Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

zaka dauka yar iska ce ni ,wallahi duk soyayarka ce ta sa kaga haka amman babu komai na gode da fassarar da ka min ta fadi haka tana matso ruwan hawaye ,hakuri yake son bata tare da fahimtar daita amman ya kasa kawai yayi shiru ya cigaba da kallonta ..

Gaba-daya suhaima ta kasa gane kanshi
A kallon da take masa yanzu ta fahimci akwai abinda ke damunsa ,shi yasa yaji haushinta dan ta shimfida masa brest dinta ,sau nawa tana yi masa bai taɓa cewa baya so ba sai yau ,
Ganin idan suka cigaba da shirun itace zata kwana ciki dan tasan halinsa idan zasu kwana tare tunda yayi irin wannan shirun bazai yi magana ba , ahankali tayi ta bashi hakuri tana lalla'bashi batare da tayi kuskure gurin salon bada hakurin ba ,bare yayi mata sha bala'i, ko ɗaukar fushi daita ..


har yaje gidansu suhaima abinda ummita tayi masa na damunsa cikin ransa ,sam ya kasa boye damuwar da yake ciki , har ya dawo gidan bai bi ta kan kowa ba d'akinsa ya shige ya kulle kansa ..sai gurin takwas na dare ya fito daga part sanye cikin riga hamles fari da wando three quarter Sai kamshi turaren 24k yake zubawa yana taku ahankali cike da izza..
Bangaren mama ya soma shiga ya iske ummita kwance kanta babu dankwali sai gashin kanta da yayi mata hijabi, tautaunawa suke ahankali wanda ba zai ce ga abinda suke magana ba tsakaninta meenal ba ,binta yayi da wani irin kallo bai san sanda ya lumshe ido ba, ahankali ya qarasa shigowa parlour'n yana binta da kallo rigar jikinta da kallo, idanunsa bai tsaya ko'ina ba sai kan yalwataccen sumar kanta mai sheki ,duk ajikinta babu abinda ke ɗan daukar hankalinsa kamar sumar kanta shima yasan yana da nasaba ne da son macce mai gashi da yake ,

tana ganin shigowarsa ta haɗe rai tamkar wacce aka aikowa da sakon mutuwa , ta janyo hijab dinta dake gefenta ta rufe gaba-daya jikinta har fuskarta ta runtse idanunta gam ..

Ganin ya samu guri ya zauna yasa meenal mikewa tsaye ta gaida shi aciki ta fice dan har lokacin haushinsa take ji ...


Two friend's (bsbs )

💗💗💗💗💗💗
WANNAN CE
QADDARARMU
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

~TRUE LIFE STORY~

FREE NOVEL NOT FOR SELL


AL'QALUMAN



*AYSHA A BAGUDO*
*FAIZA HAMMADU*


~DEDICATED TO~
MARYAM ALHASAN D'AN IYA
(MARYAM OBAM)

BEST FRIEND FOREVER AND EVER, AKWAI AMANA 'KAWARMU ALLAH YA BARMU TAREN TARE SON SO FI SABILILLAH 🥰🥰

WATTPAD @HAUESH

bismillahirrahmanirrahim


PAGE 7


...Har lokacin da yake zaune yana fuskantarta zafi yake ji a cikin zuciyarsa ,kallonta kawai yake yana jin zallar tsanarta da 'bacin rai mara misaltuwa, ban da furzar da huci babu abinda ke ta fita daga bakinsa , shi kaɗai yasan yadda yake ji a cikin zuciyarsa ,damuwa ne suka taru suka addabi zuciyarsa, lamarin suhaima da ummita koda yake shi al'amarin ummita qarami ne akan na suhaima.

a tun a wannin da suka gabata zuciyarsa ta soma yakiceta a muhallinta , ba dan baya son mallakarta s matsayin matar aurensa ba sai dan tsoro , tsoro alamarinta da rayuwarta yake bashi ,baya jin tafiyarsu zata d'aure har zuwa ga aure .....

"idan kana tunanin gujeta mata me kake tunani mahaiifinta zai d'aukeka ?
zuciyarsa tayi masa wannan tambayar mai cike da tarwatsa zuciya ..
"Tabbas maganar da mutane suka faɗa masa akanka zai tabbatar gaskiya ne ba karya ba ,zai tabbata kai din mayaudari , abinda ya kamata kayi kawai ka kauracewa zuwa gurinta na wani lokaci har zuwa sanda manya zasu shiga zance ya zanta da zuciyarsa yana sake furzar da iska mai zafi, yana cikin wannan tunanin ne mama ta sauka ..

