Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

rawa yake tsabar fargaba ,bayan fitarta Hajiya inna ta dubi mama "tam dagin agumawa kul kar naji kar na gani ,kar wani abu ya samu jikin jikin fatimatu dan nasan halinku da mugun asiri tana cikin fadar abinda ta gama ma'aruf ya fito daga cikin uwar d'akan mama "wai ke inna meye haka ne ?
"Kullun baki da abun zaki da aibun tawa sai mama me ta miki tun ba'a haifemu ba kike musguna mata har bisa ga yanzu ni fa wannan hayaniyar tana damun kwakwaluwata , wallahi idan kika sake zaginta zan gudu na bar gidan dan ihunki na damuna ..
inna tayi sororo tana kallon ma'aruf da bai wuce shekaru tara a duniya ba "ai bazan damu ba ko dukana kayi akan wannan abar ba , saboda daga kai har uwarka bakwa cikin hankalinku ,an rigada anyi muku asiri sai yadda akayi daku ..
Ransa a bace ya k'araso gaban inna ya rike mata hannu .ya shiga janta da iyakacin karfinshi "ki bar mana dakin mammamu Usman zo ka tayani mu fitar da wannan matar har usman ya mike mama tayi saurin kamo shi ta rungumeshi ajikinta zuciyarta na kuna da bugawa da karfi .
"Usman kazo mana ya sake faɗa yana cigaba da jan inna "ai nan ba d'akinku bane baba , ga uwarka ce wannan matar ba uwarka bace, ban da sharrin asiri me zai sa mutun yayi kyauta dansa , kalli can ka gani ta nuna masa jikin bango makeken hoton mahaifinsa ne ajiki "wannan shine mahaifinka hannuta ya sake yashiga kallon mama kafin daga baya ya karaso gurinta ya durkusa agaban yaana kallon fuskarta "mama wai ba kece kika haifeni ba ?
Mama tayi shiru ta kasa furta komai dan bata san mai zata faɗa masa ba , "Kece mamammu ni da usman idan bake bace wacece mamana da Usman ,kece kike mana wanka abinci da komai "makira kinyi shiru kina kina ji yana tambayarki ki faɗa masa gaskiya yasan uwarsa , yasan ba kece uwarsa ba ki faɗa masa ke baki da azirkin haihuwa sai mulmula kashi inna ta fadi haka tana dagawa mama tsawa , mama bata san sanda tace "eh bani ce na haifeka ba Hajiya umma ce wsnnan kuma shine mahaifinka ta nuna masa hoton da inna ta nuna masa ...

"yauwa kaji gaskiya yaro dan haka ka daina zakewa ,ma'aruf ya daura kanshi bisa gwaiwar mama "ina sonki mama koda bakece kika kawoni duniya ba ,bare kece mamana ki zo mugu garinku mu bar inna gidan nan ta fiyye bala'i mama tayi saurin rufe masa baki tana girgiza masa kai "aikin banza a haka zaki kare kina wannan kukan naki mara amfani ,kai kuma da kake cewa a gudu kai taɓa ganin zata wancan garin nasu taje da kai sai dai taje da wannan mai idanuwan kamar kifin cikin ruwa saboda shine dolenta ? dan haka daga yau ka sanyawa zuciyarka kai ɗan aro ne gareta ba dan cikinta ba ,dan aro kuwa baya taɓa zama naka tana gama faɗar haka
ta sanya kai ta fice daga d'akin , ranar wuni mama tayi cikin damuwa da kuka ma'aruf da Usman suna rarrashint "tabbas tasan mutanen garin su na asiri amman ita bata san ma a ina akeyi ba, kuma ko tasani zuciyarta bata da muradin cutar da wani daga cikin ahlin Ibrahim ..
Duk inda tayi ma'aruf na biye daita yana bata hakuri "mamana karki damu ki daina kuka idan na girma zan kwatar miki yancinki agurin inna har ma da mamansu rayhan ,bazan sake barin kowa ya takaki ba ,kinji mamana ki daina kuka ya janyo rigarsa yana goge mata hawayen dake zuba a idanunta ta rungumeshi ajikinta tsam "na gode d'ana Allah yayi maka albarka tana son ma'aruf sosai fiyye da Usman tana jin ko dan cikinta bazata yiwa son datake masa ba ....

