Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

cikin salon qiyayya ce , amman kinsa wani abu ?

Meenal tayi saurin girgiza mata kai a tsorace ",ina da type din namijin da nake so a rayuwata ...
"ina son namiji kamili mai nuna ko in kula ga lamuran mutane, mai Jan aji da kuma miskilance ....
ta ware kyawawan idanunta sosai sannan ta cigaba "Kinga duk cikin masu zuwa gurina babu mai wannan siffofin dana lissafa miki.

"to amman ai ya rayhan yana sonki kuma shima babu laifi yana da nashi daidai gwargwado "manta da wannan ni nafi son wanda zan so da dukkanin zuciyata ba wanda yake sona ba ......
Meenal tayi sororo tana kallonta ,inda mata ke da muradin auran masu son su da tattalinsu, ke kuma ra'ayinki daban,koda yake dama haka kike duk abinda ake so da yayi ke baki cikinsa sai wanda aka gama yayi, ko wanda ba'a so ....
"Kullun cikin mamakin wannan halin naki nake ...

Murmushi ummita tayi "meenal kenan ki daina mamaki saboda kin rigada kin san halina ba tun yanzu ba , kin san Allah sai na yiwa ya ma'aruf magana ko da itace zata zamo maganarmu ta karshe dashi arayuwata ..


Tana gama faɗar haka ta cire hannuta a kafadar meenal ta juya ta cigaba da takawa ahankalin, meenal ta biyo bayanta da sauri ",haba ummita dan me zakiyi masa magana bayan kin san halinsa ?


A fusace tace "Ke me yasa kika faɗa bayan kinsan halina ba tun yau ba ?
"Kinsan ba'a gulma dani , ba'a cin naman wani dani ,sannan duk wanda akace ya fadi abu akaina sai na same shi nayi masa magana ,idan kin manta halina gashi na tuna miki sai ki ɗauki hakurin hukuncinsa gareki dan babu makawa sai na taresa ......
"inna lillahi "ki yiwa Allah ki rufa min asiri wallahi ko aunty jidda taji sai tayi mugun sa'bani "oho ni dai babu ruwana gobe ma duk abinda akayi kizo ki faɗa min ina maraba da hakan ta haɗe hannuwanta guri ɗaya alamun godiya.....

doguwar hanyar da zata shigar daita har cikin gidansu anan suka ci karo dashi ya fito da sauri da alamun fita zai yi, ta gefenta ya wuce yana kawar da jikinsa dan ma kar ya ra'bu da ita, tana murmushi ta jiyo tana kallonsa har zai karya kwana zuwa harabar gidan tace " fat lion da iyakacin karfinta.......

Cak ya ja ya tsaya kamar an dasa shi kafin daga baya ya juyo ahankali yana fuskantarta da idanunsa masu matukar bugar da zuciyar duk wacce ta kalli cikinsu,
so yake ta maimaita abinda tace dashi take ko da kanta ,hannuta ta daga masa ",yes da kai nake zaka qaraso ne , ko ni nazo da kaina ?

Qirjinsa ya nuna da yatsan hannunsa alamun shi , lumshe masa kyawawan idanunta tayi sannan "tace Yes of course da kai nake fat lion bari na qaraso tunda kai ka kasa ..
tasoma takowa Ahankali kamar batason taka kasa yayinda qirjinta ke lugude , a daidai lokacin meenal ta qaraso tana ganin abinda ke faruwa ta juya da sauri dafe da kirjinta "shikenan na shiga uku yau a gurin ya ma'aruf..

Har ta qaraso idanunshi na kanta ta tsaya can nesa kaɗan dashi wanda bai fi taku biyu a tsakaninsu ba ,ta kyata masa yatsun hannunta biyu a daidai kunnenshi domin ta dawo dashi hankalinsa da yayi nisa gurin tunani "ya ma'aruf ko me kake da suna oho...
Koda yake ba dan haka yasa na tsaida kai ba ..
Na tsaida kai ne saboda ina son sanin me ye damuwarka da subai'a ,"me subai'a ta maka ?
"Me subai'a ta tsare maka arsyuwarka ?
"Shin ko akanka nake da zaka damun kanka da lallai sai na kula samari ?