"A'a Ma'aruf yaushe ka shigo?
Ahankali ya d'ago kyawawan idanunsa masu matukar kyau waɗan da suka wadatu da gashin gira dana ido ya zuba mata , sanye take cikin wata had'add'iyar doguwar riga majeter colour da jerin s stone tun daga sama har qasa , tayi kyau sosai a cikin rigar bama za kace itace ta haifi ummita ba, ko kuma ta dade a gidan miji kafin ta samu haihuwar ummita ba saboda yanayin tsarin jiki mai kyau da Allah yayi mata ..
Muryarsa a kasalance yace "ban jima da shigowa ba "

"A zubo maka abinci ne ?

" zubo min mamana tun safe ban ci komai ba "
"me yasa kake son zama da yunwa ?
"Ka daina barin kanka da yunwa ina ma kaje duk yau ban jika ba a gidan nan ?
"Ina gida ai tun safe sai gurin biyu na rana na fita zuwa gurin suhaima. "ayya ya suhaima take ?
"Tana lafiya tace a gaisheki "aiko ina godiya da gaisuwa ya dai kamata ka kawo min ita ta ganni na ganta muyi ido da ido daita sannan muyi kunne da kunne ta qarasa maganarta tana nufar dining table ..
"Ai dole ma tazo taga mamana idan batayi miki ba dole a canza ta ..

Murmushi mama tayi sannan tace "wannan gaskiya ne amman ai nasan ma'aruf dina bazai taɓa zaɓen tumun dare ba ... tana magana tana zuba masa abinci a plet ,ta dawo inda yake ta miko masa .
ya amsa yana kallon abinci "mama abincin nan fa yayi yawa "kai da kaci iya cinka ka bar sauran ,"na rasa dalilin dayasa baka son cin wadataccen abinci shiyasa gaka nan jiya iyau kullun ba kibar arziki "kiba fa halitta ce ma ba wai cin abinci ba, mama bata sake cewa komai ba shi kuma ya fara cin abinci , parlour'n yayi shiru kowa da abinda yake tunani gaba-daya tunanin mama ya tafi ne akan rashin lafiyar yarinyata Khadeeja ce ta shiga ta katse shiru da parlour'n ya ɗauka "ya ma'aruf wai in ji sakinar gidan baba sarki tace kazo tana son ganinka ,a fusace ya d'ago tare da galla mata wata uwar harara "get out tun kafin inzo in tattakaki anan ubanki zan mata idan nazo ..

Juyawa ta shuri takalmanta ta bar parlour'n tana qunkuni ganin yadda yayi mata kamar itace tace sakinar ..abinci daya kasa cigaba da ci kenan ya shiga jan tsaki "kai kuwa ma'aruf ba'a yin haka ya kamata kaje kaji me zata ce maka "rabu daita mama yar rainin hankali ce wai kamar sakina dan ta rainani zatace wai ni take so ina zan kaita mama ?yayi maganar yana furzar da iska "au batun na soyayya ne ai na ɗauka ko sada zumunta za'a yi , Allah ya sawwaka to me zai hana ka duba lamarin idan zai yiwu sai ka haɗa su su biyu da suhaimar "to ai ko ita suhaimar ma bangama tantancewar aurenta ba bare sakina da girme ta girmeni mama tayi mursmush irin nasu na manya sannan ta mike a hankali ta isa inda take ummita ke kwance ,ta yaye mata abinda ta lullu'be jikinta dashi "sanyi kike ji ne kika wani lullu'be jikinki haka ?
Muryarta a raunane tace "a'a mama na fi so jina haka "ma'aruf ya ta'be baki saboda yasan saboda shi tayi haka , aransa yace aikin banza yarinya ko kallo baki isheni ba "tou ai shikenan mama ta nufi hanyar step "ka daure qarasa cin abinka "ai wannan sakon ya 'bata min rai bazan iya sake cin komai ba ..
"Ka dai bi ahankali dan Allah karka je ka biyewa son zuciyarka ta fad'i haka tana taka step ɗaya bayan ɗaya ..

