Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

wannan bakin naki ?
ta maida kwallar data cika mata ido sannan ta sunkuyar da kanta cikin sanyi murya tace "inna kuwa tasan na haihu ?
Ya ɗan yi shiru " gaba-daya ya kasa bata amsar tambayar datayi , shi da akayi tambayar da ita mai tambayar sam babu kuzari attare dasu ahankali ya soma ƙoƙarin zare hannunsa cikin nata tayi saurin rikewa ,yayi shiru yana binta da kallo idanunsa har sun soma sauyawa daga farinciki zuwa bacin rai ,ya koma ya zauna suna fuskantar juna ya rasa me zai ce mata "ta san na haihuwa zuwa ne kawai bazatayi ta gani a inda ba na haifa ba ,na ɗauka haihuwar nan zai sa inna ta kaunace aranta amman shikennan babu komai ta saki hannunsa tana runtse idanunta tashi yayi ya bar d'akin dan ba zai juri ganinta cikin damuwa ba ..


Kwanansu hudu suka dawo gida mutanen unguwa dayawa sun shigo barka sai lokacin saudat tashigo tayi barka, mama ta amsa fuskarta a sake ko minti goma batayi ba ta wuce, da daddare sai ga aunty Salma tazo ganin jaririya ta ɗan dade suna barkwanci sannan tace tana zuwa , ta shiga bangaren hajiya inna faɗa tashiga yi ta inda take fita bata take shiga ba "ai wannan ya Ibrahim kike wa bakinciki inna ,dan shi zakiyi ban da maryam ba, itama me ta miki shekara kusan goma sha ana abu daya yakamata koma mene ne ya wuce an rigada an zama daya , can kuma ta koma rarrashinta kamar zatayi kuka "hajiya kiyi hakuri kije ki duba jaririyar nan bata yi miki komai ba laifin uwarta ai bazai shafeta ba ,da kyar aunty Salma ta tasa hajiya inna gaba suka je suka ga jaririyar da ko darajar ɗauka bata samu ba ,Abba na rawar jiki yaje zai dauko jaririya inna tace "barta tashi zanyi yanzu yana ƙoƙarin magana ta mike tayi waje ya girgiza kai sai da hawaye suka zubo masa "kayi hakuri yaya wannan lokacin bana kuka bane lokacin farinciki ne.
ana gobe suna abba yaje d'akin hajiya inna domin ta bada izinin sunan da za'a sakawa yarinya kamar yadda ta saba bawa sauran yan'uwansa umarni ,sai cewa tayi" kuje ku saka duk sunan da yayi muku amman banda sunana .......

Wani irin yanayi ya shiga mai wuyar misaltuwa ya dade zaune kafin daga baya ya mike ransa a matukar 'bace ya bar d'akin ,ranar suna yarinya taci sunan mahaifiyar Maryam subai'atu ..
Abba ya kashe kudi sosai haka dangin mairo sun nuna bajinta ,domin kuwa su nuna arziki haka abokan mutuncin da mama ke dasu na unguwa wanda sune suka rad'awa jaririya ummita sunyi hidima daita ..
Hajiya umma bata haihu ba sai data cika wata shadaya cif sannan ta haihuwa, kuma a gida kamar yadda tasaba haihuwarta yarinya taci amina ...

Ummita da ameena sun taso cikin kulawa da soyayyar mahaifinsu sun taso tamkar tagwaye ,kusan mama ke rainosu kwasam rashin lafiya ya kama ummita kowa yazo dubata ban da Hajiya inna Abba na kwance akan kujera rungume daita akirjinsa idanunsa a runtse yace "kowa yazo ya duba jikin ummita amman banda Inna, kiyayyar Inna ba'a kan Maryam kaɗai ya tsaya ba har akan yarinyar da bata san komai ba ya shafa.
rashin lafiyar ummita yasa mama ta fidda rai daita , ummita bata bacci ga yawon kuka numfashinta ya sha daukewa haka zasu rude ita da abba ,sai byn wani lokaci numfashin ya dawo ,atsakanin wannan lokacin mama ta rame sosai ta fita haiyacinta, wani lokacin haka zatayita kuka a daki ma'aruf da Usman suna rarrashinta ,yayinda ahankali tsanar ummita ke sake mamaye zuciyarsa, tun haihuwarta har zuwa yanzu mama bata huta ba, kullun daga wannan sai wanan,shi yasa kowa na rubbin daukar ummita Amman ban dashi , har ummita ta cika wata biyar da haihuwa bata da isasshen lafiya babu abinda hajiya inna bata ce ba "ai dole aga ba daidai ba tunda an tilasta Allah gurin neman haihuwa ayi dai mugani idan kalanzir zai yi tuyan kosai , sai da mama ta dangana da kasarta sannan ummita ta samu lafiya a gurin wani mai magani bayan an sage mata gefen bakinta tsagun da yayi mata maseefar kyau kasancewarta fara ..