Bangaren hajiya umma kuwa wannan tashin hankalin da buguwar zuciya da wuni ciki yasa zazzaɓi mai zafi ya rufeta , kwanata biyu tana fama da zazzabi daga karshe sai bleeding , abu kamar wasa sai da aka
danganata da hospital, ai Inna najin batun jini kawai ta daura hannuwanta duka bisa kai ta rushe da kuka "shikennan wannan diyar agumawar ta zubar min da ɗan Ibrahim ,zagi tsinuwa babu wanda hajiya inna batayiwa mama ba, tayi rantsuwa sai mama tabar gidan matukar cikin jikin ummah ya fita , da kyar dai likitoci suka tsaida jini , satin Hajiya umma daya a hospital sannan aka sallamita Hajiya mama kasa zuwa dubo umma tayi saboda tsoron jarabar inna sai dai ta tura ma'aruf yafi sau babu adadi ..
bata san dangin Abba na tsananin son ganin jikinsa a doron duniya ba sai da hajiya umma ta samu ciki ,sai tururuwan zuwa dubiya suke , shima kuwa Abba sai farinciki yake , tana jin zafin yadda abba ya dan sauya mata akan cikin jikin hajiya umma da bai wuce na wata biyu ba amman ta danne taki nuna masa ko a fuskarta sannan ba daina duk abinda take masa ba ..

******
Rukkaya aminiyar mama ce tun farkon kawo mama kasar ,sun shaku sosai itama bata taɓa haihuwa ba alokacin da'akawo mama ,sai daga baya akayi mata hanya gurin wani mai magani a ijoko sugar dake tsakanin ogun state , cikin yarda Allah ta dace dan Allah ya albarkaci da samun diya mace , shine ta til'asta mama da suje ta kaita ko zasu dace amman taki amincewa ,dan haka rukkaya taje mata da kanta ta amso mata magani , da kyar mama ta amshi magani dan cike take da tsoron abinda zai faru inna taga shigowar rukkaya dan bata kaunar ganin wani yazo gurinta ,mama ta soma shan maganinta da aminiyarta ta amso mata sai dai maganin akwai shegen yauki kamar kubewa , da maseefar daci duk lokacin da zata sha sai tashiga tashin hankali amatsayinta na dalibar likitanci tasan ko cikin ma tasamu maganin zai iya barar da ciki ...
Tayiwa rukkaya complain akan maganin "ki cigaba da sha haka maganin yake dacinsa bai hana ki samu idan da rabo ..

hajiya mama ta cigaba da shan maganinta tana kula da Usman da ma'aruf da suka zame mata sanyi idanunta ,kowa ya gansu sai yayi sha'awarsa saboda kulawar da suke samu da gata daga gareta , bata barin yi aikin komai komai ita ke yin kayanta hatta wanka a shekarunsu tara itace ke yi musu a cewarta ko sunyi da kansu ba fita suke yi ba , ganinsu yasa rayhan shima ke makalewa d'akinta ,bata koreshi sai ma janshi ajikinta da take , sai dai idan uwarsa ce tazo ta tasa keyarsa gaba wannan kuma babu yadda zata yi ,ita dai ido ne nata ..

Cikin haka malam na ijoko yace lallai sai an zo da mai shan magani gurinsa saboda akwai hadin da za'a mata kuma dole sai anan zata ci agabansa , mama ta rasa wacce karya zatayi tabi rukkaya suje ,kawai dabara tazo mata tace wa Abba zata garin su tunda duk kusan hanya daya ne, idan taje daga can ta karasa garinsu tayi kwana biyu ta fadawa Abba bai ki ba yace sai ta dawo tare da bata makudan kudi ta haɗa kayan Usman dana ma'aruf duk da tasan da wuya Hajiya inna ta bari dan duk zuwa bata yarda, haka zai karaci kukansa amman bazata bari ba ,abinda tayi tunani shine ya faru dan kuwa hanawa tayi ,Dole ta cire kayansa tana shirin wucewa tace "kema bazaki ko'ina ba dan ban yarda dake ba, zuwa zakiyi kiyi asirin da za'a cire cikin jikin umma , idan kuma kikaje wallahil azim abakacin aurenki da Ibrahim matukar ni na kawo Ibrahim duniya sai ya sakeki idan kika fita, ai bazaki sake fita kije wancan garin naku ba sai fatimatu ta sauka lafiya yar masu mugun halin tsiya wannan lokacin mama na jin tamakar ta biyewa hajiya inna ta faɗa mata son ranta amman bazata iya ba ,bata taso cikin irin wannan rayuwar ba, su sam agarinsu baa zagin babba , ijunansu ma girmama juna suke bare Hajiya inna da ta kasance uwar mijinta ai ko a garinsu akaji ta zageta sai an tsine mata .....