"nice nan bana ra'ayin kula su,kuma babu wanda ya isa ya sani kula samarin da ba type dina ba ,ina nan a cikin gidan tunda ba gidanku bane gidan ubana ne har sai na samu wanda yayi daidai dani ,da irin abinda nake so ga namiji,dan ba kowani kwashe kwashe zan kwasawa kaina ba ,ko a Shari'ance ance dole sai nayi zance da samari sannan zanyi aure arayuwata ?
Shi Shari'a Muslunci is different with morality wannan ya zamo karo na karshe daga yau karka sake damuwa da zuwan masu sona tun. .....
Ji kake Tasssss Tasssss Tasssss marin ya ma'aruf sai da ummita taji wani jiri ya dibeta har zai yaddata Allah ya jiho ya rayhan yayi saurin rikota cikin zafin nama saboda ganin tana shirin faduwa "yar iskar banza da wofi har ni zaki kalla ki dinga fadawa son ranki , sa'anki ne ni dan ubanki ?
"A she daman baki da hankali ?
Allah sarki ya rayhan ji yayi kamar shi aka mara har cikin zuciyarsa yaji zafin marin da ma'aruf yayi mata ..


Ita kuwa kwanciya tayi lamo a qirjin rayhan yadda ya tarota tana zubar da hawaye har ta soma jika masa gaban rigarsa "yar iska ni an ce miki rayhan ne ko waɗan can yan iskan masu zuwa suna nacin sonki ?
"Sannan idan kin ga dama ki kula masu zuwa gurinki ,idan kin ga dama karki kula su wannan ruwanki rayuwarki ce ,kece zakiyi kwantai kowa yayi aure ya barki ki zama jaka mai aikace aikace gidan ,stupid Kawai as age dinki ,bari na faɗa miki abinda baki sani ba kina qara shekara biyu nan gaba kin zama tsohuwa duk wanda ya kwasheki wallahi tsohuwa ya aura ....

Yayi taku ɗaya zuwa biyu ya zagayo ta inda fuskarta take "listing to me idiot idan kika sake kirana da fat lion I will deal with you stupid Kawai more than donkey's ...
Duk maganganu ma'aruf rayhan ji yake kamar ya rama mata, tunowa ma'aruf ne yasa yayi wani dogon numfashi dan zai iya maida maganarsa babbar magana tare da gaba , shi kuwa ma'aruf ido ya tsura musu ganin yadda yanayin rayhan ya canza alokaci daya ....

Cike da matsanancin tashin hankali ma'aruf ya juya ya isa in da motarsa take parke ya buɗe ya shiga, shi kuma rayhan yayi cikin gida daita tana rabe a gefen jikinsa yana bata hakuri , har suka shiga part dinsu , mama dake zaune ta lumshe idanunta saboda tasan duk yadda aka yi ita da ma'aruf ....ya zaunar daita yana bata hakuri yana tambayarta abinda ya hadasu taki ce masa komai sai kuka take har da shesheka kukan da mama take jinsa har cikin ƙwaƙwalwarta ,a duniya idan akwai abinda ta tsana bai wuce kukan ummita ba ,gashi me dalilin sata kukan rayuwarta ce bata haɗa shi da komai ....

Ana cikin haka meenal tashigo tana kuka ta rungume ummita ajikinta "sai da nace karki yi ummita karki sameshi da maganar amman kika yarda, kalli da yadda fuskarki tayi ta k'arasa maganar tana shafa daidai inda ya mareta, ya rayhan yace "au kinsan abinda ya hadasu ne ?
Kai ta d'aga masa alamun tasani sannan ta zayyano masa abinda ya faru da abinda ummita ta faɗa wa ya ma'aruf...