Ya ɗan dade zaune agurin yana tunani har sanda bacci yayi nasarar daukar ummita ,
Ganin tunanin ba zai bar kanshi ba yasa shi mikewa tare da zura takalmi ya isa inda ummita take ya kai hannunsa kai tsaye ya yaye abinda ta lullu'be jikinta dashi turus yayi saboda ganin bacci ya ɗauketa ,tsura mata ido yayi yana kallon shashin hannunsa kwance akan kuncinta kasancewarta fara , ahankali yaga ta motsa tana juyawa tare ƙoƙarin sake jan hijabinta bata samu nasarar janyowa ba, ta mirginowa zata fad'i ma'aruf na kallonta kamar ya tara duka hannunwansa saboda bata kariya , amman ya share dan bai son jinta a kowani Shashi na jikinsa aiko dum kake ji a kasa ta fado bisa kafafunsa da sauri ta bude idanunta sukayi 4 eye's dashi .....
Ido cikin ido suke kallon juna fuskar kowannensu cike da mamaki ," a fusace yace "dan malama tashi akan kafafuna tayi shiru tana rike da gefen cikinta "ki tashi stupid ki koma d'aki kin wani zo kin kwanta anan salon kowa sai ya fahimci baki da lafiya ya fad'i yana rakata da ƙatuwar harara , kallonsa kawai tayi ta 'bata rai ,batare da tace masa komai ba ta soma ƙoƙarin mikewa dan tayiwa kanta alkwarin ba zata sake shiga lamarinsa ba matukar ba rashin mutunci yayi mata ba ,hanyar step ta nufa yabi bayanta da harara dan baya son abinda zai haɗa shi da yarinyar .....

bangaren su meenal da jiddah da sa'ada zahra suna tsaye kowa wacce tana faɗin albarkacin bakinta akan ummita da abinda ya faru ,wasu suga laifin ummita yayinda wasu suga laifin ma'aruf ,yazo zai wuce su ,suka gaishe shi ,babu wacce ya amsawa acikinsu har ya isa makeken parlourn Abba .

Guri ya samu ya zauna a gefen abba tare da risinawa "ina yi Abba "

Abba dake kan kujera sanye idanunsa cikin medical glass tana rike da jarida yace "Lafiya lau ma'aruf ya kake fatan kana lafiya?

"Lafiya Abba "
"Kuna nan dai kuna shirin soma zuwa office Kou?
"Inshaallahu Abba ni kusan na matsu mu soma fita zaman ya dameni wallahi "
Abba yayi murmushin jin dadi "shi yasa kake qara shiga raina saboda himmarka , Allah yayiwa rayuwa albarka "ameen ya amsa "Abba ya mike "bari naje na sake ganin yanayin jikin mamana yinin yau duk bata ji dadi ba, har likita yazo ya min dubata ,mikewa yayi a daidai lokacin da wayarsa tayi qara bai ɗauka ba saboda suna tare da abba ,tare suka fito , shi ya nufi hanyar fita waje ,shi kuma Abba ya nufi bangaren mama ..

Yana ƙoƙarin fita waje yana danna number jafar kira daya jafar ya d'auka "kaga manya inji kanana wai ina kake shigewa ne kwana biyu shiru ko gurin suhaima kake lalla'bawa ne ?
"Kaga dan iska yaushe kazo gurina da baka ganni ba bare kace gashi gashi ?
"meye labari ne ina son zamu shigo gobe tare da Sa'id inshaallahu"Allah ya kawo ku lafiya "ina waccen sarkin rigima ?
Tsaki ya ja yana canza salon maganar tare da katse kiran ,yana gama katse kiran jafar kira suhaima na shigowa, yaki ɗauka tayi kira ya kai sau biyar amman yaki ɗauka daga karshe ma ya kashe wayar gaba-daya .. ..

Washegari duk ahlin dake rayuwa a gidan kwansu da kwarkwata babu wanda bai shigo duba jikin ummita ba, hatta kakarsu jiniya da bata son ummita da mahaifiyarta sai data shigo duba lafiyarta, shi kuwa ya rayhan kamar shine yake jinyar tsabar fargaba har wata doguwar rama yayi duk wata kula wa da kula da shan maganinta shine ..