Komawa tayi d'akinta tayi zamanta tare da zabga tagumi har dare lokacin da Abba ya dawo ,yayi mamakin ganinta "baku tafi bane ?
"Inna ta hana ta bashi amsa tana sauke naunauyen ajiyar zuciya ,yayi shiru tare da tsareta da idanu ya kasa gane dalilin dayasa inna take masa haka , yayita bata hakuri "kiyi min hakuri Maryam duk laifina ne ,nine nayi silar komai ,amman kuma nima bani da dabara da "QADDARAMU" dole sai mun kasance a inuwa daya wallahi ban d'auko ki dan na kuntata miki ba ,ki min hakuri ki tayani yiwa mahaifiyata biyayya , dan mu rabu lafiya daita "Ni kuma na dangwama cikin damuwa da bakinciki kensn ?
ta furta haka tana kallonsa "shima kallonta yake saboda wannan shine karo na farko da ta furta wani abu makamanci ta soma gajiya ,ya riko hannayenta duka ya sake tsareta da idanu gbdy ya rasa dalilin da yasa tayi masa tambayar,ya d'ago habarta ya haɗa da nashi "kiyi hakuri "nasani akwai gajiya ni yanzu ko cewa kikayi kin gaji dani bazan ga laifinki ba saboda kinyi hakuri dani iya hakuri , amman rabuwa dake zai sa na dangwama cikin bakincikin rayuwa saboda sonki a jinina yake dan ......
tayi saurin mikewa dan bata son jin abinda zai sake faɗa , tasan yana sonta amman akwanakin nan ya sauya sosai d'akinta ta shige ya biyota , yana sake bata hakuri tana kokarin zubewa kan bed tana kuka yasa hannunsa ya rikota yana dukan bayanta yana bata hakuri ,ki bari muyi baccinmu Kinga yara har sunyi kuka take sosai tana jin kamar ta mutu shi kuma yana bata hakuri har sai datace ta hakura sannan ya barta ya cire kayansa ya kwantar daita ya kwanta abayanta ya rungumeta ranar ko abinci bai ci ba haka ko bangaren umma bai shiga ba .. ..


Cikin Hajiya umma nada wata uku ,mama ta fahimci tana da ciki sakamakon rashin ganin al'adar ta kimanin wata uku dan tun kafin tasoma shan magani amman ta share duk da tun zuwanta bata taɓa batan wata ba sai a wannan watannin baya zuwa wannan lokacin sai take ganin kamar ba gasky bane ..

ta cigaba da rayuwarta sannu ahankali cikin mata na girma da tsine na mama na bajewa da bin jiki ,zuwa lokacin sosai ta fahimci ciki gareta tayi kuka tayi murna ta godewa Allah, da tayi azumi tayi sadaka a danginta babu wanda bai san da samuwar cikin ba ,mota guda sukayi har mahaifinta suka zo dubata sai dai sun kama bakinsu sun yi shiru basu nuna wata alamar abinda ya kawosu ba .. dangin Abba kuwa gaba-daya hankalinsu na kan cikin hajiya Ummu yadda ake boye hajiya umma haka itama take boye cikinta , hatta mai cikin bata bari ya sani ba lokacin dai yaga ta kara kiba tayi kyau ,bayan wasu yan kuraje da suka fito mata a fuskarta babu wata alamar da zaka gane ciki gareta Amman sai da Abba ya dan fahimci wani abu yana cin abinci ya dubeta "ni kuwa maman yara sai nake kallon mai shigar ciki ko ma nace mai ciki ?
Murmushi tayi tare da cewa "Allah yasa hakan ta faru "ameen ina tsananin son naga kin haifa ko daya ne ,cikin jikin hajiya umma ina jin ina ma kece ke dauke dashi "
"Karka damu lokaci dai Allah ya raba duk wata mai dauke da ciki lafiya ..yace "ammen ki ƙara hakuri akan wanda kike dashi ina sonki ina son na kasance dake har karshen numfashina ,a aljanna ki zamo uwargidana malamai dai masu sanyi da kwantar da rai ya dinga furta mata yana janta da hira ...