watansu uku kamar bazata dawo ba sai data ga abban yayi fushi mai tsanani daita sannan ta soma zance komawarta ,
Rayhan na matukar son ummita kusan agurinta yake shiricewa sai ya kwashe lokaci mai tsawo yana tare daita wani lokacin sai dai mama tazo ta tarar sunyi bacci tare ummita na jikinsa ..

*****
Ahankali tsantsar kamanin ummita da mahaifinta ke sake fitowa , babu abinda ta dauko na mama sai farin fata banbancinsu da mahaifinta ita bata cika dariya ba saɓanin Abba dake da sakin fuska ga kowa, haka zalika kamar su ɗaya da ma'aruf hatta dimple da yanayin fuskarsu iri daya , shekarata ɗaya lokacin su ma'aruf suka cika shekara sha daya a duniya , aka fara yi mata shirin birthday din shekara daya dan lokacin tana tafiya har da gudunta ,Usman da rayhan sunyi murna sosai dan har gift suka kawo mata , amman banda ma'aruf wanda tsabar da miskilanci ke hanashi nuna farincikinsa akan komai, ummita na da burgewa da shiga rai kowa yana sonta Banda Inna da saudat tana yarda da kowa amman bada ma'aruf dan ko mama tasa ya d'auketa baya sakar mata fuska sanan baya wasa daita saɓanin Usman da rayhan ..
Lokacin da aka hallara domin birthday dinta kusan kowa yayi hotuna daita Amman Banda ma'aruf Dan yana d'aukarta ta saka kuka, yin duniya taki yarda dole ya sauketa cike da jin haushi tayi kyau sosai kowa yana son d'aukarta ita kuwa mama idan ka kalleta Bama zakace ta haihuwa ba dan babu abinda ya canza ajikinta mutane dayawa sun bawa ummita kyaututtuka ranar ummita tasha kuka saboda gajiya dan kowa nasan d'aukarta ..
Shekara ummita uku yanzu amman har lokacin mama bata sake samun ciki ba haka ma Hajiya umma bata da sai saudat ce ke haihuwarta mama ta godewa da Allah ɗaya bata guda dayan kuma tana yiwa waɗan da basu samu ba addu'a domin haihuwa rahma ce ,kace bari ma wani abu ne yafi ka zauna jugun a daki ..
*******
Dakin hajiya inna nan ne mattara hira , haka jikoki zasu cika dakin manya da kanana, duk lokacin da aka haɗu sai an san yadda ummita tayi kuka, sau tari idan za'a ta dawo mama daita zata ganta da kunburaren baki ko yakushi a fuska da sauransu ko ta tambayeta bata samun wani haske daga gareta dan tayi nauyin baki bata magana sai gwalangwancinsu na yara, yayinda meenal da saada abokan haihuwarta magana radau ,mama ta hana ummita zuwa d'akin inna bata son ana dukanta , amman haka ummita zata yita kuka ita abarta ,yanzu ma kuka take ita zata bi abbanta dake ƙoƙarin fita, amman mama sai kaucekauce take tana kokarin goyata ,Abba ya kalkeshe jikinsa a sanyaye ya janyo mama jikinshi ya rungumeta har ummita "kiyi hakuri ta kalleshi duk tayi kalar tausayi "kiyi hakuri da komai nasan duk ni ja komai dana makale lallai sai ke, ina sonki Maryan tamkar raina bazan iya rabuwa dake ba haka bazan taba canza uwa ba kuma ba zaki raba ummita da inna ba ,ummita jinita ce dole taso zuwa gurin inna ,ki bar min yarinya ta shawaginta cikin yan'uwanta a dakin Inna,kiyi addua Allah ya raya mana ita ,ahankaki ya saketa ya dauki ummita ya dake tsale tsalle ya sabata a kafadarsa ya nufi bangaren inna koda yashiga dakin cike da yara kasancewar weekend ce sunata tsalle tsallensu Hajiya inna na zaune ya sauke ummita ,aiko take tashige cikin yanuwanta, har gaban hajiya inna ya karasa suka gaisa ya dan zauna jin suna hira sannan ya tambayeta ko akwai abinda take so tace "a'a na gode allah yayiwa rayuwa albarka yayi mata sallama ya fita ya bar ummita ..