Bayan sati daya


Ummita taji sauki sosai sai dai har lokacin bata zuwa ko'ina tana kwance a parlour'n su tana kallo twist of fate , Khadeeja ta shigo, ta miko mata wata farar envelope mai shegen kyau daga ni bana kasar nigeria bane kin amsa ummita tayi ,illa binta da idanu da tayi tana kallonta "ki amsa mana kina wani kallona .
"nayi me dashi ?
"Ke akace na bawa ?
"Inji wa kenan fa ?
"idan kin buɗe zaki ga ko waye tayi shiru tana tunani ,ita kuwa Khadeeja ta ajiye mata envelope a saman cinyarta ta juya tana magana ahankali "dadina dake yangar bala'i mijin da zai aurenki yana da aiki wallahi..
ta dade zaune agurin bata san lokacin data wuce ba ..

Ahankali ta mike tsaye daga zaunen da take ta soma takawa zuwa hanyar d'akinta ta zauna a gefen gadonta tana sake juya envelope din .. kafin daga baya
a hankali ta buɗe envelope wasu takardu ne suka zuba ta d'aga greating cards din farko mai ɗauke da sakon murnar samun lafiyarta, na biyu dana uku kunshe suke da kalaman soyayya masu tsuma rai da sanyaya zuciya a kowane kasan greatig card din sunan hafiz almustapha ne a rubuce .

Tabi katunan da kallon mamaki ba wai burgeta ne basu yi ba ,mamakin nisan tafiyar da suka sha kafin su iso gareta tare da dinbin al'ajabi yadda mai sakon yasan halin da take ciki alhalin sun ɗauki tsawon shekaru batare da sunyi arba da juna ba ..

Ranar had'uwarsu ta karshe ranar yake sanar mata zai koma makaranta yayi wani cos na tsawon shekara biyu , a lokacin ne ta rokeshi da kada ya sake kawo mata ziyara arayuwarsa dan ita babu ajandar yin soyayya nan kusa asalima babu batun soyayya agabanta..

A lokacin ta fuskanci maganar datayi ta maseefar bata masa rai matuka ,domin ya juyata da mummunar fassara " nasani subai'a ni ne baki so ba wai soyayyar ce bata gabanki ba ,nasan ni ke kidina da rawana, tabbas nasan ni ne baki so kuma baki damu da halin da zan shiga ba ....

Ajiyar zuciya ta sauke alokacin da abubuwan da suka fara suke dawo mata " idan har soyayya ta zame mata dole tabbas ya rayhan yafi cancanta taso domin shine mutun na farko daya soma furta mata kalmar soyayya arayuwarta, tun lokacin da take da shekarun da basu wuce goma a duniya ba, lokacin tana aji daya a secondary..

Shi kuwa almustapha malaminta ne wanda natsuwarta da kaifin baserarta da saukin kai, su suka fara cusa kaunarta a zuciyars malam hafiz almustapha kusan a cewarsa tafi kowacce daliba fahimtar darasi da yake daukarsu history ,ya jima yana dakon soyayyarta kafin cikin dabara ya fahimtar daita take ta sanar masa ita yarinya ce bata isa aure ba ,kuma karatu zata yi cikin murmushinsa mai bugar da zuciya yace " nima ai yaro ne har yanzu subai'a , ban isa aure ba zan jiraki har zuwa lokacin da zaki girma ki gama karatunki sai muyi aure , lokacin da yayi kokarin kawo mata ziyara kuwa dakatar dashi tayi saboda gudun bacin rain ya rayhan da kuma rashin amincewa da zance ,duk da bata son ya rayhan bazata so ya ganinsa cikin damuwa ba .....

"Hafiz almustapha ta furta ahankali tana runtse kyawawan idanunta ..


Two friend's (bsbs)

💗💗💗💗💗💗
WANNAN CE
QADDARARMU
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

~TRUE LIFE STORY~

FREE NOVEL NOT FOR SELL


AL'QALUMAN



*AYSHA A BAGUDO*
*FAIZA HAMMADU*


~DEDICATED TO~
MARYAM ALHASAN D'AN IYA
(MARYAM OBAM)

BEST FRIEND FOREVER AND EVER, AKWAI AMANA 'KAWARMU ALLAH YA BARMU TAREN TARE SON SO FI SABILILLAH 🥰🥰

WATTPAD @HAUESH

bismillahirrahmanirrahim


PAGE 8


............ Tana zaune a gurin shiru hankalinta yayi nisa cikin tunanin hafiz almustapha .....
kusan minti goma ta ɗauka zaune tana nazarin katuna nan daya turo mata a matsayin tuni ga soyayyarsa .
ta rasa a wani muhalli
ya kamata ta'a ajiye lamarinsa , motsin shigowa d'akinta da'ake ƙoƙarin yi ne yasa tayi saurin dawowa haiyacinta haɗe da tattara katunan greating card din ta tura a karkashin pillow baccinta ta maida idanunta kan kofar shigowa ..