Ahankali mama ta buɗe idanunta "sai kiyiwa mutane shiru mara jin magana "haba mama da me zata ji mari har uku fa bayan zaginta da yayi inji cewar rayhan" ka barni da yarinyar nan rayhan wannan ai rashin kunya ne har yar'uwarki na baki shawara kice sai kinyi saboda gaki tattacciya, zaki tashi ki 'bacewa ganina anan ko sai na qara miki wani marin ..

"Haba mama Allah sai dai ki haɗa dani ki mara ,"hannu ummita ya kamo" tashi kije ciki kinji my everything yayi mata maganar adaidai kunnenta, ta soma tafiya tana kuka "gaskiya mama bai kamata kice mata haka ba ,zai sa taji kamar kin tsaneta ne shine fa yake fara shiga rayuwarta, ina ma ruwansa da masu zuwa ba'a kulasu ban da dai bakin ciki irin nasa, an ce masa tayi kwantai ne da zai dinga neman talla da ita ?
"uhnmmm rayhan kenan kai ma kana yi kamar ba kasan ummita ba .....



Two friend's ( bsbs)

💗💗💗💗💗💗
WANNAN CE
QADDARARMU
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

~TRUE LIFE STORY~

FREE NOVEL NOT FOR SELL


AL'QALUMAN



*AYSHA A BAGUDO*
*FAIZA HAMMADU*


~DEDICATED TO~
MARYAM ALHASAN D'AN IYA
(MARYAM OBAM)

BEST FRIEND FOREVER AND EVER, AKWAI AMANA 'KAWARMU ALLAH YA BARMU TAREN TARE SON SO FI SABILILLAH 🥰🥰

WATTPAD @HAUESH

bismillahirrahmanirrahim


*RIGIJI GABJI,RANAR KUKE JIRA YAU GATA TAZO MASOYA*


*MARUBUCIYAR NAN TAKU WADDA TA SABA KAWO MUKU LITATTAFAI INGANTATTU MASU TSUMA ZUCIYAR ME KARATU WATO HASSANA D'AN LARABAWA*

*MARUBUCIYAR*:

SANADIN HOTO
Da
HASSANA DA HUDSAINA

*YAU TA SAKE DAWO MUKU DA SABON LITTAFINTA WANDA YA ZARCE DUK LITATTAFANTA A KOMAI WATO CIN AMANAR RUHI,KAI DAGA JIN SUNAN KUN SAN AKWAI TAFKA TAFKA DA K'ULLE K'ULLE ,AMMA ZATA WARWARE MUKU K'ULLIN DA ZARAR KUN BIYA 200 DOMIN SAMUN LITTAFIN,KAR KU BARI YA WUCEKU ,DOMIN WANI IRIN LABARI NE DA BAKU TAB'A CIN KARO DA IRINSA KO MAI KAMARSA BA,FAD'AKARWA ,NISHAD'ANTARWA,ILIMANTARWA,TAUSAYI,DA SOYAYYA ME TSAYAWA A ZUCIYA ,TARE DA WATA IRIN CIN AMANA DA BAKU TAB'A RISKAR IRINTA BA,KU DAI KU HANZARTA NEMAN MARUBUCIYAR DOMIN KU SIYA KU KARANTA AKAN KUD'I K'ALILAN 200*

*ZAKU IYA NEMANATA AKAN LAMBARTA KAMAR HAKA,08080049548 DAGA NAN ZATA GAYA MUKU YADDA ZAKU BIYA KUD'IN ,KU DAI KU HANZARTA KAR AYI BABU KU ,KU TUNA DA SUNAN LITTAFIN*