Two friend's (bsbs)

💗💗💗💗💗💗
WANNAN CE
QADDARARMU
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

~TRUE LIFE STORY~

FREE NOVEL NOT FOR SELL


AL'QALUMAN



*AYSHA A BAGUDO*
*FAIZA HAMMADU*


~DEDICATED TO~
*AUNTY ZEEY MAMAMMU MAMAR MAI DAMBU , ALLAH YA BAR MANA KE MUNA SONKI FI SABILILLAH*


PAGE 17

........a d'akin Inna ummita ta yini ko abinci a nan taci cikin yara y'an'uwanta duk da irin kyara da kora da halin da inna ke mata hakan bai sa ta bar d'akin ba, ta makale abunka ga yaro sai dai duk a tsorace take da inna tayi magana take firgita daga karshe sai faɗa tsakanin ummita da sa'ada akan bebin roba , sa'ada ta kwace abunta ba sai dambe ya kaure atsakaninsu ba saboda ummita taki yarda ta bata bebinta ummita har da cizo saboda jin zafin dukan da Sa'ada tayi mata ,nan sa'ada ta rufe ummita da duka tana kuka , aka rabasu, ummita ta makale kafad'a ala dole sai ta rama tana kuka, rayhan ya shigo d'akin bai tsaya jin dalilin kukanta ba ya rama mata tare da d'aukarta ya saɓa a kafad'arsa yana rarrashinta, amman still tace sai ta sauka ta rama.
"kai rayhan fita daga idona dan me zaka daki Sa'ada akan wannan jairan tarinyar mai fadan rashin gaskiya "haba inna baki ga ba karfinsu ɗaya ba kuma ai Sa'ada tafi dukanta guda nawa jikin ummita yake ?
"Ban sani ba mara sanin ciwon kai ,ga jininka amman dan shishigi kake makelewa wannan abar "itama jinina ce kamar yadda Sa'ada take"

" Yi min shiru kuma ka fitar da yarinyar nan mai kai kamar na maciji daga dakina , yarinya sai jarabar kukan tsiya idan an barki daita iya mata zakiyi ? Cikin fushi ya juya ya fito daga d'akin ya kai wa mama ita tana kuka , mama ba tace komai ba ta karb'eta dan tasan za'a rina , tayi mata wanka tana rarrashinta daga nan sai bacci .


sannu ahankali suna girma kyawun ummita na sake fitowa sosai , duk tafi jikokin hajiya inna kyau , batun so a tsakanin inna da ummita babu shi dan gaba-daya tafi son ma'aruf acikin jikokinta , saboda me sunan babanta ne, sai kuma ya'yan saudat , zata iya hana kowa abu ta basu numfashinta ne kawai bazata iya cirewa ta basu ba ,Inna na son yaran fiyye da komai sai gashi Allah ya jarabi yaran saudat guda biyu da rashin jin magana da shaye shaye ga sata kamar me , malik da sadam babu abinda zasu gani matukar za'a siya to zasu ɗauka suje su siyar suyi shaye shayensu dashi ,ga rigima kamar me , da anji ihu a waje ba'a tsaya wa tambaya an san dasu ne hajiya inna da saudat babu Allah aransu suka lakawa mama cewar itace tayi musu asiri , da yarda Allah sai sharrinta ya koma kanta da yarta ..
Ita dai mama bata tanka musu ba , sai addu'a da tayi musu da itama sun sha mata satar shiru kawai take saboda gudun maganar hajiya inna .

