gidan baba sarki sai da tayi tambayar sannan ta fahimci kuskuren da tayi ,five seconds ya d'auka zaune yana Kallonta da tsantsar mamaki a fuskarsa, tsareta yayi sosai da sexy eye's dinsa ya kasa kawar da idanunsa akanta , duk ƙoƙarin d'agowar daya ga tana yi izuwa kallon fuskarsa hakan bai sa ya dauke idanunshi akanta ba karaf idanunsu ya tsarke cikin juna ....

Wata uwar harara ya banka mata lokacin da ya ga tana ƙoƙarin sake yin magana "kika sake naji kin sake cewa wani abu anan sai Kinga abinda zan miki "to to ni ance maka maganarka zanyi ? Yana gama faɗar haka ya mike ya fice daga dakin zuwa nashi batare da yaci abinci ba.

"kin gani kou ,kinsa ransa ya ɓaci ke kinsa ba shan inuwa ɗaya dashi kike yi ba meye na saka bakinki cikin maganarsa ?
"To ai ni ganin nayi me zai yiwa aunty sakinar gidan sarki data zo nemansa , ni wallahi takaici yammata dake biyosa nake dan ni banga abun bi agurin yaya ma'aruf ba, Allah kuwa mama ke ma har da dariya kina wani nuna kinji dadi , wallahi faɗa ya kamata ki dinga wa masu biyosa wannan ba mutuncinsu bane .
" Karki ji yadda nake ji idan sun zo "kun ji min ikon Allah , Allah ya bawa d'ana farinjini kice na dinga kore masa yammata, a'a ba'a yi haka dani ba ,maza tashi ki bishi da abincinsa sauran kiyi nasa rashin kunya ..tana jin mama ta share dan bata jin zata sake shiga d'akinsa har ƙarshen rayuwarta ...




Shiru yayi a d'akinsa, shi kaɗai bayan ya tattara hankalinsa da tunaninsa guri daya kafin daga baya ya janyo wayarsa ya shiga duba sakonnin da aka a turo masa ta what's app da facebook Instagram wanda mafi yawon sakon yammata ne masu barar soyayyar sa ,Ahankali ya shiga karantawa daki daki, yana cikin karantawa ne rayhan ya shigo dakin yana dafa kafadarsa , d'ago kai ma'aruf yayi Ahankali yana dubansa tare da cire hannunsa ya ajiye wayar yana ƙoƙarin mikewa rayhan yayi saurin riko tafin hannunsa "haba ma'aruf kar dai fushi ka ɗauka dani nifa wallahi da wasa nake maka abinda ya faru ?
"To ni da gaske na dauka dan kuwa tuni na rufe babinka a rayuwata, tunda ka nuna kafi son fat lion akaina ....ya k'arasa fad'ar haka yana ƙoƙarin zare hannunsa cikin nasa ,"kowa ya tsaya matsayinsa bazan hanaka shigar mata fada ba Sannan bazan hanaka mu'amala da ita ba, halaka dai na yanke da kai har abada ..

"Karka ce haka ma'aruf , ko ba zaka duba halaka ta jini da yan'uwankata ba , ka duba darajar iyayen Ummita gareka ,ka duba matsayin da suka baka Arayuwarka akwai qauna mai girma atsakaninka dasu " And so ?

"Shi kad'ai ya isa ka daina zurfafa qiyayyarka ga tilon diyar da Allah ya mallaka musu ,sannan ita kanta ummita guda nawa take bare ka ..... "dakata rayhan me ma ya kawoka gareni "me ye damuwarka dani ?
"Ko kazo ne ka bata min rai da wannan surutun naka ?

"Babu komai kawai dai ina jin babu dadi araina ne akan lamarinka da ummita ,bana jin dadin abinda kake mata ummita yarinya ce har yanzu da kuruciya tattare daita "a'a ko haihuwarta ma ba'a yi ba tukuna ,ita baga ganin irin tsanar data min sai nawa kake gani har kake ganin laifina akanta saboda ni ba zuciya bace akirjina ....
Har rayhan ya buɗe baki da niyyar sake yin magana ma'aruf yace "bana son sake Jin komai daga gareka kaje kawai kayi rayuwarka ,nayi tawa ba dole sai kayi mu'amala da ni ba ,"bai kamata ka damu kanka akan dole sai na daina kinta ko akasin haka ba, tunda wannan ba wani sabon abu ne ka rigada ka saba ga...sai kuma yayi shiru yana jan tsaki..
Iskar bakinsa ya furzar ya dafe gaban goshinsa Ahankali ya soma jan kafafunsa ya k'arasa gurin kujerar mai zaman mutun daya dake ajiye a dakin ya daura kanshi ..