Mama ce ta shigo tana dubanta a tsanake sai dai fuskarta cike take da damuwa "yaya dai ko jikin ne naga kin dawo d'aki ?
Murmushi tayi wanda ya bayyana kyawun fuskarta sannan tace "A'a mama nifa na rigada na warke sumul, babu abinda ke damuna, sannan babu inda ke min ciwo.
Naunauyen ajiyar zuciya mama ta sauke ahankali "har na ji sanyi a cikin zuciyata dan bana son ciwon kan nan naki mai naci tsiya ...

"mama kenan kina nuna kamar kina sona alhalin ni nasan ba haka bane , "Allah ko saboda bana bin bayan karya akan gaskiya ba ?
Ni tashi kije ga rayhan can yana jiranki a parlour'n , ummita ta mike daga zaunen da take tana yatsina fuska "kai nifa na soma gajiya da nacin nan nasa .

"lallai ummita wuyanki ya isa yanka rayhan din kike cewa haka ?
" mutumin daya damu dake ya damu da lafiyarki ,rayuwarsa ce kawai ba zai iya baki ba ,ke ko bayan raina nasan ba zaki yi kukan maraici ba matukar rayhan kika aura..... matsalar dai uwarsa, fitinarta nake tsoro bancin haka ni kaina mai tsayawa rayhan ce, ai duk mai son naka ya gama maka komai a rayuwa .
Ummita ta ta'be baki "ni kuma Kinga bana kawo ummansa a raina, ko dan ɗan nata baya cikin zuciyata ne ban sani ba.. "ke rufe min baki kullun maganar kenan ba'a miki ba , naga ranar da zaki ce ga wanda zuciyarki take so, ki dai tsaya kallon ruwa ....
tun kina samun masu sonki har kizo ki rasa .
"haba mama karki min baki mana ke fa mahaifiya ce, idan kina furta haka komai zai iya faruwa dani fa ,"ba baki bane ummita ni kaina nafi son kiyi aure da Karachi shekarunki..

"Ni mama wani aure zanyi yanzu nida nake son na cigaba da karatuna "ni dai nafi son kiyi aureki yanzu saboda .. ..

"na haifa miki jikoki tun kina raye ba ?
Tayi hanzarin katseta ta hanyar fadar haka tana murmushin tsokanar mahaifiyarta "wallahi zan murd'e wannan bakin rashin kunya ...
Ummita ta matso sosai da bakinta kusa da mama "to ga bakin ki murd'e... mama ta kamota da niyyar murd'e bakin aiko ummita ta rungumeta tsam ajikinta suka zauna a gefen gado suna murmushi tare da fuskantar juna "ummita ..
mama ta kira sunanta a tsanake "na'am mamana ,duniyata,
farincikina "ki dinga hakuri da rayuwa ummita ,ki dinga danne abinda baki so a cikin zuciyarki, banason yadda kuke yi da ma'aruf, sanin kanki ne bazan tsani ma'aruf saboda ke ba ,kin tashi kin buɗe idanunki kin ganshi a d'akin nan muna rayuwa ....
" duk abinda zai miki kiyi hakuri ki ɗauka tamkar nice nayi miki , ni nasan haka nan ma'aruf ba zai tsaneki ba ,akwai dalili da yasa ya tsaneki .
"me ye shi mama ?
"Me ye dalilin tsanarsa gareni ?
"Nima ban sani ba sannan bansan dalili ba amman da zaki canja ummita da zaku dinga shiri dashi "babu wani dalilin tsanar dake tsakaninmu , ni sam bana buƙatar shiri dashi a rayuwata , gara kowa yayi lamarinsa kawai ,ta fad'i haka tana mikewa mama ta riko hannunta cikin nata ta sake kallon mama taga har lokacin ita take kallo tana murmushi wanda tasan na dole ne dan ƙoƙarin shawo kanta "a lokacin da ban samu haihuwarki a rayuwata ba, na shiga kuncin rayuwa da takurawar uwar miji ,wanda har lokacin dana haifeki kika girma wannan tsanar tana nan ba taje ko'ina ba, a lokacin ma'aruf shine .."
Mama dan Allah ki bar zancesa haka wallahi yana sani jin fad'uwar gaba tare da haddasa min mummunar ciwon kai mai tsanani,ko ba ma haka ba tarayyarmu dashi risky ne gaskiya ta k'arasa maganar tana zare hannunta cikin na mama ...
Mama ta girgiza kai kawai tana jin babu dadi a ranta ,ita kuma ummita ta langwa'be kanta gefe tamkar abar tausayi
"Shikenan jeki Allah yayiwa rayuwarki albarka ..."ameen mamana na gode, Allah ya rayamu tare kiga ya'ya na ....
"Ameen mama ta furta a kasan ranta tana lumshe ido, ita kaɗai tasan yadda take jin bakinciki rashin jituwar Ma'aruf da ummita, Allah ya sani tana matukar kaunarsa bata jin akwai abinda zai sa taji ta tsaneshi .....