CIN AMANAR RUHI KARKU DAKE A BAKU LABARINSA
🥰🥰🥰🥰


PAGE 6

...Cike da tausayawa meenal ta sake matso hawayen dake cikin kwarnin idanunta suka gangaro bisa kuncinta tana duban fuskar mama cike da jin haushi da takaicin maganarta ,
ta kasa fahimtar wani irin matsanancin so mama take wa ya ma'aruf , "wacce irin shakuwa ce haka a tsakaninsu da har zata fifita shi akan diyar cikinta ?
Mama bata ganin laifinsa akan komai da zai aikata ,sannan bata son taji an fadi laifinsa akan komai matsawar kuwa ayi kuskuren faɗar laifinsa a gaban ta yanzu ne zata nuna bacin ranta, kallon mama mennal take har zuwa lokacin wacce abubuwan da ya ma'aruf ke wa tilon diyarta sam baya damunta wani lokacin ma har karfin gwiwa take ƙara masa .....

kusan minti shabiyar da barin ummita parlour'n amman hawaye ne yake cigaba da zubowa daga idanun meenal, barin ma data tuna itace silar komai ,tunda ta rigada tasan muguwar tsanar da suka yiwa juna ...

Sautin muryar mama ce ta doki kunnen meenal "Ki tashi ki wuce tun baki qarar da ruwan hawayenki a banza ba.. meenal ta marairaice murya tace "haba mama ki daina yin haka , da me kike son taji ?
"mari fa ba d'aya ba har uku ya ma'aruf yayi mata a kuncinta , ai hakan bai kamata ba a matsayinsa na babba , gaskiya mama ki dinga adalci daga ya ma'aruf har ummita naki ne kamar yadda kowa ya sani ,ki daure ko sau ɗaya ne kiyi masa magana akan abinda yake yiwa ummita nasan zai fahimta..

"Wallahi muddin kece kika faɗa masa illar abinda yake yi am very sure zai fahimceki kuma ya daina saboda yana matukar jin maganarki ,
yana ganin girmanki fiyye da uwar da ta kawo shi duniya....
"kema kinji abinda kika ce, mutumin dake ganin girmana da muntuncina, mutumin da zai iya tsallake maganar uwar data kawo shi duniya akaina, shine mutumin da kike tunanin na yiwa magana dan ya hukunta diyar cikina bisa ga laifinta..
"To na zaunar dashi na karanto masa me "nace masa me ya hukuntata ko me kike son nace masa?
" ki ce masa duk abinda zai had'asu da ummita ban da duka ,murmushi mama tayi "kai meenal an gaisheki mai yar'uwa kema sai kiyi yar'uwartaki faɗa ta daina abinda take yi ,rashin kunyarta bata karewa akan kowa sai d'ana "to mama ai shine yake farawa "ke dai tashi kije ki cire uniform kici abinci ki hutawa ranki da wannan damuwar ita kanta wacce kike fushin akanta ma killa tayi bacci.

Ta mike ranta a matukar 'bace "Allah tunda abun ya zama haka da Abbanmu zan hadashi tun da ba jaka bace, ina laifin yayi mata faɗa amman komai duka .

"Ni dai babu ruwana kije kiyi abinda ke gabanki, ai duk rashin kunyarta ne ya jawo mata ,ni nasan ma'aruf matukar bata shiga lamarinsa ba ,ba zai shiga nata ba dan haka ko gobe tayi masa rashin kunya ya ninka mata fiyye da wanda yayi mata yau a fusace ta bar part din mama tana gunguni dan taji zafi sosai ..

rayhan dake zaune ya tasa mama gaba da kallo ya girgiza kai "gaskiya mama zaki jawo ayi bala'i a gidan nan ,zaki sa mu samu matsala da ma'aruf akan wannan duke duke .
"wannan kuma damuwarku ce kun fi kusa idan dai ummita ce kaima baka tsira ba agurinta , zuciyarsa na matukar zafi ya mike ya fito daga part din mama ..