Matsowa kusa dashi rayhan yayi , "shikenan ma'aruf kayi hakuri bazan sake shiga maganar ku da ummita ba amman dan Allah ka daina mata dan "Please ya faɗatare da daga masa hannu al'amun ya kyaleshi ..


Barinsa rayhan yayi ba dan yaso ba sai dan sanin halinsa da yayi idan yace Yes ,Yes ne idan yace no,no ne,idan kuwa ya kafe akan abu to zai yi wuya a sashi dole ..

"Allah dai ya baka hakuri kuma ya huci zuciyarka ,yasa ka gane kuskure ne abinda kake yi ,bazan gushe ba gurin maka addu'a ,saboda bayan halaka ta jini akwai sirrin qauna atsakaninmu ,har kullun ina sonka ma'aruf "jeka kawai dan Allah, ka ma daina sona daga yau , dan ni tuni nayi deleting dinka arayuwata.

"sabod ina kula ummita kou ?
Wani duba ma'aruf yayi masa sannan ya ja dogon tsaki "I don't know what to say but I feel like that ya fad'a Yana runtse idanunshi .

"Haka ne ma ,ba wai kana jin kamar haka bane " dan darajar Allah rayhan karka sake min maganar fat lion anan ..
I don't like it dan a duniya idan akwai halittar dana tsana itace ,kai tun da aka haife yarinyar nan na daura idona akanta naji na tsaneta, kawai wani lokacin darajar mama ne ,kuma bana tunanin zan sota har karshen rayuwata .....

Dariya sosai rayhan yayi "oh ma'aruf sai dai abarka da halinka ,"tam naji abarni dashi ,dan Allah ka wuce karka samin ciwon kai "ko baka faɗa ba tafiya zanyi gurin my quen amnan ka d'aure dai ka sota koda cikin cokali ne... ya faɗa yana juyawa ya fice daga dakin yana murmushi tare da cewa "Allah ya ganar da kai illar abinda kake yi ...


ummita dake tsaye a parlourn ma'aruf hannunta rike da kular abincinsa tana sauraron abinda suke tautaunawa,jin motsin fitowar yaya rayhan daga dakin yasa ta koma da baya ta la'be abayan kofa tana jan tsaki " to dama wa yake kaunarka, koni har karshen rayuwata bazan taɓa sonka ba

Two friend's (bsbs)

💗💗💗💗💗💗
WANNAN CE
QADDARARMU
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

~TRUE LIFE STORY~

FREE NOVEL NOT FOR SELL


AL'QALUMAN



*AYSHA A BAGUDO*
*FAIZA HAMMADU*


~DEDICATED TO~
MARYAM ALHASAN D'AN IYA
(MARYAM OBAM)

BEST FRIEND FOREVER AND EVER, AKWAI AMANA 'KAWARMU ALLAH YA BARMU TAREN TARE SON SO FI SABILILLAH 🥰🥰

WATTPAD @HAUESH

bismillahirrahmanirrahim

PAGE 4


..... Ahankali hawaye ke zubowa daga idanunta a lokacin , ta ajiye kular dake rike a hannunta haɗe da durkushewa agurin tana son sanin abinda yasa yaya ma'aruf ke mata irin wannan qiyayyar .
"me yasa baya sonta ?
"Me yasa baya son kusancinta dashi ?


"Tun farko shine ya soma nuna zallar qiyayyarsa gareta , tun tana d'aukar hakan a matsayin rashin haɗuwar jini har ta girma ta fuskanci tsabar qiyayya ce kawai ke d'awainiyya dashi wanda ko a gaban mahaifiyarta baya iya 'boye haka .

Kuka take sosai tana girgiza kai, domin zuwa lokacin babu abinda ke d'awainiyya da zuciyarta kamar qiyayyarsa, baka jin motsin komai a parlour'n sai sautin kukanta ..
Wani irin yunkurawa ma'aruf yayi a matukar fusace ya soma ƙoƙarin fitowa daga bedroom d'insa sakamakon sautin gunjin kuka da yake ji ya shiga cikin kunnuwansa ..