*****
Ma'aruf yana bacci a d'akinsa ya dinga jin hayaniya da ihu , sai ya farka ya fito, yana fitowa sai yaga faɗa ake yi da sadam da wani yaro har anji masa ciwo duk jama'a unguwa sun fito suna ta kallo,masu zagi nayi masu addu'ar Allah yashirya sunayi, shi kuma daman irin wannan fad'ace fad'acen bata masa rai yake saboda baya son hayaniya, kawai yaje ya nemi guri yayi zamansa akan banci yayi tagumi yana kallonsu , hatta Malik kallonsu yake yana dariya dan dama basa shiri da sadam kusan dai yadda 'yan shaye shaye ke yi , da kyar aka samu aka raba faɗan , gashi inna da Hajiya saudat basa nan sai da suka dawo suka samu labari Hajiya saudat taje ta kai yaron da sadam ya jiwa ciwo da kwalba chemis domin ayi masa treatment, tana dawo kawai sai sautin muryar hajiya saudat yaji tana cewa "ma'aruf ana faɗa da ɗan uwanka dan rashin so shine ka zauna kana kallo ,da an kasheshi ma babu abinda zaka ce har da wani harde hannu....
abun yayi matukar bawa maaruf dariya Amman da yake miskili ne sai ya dake yaki yin dariya , sai rayhan daya zame masa dole ai ya tafi da gudu ya rabasu lokacin da aka d'auko katakobi za'a buga ma sadam abun yayi matukar bashi mamaki yaga bata nan lokacin da abun ya faru, muryarsa a da ke yace " waye ya faɗa miki ina nan ?
"Ya fad'i haka saboda ya samu damar cin uban ko waye , babu kunya ba tsoron Allah tace "ummita sannan ta juya ta shige ciki .

"Yayi shiru yana tunani yarinyar da ko magana kirki bata fiyye , sai dai bayi mamaki jin haka ba saboda ya ga ummita agurin lokacin da'ake faɗa yana kallonta ita da sa'ada sannan ya ganta lokacin da hajiya saude ta dawo suna magana , amman yayi mamakin yadda har ta iya munafurci haka hjy saudat na gama shigewa cikin gida , sai grama tazo ta sameshi " na gode babana Allah ya saka da alkhairi Allah ya bar zumunci ana faɗa da d'anuwanka shine ko ka shiga, ko kallon inda take bai yi ba ya shigo cikin gida yana ciccin magani yana dube duben inda zai ga ummita bai ganta ba dan haka yayi wanka ya fita,yana dawowa da ummita ya soma cin karo daita mari biyu yayi mata masu da kyau a gigice tayi d'akinsu tana kuka mama ta tambayeta "maaru ne ta faɗa tana kuka mama najin haka bata sake cewa komai ba ta koma kitchen tacigaba da aikinta..

ummita ta taso shiru shiru ba kamar meenal ba , batada wayon magana sai tsiwa , sai dai a ɗan girmanta Allah ya jarabeta da rashin jin magana mai tsanani itama ga yawo kamar wacce taci kafar kare daga school ne makarantar islamiyya yawon ya ciyota zata je abunta hankalin kwance , abu kamar wacce akayiwa asiri , domin sometime ko anje nemota sai dai a sameta ita kaɗai duk yara sun watse sun barta tana wasa, zata iya kaiwa har dare tana wasan kasa , ko abinci bata damu dashi ba kamar yadda ta damu da wasa , duk da wannan jarabawar da Allah yayi mata na yawo Allah bai barta haka ba , ya wadatata da tarin ilimin boko da Arabic ..wannan yawon shine abinda yafi komai d'agawa hajiya mama hankali da masoyanta , akwai lokacin data wuce yawo daga school akayi neman duniya ba'a ganta ba sai a bakin jobade hotel ma'aruf yayi nasarar ganinta, aiko tun daga can ya dinga dukanta yana ball da ita ,tasha zagi iri iri rana shegiya biri mai fuskar zaki wanda zaki kashe kike nema kece zaki mutu ki bar mana fat lion kawai , sai da yaji mata ciwo tukunnah ya kawota gida ..