Ummita kuwa tana shiga d'akinta ta zube akan katifa , wani sabon kuka ya kufce mata , numfashinta ne ya soma canzawa ya dawo yana fita ahankali tamkar mai cutar asma .....
yayinda zuciyarta ke mata wani irin zafi tana harbawa da sauri ,gefen guda kuma wani irin azaɓaɓɓen ciwo kanta ke mata, hannuwanta duka tasa ta rike kanta da taji kamar zai fita a saman wuyanta , juyi kawai take akan katifa,tsawon lokaci tana kwance tana fama da ciwon kai da ciwon zuciyata gashi bacci yaki d'aukarta bare ta rage jin azabar da take ji a sansar jikinta hatta kayan makarantar dake sanye ajikinta ta kasa cirewa ,jikinta yayi wani zafi tamkar garwashin wuta , cikin haka meenal ta shigo d'akin, ta qaraso da sauri saboda ganin yadda take rike da kanta, dafe da gefen zuciyarta, muryarta a marairaice kamar zatayi kuka tace " sannu ummita meke damunki ?
"Ko kanki ke ciwo ?
"Zuciyata meenal zuciyata zata buga zafi nake ji ......"sannu kema dan Allah ki daina biyewa ya ma'aruf ki dinga barinsa da halinsa ,
Kin san halin ya ma'aruf bashi da kyau ta kowani fannin ..ki rabu dashi Allah zai saka miki mugu kawai ta ta k'arasa Maganar tana rungumota jikinta" ki rabu dashi Allah zai saka miki "bafa zan barshi ba meenal dole na dinga kwatowa kaina 'yancina , har yaushe abubuwa zasu daidaita a tsa....
tari ne ya tsarketa, ta dinga tari tana sake dafe dai-dai saitin zuciyarta.. da sauri ummita tayi hanyar fita domin kawo mata ruwa ..

cikin wani irin yanayi ta yunkura ta mike ta fito zuwa parlour'n kasa, akan step suka haɗu da meenal hannunta rike da cup din ruwa,tayi saurin kamota jikinta "sannu ummita da kinyi zamanki adaki "kamota tayi sosai suka sauko ta kwantar daita akan kujera mai zaman mutun uku tana jero mata ......

Mama ta leko daga kitchen saboda jin motsin mutune ganin yadda meenal ta riko ummita dake faman runtse idanunta tana jujjuya kai yasa ta fito da sauri zuwa gareta fuskarta tattare da damuwa ..
ko cikakken minti biyu mama ba tayi tsaye akan ummita ba ya rayhan ya shigo part din ....

muryarta a raunane irinta marasa lafiya ummita tace" yayaaaaaaa.........
da sauri ya nufo inda take haɗe da cewa "mama lafiya "me ke damun sarauniyata ?
Ya faɗa tare da ƙoƙarin taɓa wuyan ummita. .
"Murmushin yake mama tayi "kai kasan son jiki irin na ummita ina ganin zazzaɓi mari za'a yi... "wasssssss mama kaina zai cire,zuciyata zafi .... tayi maganar hawaye na gangaro mata ,maganar da ummita tayi yasa mama yin shiru cikin damuwa ,ya rayhan yace "plz mama bari na ɗauketa na kai ta hospital ,ina masjid jikina ya bani sarauniyata babu lafiya shine nazo" mama a kira min doctor husain...
Mama bata ce komai ba illa ciza lip's dinta da tayi tattare da damuwa "karki damu yanzu zan Kira shi , mama ta nufi hanyar d'akinta cikin sauri ,shi kuma ya rayhan ya zauna kusa da ummita ya kamo hannuta ya haɗe cikin nashi yana faman yi mata sannu "Allah ya baki lafiya my princess inshaallahu zaki samu sauki ..