Tana cikin tunani da sheshekar kuka taji alamun motsin fitowarsa daga bedroom d'insa , jikinta na rawa ta soma ƙoƙarin goge hawayen dake kwance akan kuncinta, bata gama gogewa ba , taji tsayuwarsa a gabanta yana mata wani irin kallo mai tattare da tsana da jajayen idanunsa da suka canza kala yana fidda wani irin numfashi tamkar zaki ..

a matukar firgice ta mike tsaye jikinta na wani irin rawa yayinda take qirjinta ya shiga dokawa da sauri tamkar zai fito ..
Ya tsura mata ido yana kallonta cike da zallar tsanarta , ta bala'in bashi haushi sakamakon tunanin da zuciyarsa ta yi akanta ,ya ƙara taku zuwa inda take tsaye tana kyarma ..

Da sauri ta qara yin baya yana biyota har sai data kurewa bango, taja ta makale gabanta na faduwar ,shima ya ja ya tsaya yana fuskantarta ,
tayi saurin yin kasa da fuskarta qirjinta na dokawa "wayyo Allah na shiga uku ,me yasa na tsaya har ya fito ya same ni ?
Cike da tsanarta ya sa hannunsa ɗaya ya dafa bango yayi mata katanga tare da sunkuyo da kanshi daidai fuskarta ,yayinda fuskarshi ke murtuk tamkar hadari Muryarsa a kausashe yace "ke uban me kike wa mutane anan ?

Ta bude baki zata yi magana ya katseta da sauri ta hanyar cewa
" Shiiiiiiiiiii yi min shiru yar iska manafukar Allah daman 'labe kike wa mutane kou... ?

Maganar sa ta doki qirjinta da kunuwanta alokaci ɗaya har yayi nasarar shiga zuciyarta ya samu kyawawan mazauni a tsokar dake makale da qirjinta ,take taji hankalinta yayi bala'in tashi ,gaba-daya ta rasa me ya kamata tayi , ta d'ago kanta ahankali ta mai da idanunta kan kular data shigo dashi ko zai fahimci abinda ya kawo ta d'akinsa domin ya cire zarginsa gareta ,a kallon da take wa kular abinci ne wasu sabbin
hawaye sharrrrrrrr ....
sharrrrrrrr .. suka sake gangaro mata .
ta kasa tsaida kukanta tana dubansa zuciyarta na sake tsanarsa "okay da alamu kinji duk abinda muka tautauna da rayhan kenan , shiyasa kike hasarar hawayenki ba ?

"ai ba karyar na faɗa masa ba ,abinda ke cikin zuciyata kenan , babu abinda ke cikin raina kamar zallar tsanarki, dashi na girma fat lion banga Kuma mahalukin da ya isa ya kankare wannan tsanar ba , bana sonki !bana sonki !! Ke mai sonki ma bana qaunarsa kamar yadda kema nake hango tawa tsanar acikin kwayar idanunki.

"Tayi saurin runtse kyawawan idanunta saboda d'acin kalmar gareta .....
"Okay kina kuka ne saboda bana sonki ko me ? Yayi mata tambayar yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa ..

Tsareshi tayi da idanuwanta masu matukar kyau da haske , batare da tace masa qala ba, shima tsareta yayi da idanunshi yana mata kallon kaskanci da wulakanci ,a qalla sun ɗauki tsawon minti biyar suna kallon cikin kwayar idanun juna batare da kowannensu yayi d'an'uwansa magana ba ..

" Da ido yayi mata alamar ta fita a d'akin ,
" ba mutsu ta raba ta gefensa zata wuce sai dai muryarta a raunane tace "zan wuce ..
"ki wuce mana na rike ki ne da zaki wani tsare mutane da wannan banzar idanunki naki dake firgita mutane ?
"Gaba-daya ke abar tsoro ce ga al'umma ,kuma abar gudu kwata kwata baki ...
"Dan Allah malam enough ,"enough is enough yaya ....."ya isa ba dogon turanci na nema daga gare ka ba matsawa kawai zaka yi na wuce, dan bana son jikina da naka su haɗu, tayi maganar a dake , sai dai zuciyarta cike take fal da matsanancin tsoro da fargaban abinda zai mata .


"Ware idanuwanshi yayi sosai cike da mamakinta yayinda ya dinga jin wani sabon tsanarta na huda zuciyarsa tare da samun kyawawan mazauni daban a sansar jikinsa .... .

" Ta hura hancinta sanan ta sanya bayan hannunta ta goge fuskarta "ka daina mamaki abinda na faɗa ... dana bari shashin jikina ya haɗu da jikinka gara na haɗa jikina da bakin jaki......
"Abu na
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On WANNAN CE QADDARARMU
avatar
amina-4

11 months ago

Reply

Interesting novel

avatar
amina-4

11 months ago

Reply

Interesting novel

Please Login or Register in order to submit comment