Two friend's (baba)

💗💗💗💗💗💗
WANNAN CE
QADDARARMU
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

~TRUE LIFE STORY~

FREE NOVEL NOT FOR SELL


AL'QALUMAN



*AYSHA A BAGUDO*
*FAIZA HAMMADU*


~DEDICATED TO~
*RAMLAT MANGA ABOKIYAR SHAWARA, ALLAH YA BARMU TARE ALLAH RAYAMANA MUWADDAH SON SO FI SABILILLAH*

WATTPAD @HAUESH

bismillahirrahmanirrahim


PAGE 16

.....kwasam hajiya inna tazo da tsirfan wani sabon salo, wai abba ba zai sake kwana a bangaren mama ba , bisa hujjarta ta mama bata haihuwa, dan me zai dinga hasarar spam d'insa a inda bai da amfani ,lokaci data fadi haka babu wanda bai girgiza ba ,sannan babu wanda bai ji kunyar maganar ba ,daga yau na kashe maka kwana a wancan d'akin sai dai ka tattara ka koma kwana a d'akin fatima, zai yi magana "no ibrahim don't say anything .... mama saurin fadar haka yin maganar cikin harshen turanci "babu komai inna yaje can din ya cigaba da kwana ita ai tafi bukatarsa kuma dana da can duk daya ne "ko baki ce ba kinibabba , ba zai sake kwana ba ,daga Hajiya umma har Abba basu so wannan tsarin ba, shiyasa duk suka shiga damuwa sannan babu wata mu'amula data sake shiga tsakaninsu, a qalla sai da suka ɗauki wata biyu suna cikin wannan damuwar batare da kowa ya sani ba suna neman mafuta daga Allah , yayinda ita mama ko ajikinta sha'anin gabanta kawai take dan bakincikinta ragu sosai ,a lokacin jin zuciyarta take cike da farinciki , bata jin damuwar komai duk abinda take so iyayenta suna mata , sakonsu kullun yana tafe sannan kafa bata yankewa daga gurin daginta ,idan wannan bai zo ya dubata lafiyarta ba, wannan zai zo ,sai dai idan sun zo inna tayi ta zage zagen ana yi musu zariya a gida ,sam inna bata son ana zuwa gurin mama tafi son ta ganta ita kaɗai cikin damuwa ,haka ta bangaren rukkaya da ma'aruf suna kwantarwa mata da hankali , kusan lokacin ma'aruf ke yiwa mata komai duk tana kokarin hanashi amman baya yarda, sai yace"ai shima ya girma yanzu ba zata sake yin aiki ba , da zarar ya dawo daga makaranta baya zuwa ko'ina yana makale da mama, duk mai son ganinsa sai dai ya biyosa bangaren mama ,mama naji dadinsa sosai , a wasu lokutan tana addu'a ta haifi diya mace ta bawa ma'aruf aurenta idan hajiya inna da danginta basu hana ba ......


Cikin haka injiniya ya samu labarin halin da'ake ciki ai kuwa shi da aunty Salma suka rufe ido suka ki bin bayan karya , suka yiwa inna tatas dan basu fiyye shakkarta ba, barin ma idan sun san bata da gaskiya , hatta baba sarki sai daya shiga cikin maganar sannan Abba ya dawo d'akin mama da kwana alokacin da cikin mama na wata tara Hajiya umma kuma tana wata goma haihuwar ce dai har lokacin shiru babu labari ..

da murnarsa da komai ya shiga d'akin mama kawai yaganta tana tsugunne tana murkususu rike da ciki da sauri ya K'arasa gareta yana kiran sunanta "Maryam! Maryam !! lafiyarki meke damunki?
"ai ko gama rufe bakinsa bai yi ba sai yaga kamar nakuda take . ...
Tsayawa yayi cak cike da matsanancin firgici da tashin hankali ya Daskarewa a tsaye yana sake kallonta cike da mamaki ,mafarki yake ko kuma gaske ne abinda yaga yana ƙoƙarin faruwa agabansa ...?
Cigaba yayi da kallonta ,"yaushe tayi cikin da har zata haihu ? Yayi wa kanshi tambayar idanunsa na tsaye kyam akanta ya kasa karasawa gareta haka ya kasa daina kallonta ..