"Ya rayhan jikinta yayi zafi sosai ,wai me yasa ya ma'aruf ke yin haka ne? Kwata kwata babu emani acikin zuciyarsa ko daraja mama ya kamata ya daina wasu abubuwan jin furucin meenal dake shiga cikin kunnenta yasa ta soma yin kasa daga jikin ya rayhan tana kiran sunan
"meenal .......
"na'am ummita "dan Allah karki sake ambaton suna nan sa anan ina jin kamar na mutu ,zuciyata na sake jin ciwo mai rad'ad'i ...."sannu shikenan na daina ....

******
Dr husaien zaune a gabanta bayan ya gama aune aunensu na likitoci ya daura mata drip ya tsura mata ido kawai yana Kallonta fuskarshi ɗauke da damuwa ,
muryarsa can kasa ya kira sunanta "ummita meke damunki ?
"Tunanin me kike yi haka da har zuciyarki ke daf da kamuwa da ciwo mai tsanani ?
"faɗa min meye damuwarki a rayuwa ,?
Tayi shiru ta kasa ce masa komai "ina sauroronki ki faɗa min abinda ke damunki kafin na sheidawa iyayenki jininki ya hau fiyye da ka'ida watakilla su zaki sanar musu da damuwarki .


"Doctor kai taimaka karka sheida masu komai ina tausaya musu, ina tausayawa halin da zasu shiga ,na fi jin tausayinsu akan kaina, plz karka faɗa musu wallahi babu abinda ke damuna idan kuma akwai zan faɗa maka ..

"No ummita akwai damuwar dake damun zuciyarki idan kika cigaba a haka ciwon zuciya zai kamaki jininki ya hau sosai ,dan haka ki faɗa min tun wuri ayi maganin matsalar ko
"Kin fi son Sai lokacin da ciwon zaici karfi ajikinki , mutuwa ta riskeki sannan suji abakina ?


"Ni doctor tare da irgiza masa kai "to ki cire damuwa aranki ,kina yawan damun zuciyarki da tunani shiyasa zuwa yanzu ta soma samun rauni ,har kika fara jin ciwo ,da zaran ciwon ya kama zuciyarki gaba-daya shikenan sai mutuwa ko kina son ki mutu tun yanzu ne ?

"inshaallahu ma babu abinda zai sameni kuma nayi maka alkawarin bazan sake damun zuciyata ba, "kenan kinsa abinda ke damunki har jinin ya hau ?
Sake girgiza masa kai tayi "a sanina bani da damuwar komai sai ta karatuna .

Girgiza kai yayi "Allah yasa amman ya kamata dai su sani "don't worry doctor tunda ciwon bai rigada ya kamani ba kaga ai bai kamata a faɗa musu abinda zai tada musu hankali ba ,shiru yayi ya cigaba da bata kulawa yana tambayarta "me matakin karatunki ?
ahankali ta motsa bakinta ,"bana na qare secondary school ina jiran result ne "kenan zaki cigaba ?
"Sosai kuwa shine cikar burina " kina ganin abbanki zai barki ki cigaba da karatu ?yayi mata tambayar yana tsareta da idanunsa"gaskiya bazan sani ba ko zai bari amman nasan dai zai barni inshaallahu "Allah yasa" matakin karatun addini fa kin sauke ne Alqur'ani ne?
"Eh nayi sauka tun shekara biyu data gabata yanzu shahada zan amsa sabon wata inshaallahu .
Doctor ya jinjina kai tare da yaba mata hakan yasa yaji ta sake shiga ransa tambayoyi ya cigaba da yi mata har sanda meenal ta sake shigowa " sannu ummita Allah ya baki lafiya ?
"Ameen ta faɗa tana lumshe mata ido "guri ta samu ta zauna kusa daita tana cigaba da yi mata sannu, yayinda bacci ya soma fizgarta dan har ta soma ganin mutanen dake zaune dishi dishi , mama ta sauko tana yi mata sannu ,"doctor meke damunta ne ko sai mun dangana da hospital saboda naji tana ta complain din zuciyata ?