Cike da sanyi jiki take saukowa tana taka step a hankali har ta iso garesa idanunshi na kanta ya kasa ɗauke idanunshi akanta ,wani sanyayyen dadi ne ya mamaye zuciyarsa ganinta kaɗai yana sanyashi jin farinciki mara misaltuwa ,har ta zauna nesa kaɗan dashi bai dauke idanunshi akanta ba "ina yini ya rayhan ?
Matsowa yayi sosai tamkar zai shige jikinta yace "Lafiya lau my princess me kike yi a sama tun d'azu nake zaman jiran gimbiya?

"Nothing kawai tace atakaice tana cizan lip's dinta na kasa, ya sauke naunauyen ajiyar zuciya sannan yace " my princess lokacin aurenmu ya kusa fa tunda aiki ya kankama ...

"dawa kenan lokacin auren naku yayi kusa ?
A matukar firgice qirjinshi na dokawa yace "wace irin magana ce wannan? dake mana, da zaki min wata irin tambaya?

Ta sauke numfashi da ajiyar zuciya a tare "gaskiya ni ya rayhan ba yanzu zanyi aure ba tukuna ,kai aure ma sai yadda hali yayi ......
yayi shiru yana Kallonta da tsantsar mamaki a saman fuskarshi yayinda ilahirin jikinsa ya ɗauki kyarma ,sake matsowa yayi sosai ya kamo hannayenta duka biyu cikin nasa yana cigaba da kallonta tana murmushin yake ...
"Haba me yasa zaki min haka ummita,bayan kinsa yadda nake sonki arayuwata ?
yayi maganar yana matse hannunta gam cikin nashi , runtse idanunta tayi saboda rad'ad'in data ji ya ratsa tafukan hannunta "wayyo hannuna ya rayhan "yayi saurin sakar mata hannu ya dafe kanshi da hannunsa ɗaya , can kuma ya tsura mata ido, yayi mata kallon second biyu sannan yace "zan jiraki har sanda zaki gama karatunki ,bazan takuraki ba har sai idan kece kika fahimtar dani ....
Still shiru tayi taki cewa komai ,ganin tayi shiru taki cewa komai yasa ya d'aura kanshi a gefen kafad'arta ,tana jin yadda zuciyarsa ke dokawa da karfin gaske...

"Subai'a shirunki na nufin abubuwa dayawa gareni ,zai fi dacewa ki buɗe bakinki ki min magana ,"zaki aure ni na jiraki har ki gama karatunki ko kuma na qara gaba ko Allah zai had'ani da wacce zata so ni?yayi maganar kamar zai yi kuka ..

Yanayin yadda yayi maganar yasa jikinta yin sanyi ,hankalinta ya tsananta tashi, zuciyarta ta cika da tausanyinsa , tabbass a soyayya idan akwai wanda ya dace taso kuma tayi rayuwa dashi to shine .....
Runtse idanunta tayi ,sai ga wasu tsiraran hawayen sun gangaro daga cikin idanunta , tausanyinsa yayi mugun kamata sosai , sam bata jin sonsa
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On WANNAN CE QADDARARMU
avatar
amina-4

11 months ago

Reply

Interesting novel

avatar
amina-4

11 months ago

Reply

Interesting novel

Please Login or Register in order to submit comment