tunda ummita take yawonta babu wanda ya taba dukanta sai ma'aruf , aikuwa ranar inna kamar tayi yaya dan dadi albarka kam ya sha daga karshe reshe ya juye da mujiya , dan zageta yayi tatasss , har sai daya sha mari gurin injiniya ,
kwana ummita tayi da zazzaɓi saboda dukan da taci agurin ma'aruf, mama kuka ummita shesheka kuka tana rungumeta ajikin mama jikinta yayi zafi sosai mama kasa runtsawa tayi tana tofeta da addu'a ...

ma'aruf ya kasa ya tsare akan ummita duk saboda mama, dan baya jin dadin ganin yadda yake ganinta cikin damuwa ,da zarar yaga ummita a waje zai korota gida , haka Usman da rayhan wanda su lalla'bata suke da rarrashi ta daina zuwa yawo ..

wasa wasa sanadiyyar dukan da ma'aruf ke ma ummita ya jawo rashin shakuwa a tsakanin ummita da ma'aruf daman shi bai damu da yara bane , da wuya ka ganshi rike da yaro ko yana wasa da yaro ..

Da kyar ummita ta daina yawo da taimakon allah da addu'r mahaifiyarta , sai kuma ta dawo mai shegen tsokanan bala'i , wata rana aunty Aysha diyar aunty Salma tace Suzu su rakata oshodi siyan ankon bikin kawarta ita da Khadeeja , bayan sun shiga mota , karen mota yace su bada kudi ummita tace kar aunty Aysha ta bayar sai sun sauka kafin su sauka ta kwace kudin motar a hannun aunty Aysha ta rike gam a hannuta , basu K'arasa inda zasu sauka ba direban ya juya kan motar yace kowa ya sauka anan , tayi murmushin tace "kin gani aunty daman nasan haka zasu yi , suka sauka , karen mota ya miko hannu ta bayar da kuɗi ,ta mika masa rabi kudi , aiko take karen mota yace bazai amsa rabi ba , ita kuma tace" bazata bashi duka kudin ba tunda bai kawosu inda zasu sauka ba yana zaginta tana ramawa sauran yanuwata suna ta hanata amma in taki , har abun ya zama bala'i ta nemi guduwa karen mota ya janyo hijabinta zai kai mata naushi, sa'ada tayi saurin riko hannunsa aiko naushin ya sauka akan idanunta , ita kuma ummita ta arce ta gudu basu sake ganinta ba sai da suka dawo gida , nan kuma bala'i ya kaure atsakanin har da dambe , sa'ada Khadeeja da ummita case har gurin injiniya da kyar ya sasantasu, lokacin dukkansu basu wuce shekara sha biyu ba, yayinda su ma'aruf suke shekara a shirin da uku ..

idan kuwa ummita taga Khadeeja ko meenal ko sa'ada sunyi shiri daban ko to match yanzu ne zata soma zaginsu ,ko islamiyya haka take da sakawa mutane suna kuma duk wanda ta saka wa suna zai bishi , idan suka sakamata an dinga bala'i kenan, idan tasa maka suna toh ya zauna kenan dan ko zaka mutu sai suna ya bika , dan dashi zata dinga kiranka dashi , ita kuma ba'a isa a kasa mata ba , meenal da ummita suna tsaye da wasu yan makarantarsu guda biyu a kofar gida sai ga raliya makwafciyarsu ta sha kwaliya sosai ,ummita tayi mata kallon sama da kasa " raliya yau to match kikasa haka lallai kan mage ya sake waye an yi wanka, wanka yabi jiki Allah yasa a d'ore ..

Cikin haka sai ga Khadeeja ta fito , ahankali idanun ummita
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On WANNAN CE QADDARARMU
avatar
amina-4

11 months ago

Reply

Interesting novel

avatar
amina-4

11 months ago

Reply

Interesting novel

Please Login or Register in order to submit comment