muryar doctor husaien taji cikin kunnenta " "Hajiya muje daga waje ina son muyi wata magana mai mahimmanci "okay doctor Allah yasa ba wata damuwar bace ?
Doctor yayi gaba mama ta biyo bayansa
da sauri ummita ta kamo hannun meenal "dan jiyo min mai likita zai faɗa mama ...
"kamar la'be zanyi musu kenan bayan kin sha cewa babu kyau ",eh la'be haramu ne ba kuma shi nace kiyi musu ba , jiyo min kawai abinda zai faɗa mata zakiyi nasan ko tsaya wa kika yi a gabansu mama bazata koreki ba akwai abinda bana son doctor ya sanarwa mama ne ..
Kamar bazata tashi ba sai kuma ta mike tabi bayansu ...

Suna ƙoƙarin fitowa daga part din sai ga ya rayhan "yauwa doctor ga rayhan nan kana iya masa bayanin komai sai ya sanarwa abbansu , rayhan likita yace akwai magana mai mahimmanci da zai faɗa dangane da Ummita sai ka sauraresa ta fadin haka tana juyo ta dawo ciki ,ganin haka yasa meenal dawowa da sauri ta zauna batare data ce komai ba .
"Uhmmmm likita ina sauraronka, ka yi shiru kamar baka san da tsayuwar mutun ba sautin muryar rayhan ta ratsa kunnuwan doctor Wanda kana jin muryarsa kasan cike take da rauni da kuma fargaba .. naunauyen ajiyar zuciya doctor ya sauke "daman jinin ummita ne ya hau sosai fiyye yadda ake bukata shine ma abinda ya haddasa mata zazzafan ciwon kai da zafin zuciya wanda idan ba'a hattara ba komai zai iya faruwa daita ,girgiza kai ya rayhan yayi yana bin likita da kallo "to meke damunta ?
"Me ye hadinta da ita ?
"Wannan amsar na gurinta duk da nayi iya kokarina naga ta faɗa min ,ku dai bita a hankali nasan zata faɗa doctor ya k'arasa maganar yana mikewa ya rayhan hannu shima ya mika masa sannan ya wuce ..
Jiki a sanyaye ya shigo part din inda ummita ke kwance zuwa lokacin bacci ya ɗauketa gabanta ya durkusa ya tsira mata ido yana dubanta soyayyarta da tausayinta na sake huda zuciyarsa..
Parlour'n yayi shiru baka jin motsin komai sai numfashin mutanen dake zaune a cikinsa.

*****

bangaren ma'aruf kuwa kai tsaye gidansu suhaima ya nufa ,cike da rawar jiki batare data yi la'akari da yanayinsa da yake ciki ba ta faɗa jikinsa har yana iya jiyo dumin manya dukiyar fulaninta ,runtse kyawawan idanunshi yayi yana jin kirjinsa na dokawa , idan akwai abinda ya tsana bai wuce yaga tana yi masa tallar Brest dinta ba ,zareta yayi a hankali ya zauna tare da d'aura kafarsa ɗaya kan daya yana kare mata kallo can yayi gyaran murya "suhaima ...
"Na'am habibi "banason abinda kike min bana son kina.....saurin dafe goshinsa yayi saboda bazai iya qarasawa ba "uhmmmm ina jinka me akayi ,kuma meye baka so ?
tayi maganar tana sake matsowa inda yake yayi saurin dakatar daita "kinsa abinda kike yi kuma kinsa bani da interest so stop it I don't like it ,ba shashanci ne ya kawo ni gurinki ba aurenki zanyi dan....
Kawai yaji ta rushe masa da kuka "dan kaga ina rungunarka shine
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On WANNAN CE QADDARARMU
avatar
amina-4

11 months ago

Reply

Interesting novel

avatar
amina-4

11 months ago

Reply

Interesting novel

Please Login or Register in order to submit comment