Sunanshi data kira a galabaice yasa yayi saurin dawowa haiyacinsa gabad'aya ya rasa me ya kamata yayi a lokacin Kawai ya juya zai fita "bari naje na kira uwar marayu ya fita ,da kallo mama ta bishi tana ciza lip's dinta , koda ya shiga d'akin Umma kallonsa take saboda jikinsa da taga yana rawa gashi ya kasa magana illa hannunta daya riƙo cikin nashi sai dakin hajiya mama , a yadda ya barta a haka ya dawo ya sameta tana jujjuya kai , ita kanta umma mamaki tayi , sai dai tafi shi karfin hali ,dan tuni ita takarasa gareta tare da dafata " ikon Allah haihuwa ce nan ta kamota shima ya rikota , ahankali ta furta ga jakar kayan baby can ......
wani sabon mamaki, kenan ita ta gama shirinta na haihuwa, kai tsaye sai asibitin, suna zuwa akayi labour room daita tare da tambayar kayan haihu Hajiya umma ta mika musu karamin akwati ,ciwo kamar jira yake azo hospital sai nakuda zanga-zanga amman baby shiru, sai baby yayi kamar zai tawo sai ya koma yayi zamansa ,iya wuya mama tasha kwanata daya tana cikin wannan halin tun tana kuka ta dawo bata iya komai tace "Ibrahim ka kira min iyayena mutuwa zanyi , babu abinda take iya faɗa sai sunan iyayenta, tsoro ya kamashi kar azo wani abu ya faru daita ya shiga uku ,dan ko numfashi bata iya yi sosai , dan haka ya kirasu , jirgi suka biyo suka zo hankalinsu ya tashi matuka sai dai basu da yadda zasuyi sai addu'a gaba-daya suka tattara hankalinsu akan halin da diyarsu take ,wasu dagan cikin yan'uwa sun zo, amman daga saudat har inna babu wanda yazo suna gida abunsu , hankalin ma'aruf yayi mugun tashi , kasa komai yayi sai kuka yake yana addu'a akan Allah ya raba mamansa da cikin lafiya, ya shiga d'akinsa ya dauko bakinsa da yake ajiya kudi ,ya fasa ya je ya tsiyo sweet ya dinga rabawa yara da niyyar Allah yasa ,ya sake ganin mama arayuwarsa ,duk wanda ya bawa sadakar sai yace kace Allah ya sauki mamana lafiya ,idan baka faɗa ba ya kwace sweet d'insa ya bawa wani , akwana na biyu likitoci suka ce dole sai dai ayi mata aiki ,batare da bata lokaci ba Abba yasa hannu akayiwa mama cs, aka ciro mata kyakkyawar baby girl fara sol tamkar uwarta ,daga hajiya umma da Abba har su ma'aruf babu wanda yabi ta kan baby dan shi ,tun wahalar daya ga mama na sha , yaji ya tsani baby ,dan baya son abinda zai taba masa mamansa .....

Har dare babu wanda yazo daga inna har saudat gara ma saudat mutane basu ga wani laifinta ba , saboda itama jego take , amman duk da haka sai da injiniya ya tambayeta ko taje , tace taje shi kuma bai tsaya tambayar ko tazo ba...

****"
washegari ranar Abba ya shigo d'akin da mama take kwance ya zuba mata ido shi kaɗai yasan yadda yake jin kanshi a halin yanzu tsantsar kaunarta da tausayinta ne suka sake haɗe masa guri daga , ya ciro hancky daga a gaban aljihunsa ya goge hawayen da suka zo masa , tsawon lokaci yana zaune yana kallonta sannan ya tashi ya bar d'akin yana jin ciwon abinda inna tayi masa , har lokacin babu wanda yabi ta kan baby kawai farkawar mama suke son gani .
sai bayan da mama ta dawo daidai sannan Abba ya samu damar daukar jaririya ya dade yana kallonta yana jin dadi da farinciki yana murmushi har sujjada yayi , itama Hajiya umma tayi murna ta amshi baby tana mata addu'a, rayhan da Usman sunfi kowa zakewa gurin kallon baby Banda ma'aruf da har lokacin bai ɗauketa ba, asalima ko kallon inda take baiyi ba ....yana makale da mama kamar yadda Abba ke makale daita .

ranar asabar dayawa daga cikin dangin mama sun zo amman hakan bai sa Abba ya daga kafa ba yana nan manne daita yana sakar mata murmushi ..itama murmushi take tana kallonsa , tunda akayi aikin cikin Sa'a iyayenta suka koma ,kafin mahaifinta ya wuce ya sakar musu kudi sosai yace a kula da mama da babynta shiru mama tayi tana dubansa ta ɗan motsa bakinta sai kuma tayi shiru ya kalleta sannan yaje ya ajiye baby a gadon jarirai ya dawo ya rike hannuta "me kike son ki faɗa naga kamar akwai Magana acikin
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On WANNAN CE QADDARARMU
avatar
amina-4

11 months ago

Reply

Interesting novel

avatar
amina-4

11 months ago

Reply

Interesting novel

Please Login or Register in order to submit comment