Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

masa dakin cikin zafin nama ya damkota yayi kan bed daita "ki bari mushirya cikin girma da arziki ya faɗa yana ƙoƙarin zare rigar jikinta ta rike rigar gam "banason abinda kake min ya narke mata ajiki "haba qauna kece fa duniyata hasken zuciyata taurawa a zuciyar mah'ruf kiyi hakuri ,kinsan kowa da irin kishinsa ido nane ya rufe ki taimakeni yana magana yana sama da rigarta har ya samu nasarar zareta ya mannata da jikinsa nan take mazantakarsa ta motsa ya soma shafa jikinta kasancewa tare daita ya dauke masa damuwarsa take zuciyar ummita tayi sanyi ya haɗe fuskarsu guri daya yana busa masa numfashinsa hannuwanta duka ta kai fuskarsa tana shafowa ta haɗe bakinsu kamar wani mayunwacin zaki ya cafki bakinta ya shiga tsotsa yana aika mata da zafafan wasaninsa yana fitar da numfashi gabadaya ya dimauce ya gigice suka fita daga haiyacinssu ya daina ganin komai ya daina jin komai sai shafata yake, ita kuwa kwakwaran motsi ma ta kasa duk da bata jin karfin jikinta haka ta biye masa ta kwantar da kanta a kirjinsa sannu a hankali da rarrashi da kalaman soyayyaya ya ɗauke mata hankali suka lula duniyar ma'aurata daren ranar hajiya rahma ta fita tsirara kamar yadda bokanta na ijaye ya bata asirin ba ita ta dawo gida ba sai daf da asuba jikinta yayi rudu rudu da cizon sauro kai tsaye wanka tashiga ta zira doguwar riga ta kwanta ba maganar sallah,ita kanta suhaima ta tausaya mata tana jinjinawa yayartasu ta dauko man zafi ta shafa mata ajiki tana mammatsa mata har bacci ya ɗauketa , kullum mah'ruf yana tare da ummita yayinda suhaima ke can gidan hajiya rahma da zumar sati na cika zata tattara ta koma gida bayan kwana uku hajiya rahma taga babu aikin daya ci acikin ayyukan da bokayenta suka bata tunda gashi har lokacin babu wani cigaba dole sai an dangana da kotu dan haka ta shirya tayi sallama da suhaima da yaranta ta tattara sai gidan boka na isheri , tana zuwa gidan yayi murmushi har jajayen hakoransa suka bayyana ya lashe labensa daman ya dade yana sha'awar hajiya rahma cikin kaukausar muryarsa mara dadin sauraro yace "duk kin gama yawace yawancenki ? "Lallai ramota da yake haka yake kiranta kamar baki gama sanina ba ,"ai duk aikin dana amsa duk inda zaki sai kin dawo gareni.....

Ta gyada kai tana kallonsa da kwayar idanunta sannan tace "na matsu ne ina jin bakinciki halin da yar'uwata take ciki gashi anki barin mu ganta ga mahaifina ya kwanta rashin lafiya sanadiyyar tana hannu ma'aikata yanzu dai asan yadda za'a yi gani nazo ya baza ido akanta yaki kiftawa hakan yasa taji wani iri ajikinta gabanta ya shiga faduwa wanda bata taɓa jin irinsa ba "tashi muje a soma aiki ya mike ya itama ta mike yana tafiya tana biye dashi su dan yi tafiya mai nesa daga dakin da yake aiki suka isa wani daki ya shiga itama ta shiga ya dauki kwayar tsafi ya soma magana da tsaface tsafacensa yana kur'ban ruwan dake cikin kwaryar yana busa mata ajiki take taji ilahirin jikinta sun mace kanta ya soma juyawa ta soma cire kayan jikinta da kanta ta isa garesa ta rungumeshi tsam ajikinta ta soma shafa jikinsa ya ajiye kwayar tsafinsa ya farmata, yayinda kotu ta cika makil da mutane ta bangaren iyayen yaron daya mutu da bangaren zulaihat suhaima da wasu daga cikin dangin mahaifinsu da mahaifiyarsu ,bayan dogon bayani majistr ta tambaye zulaihat akan furucin datayi cikin kuka ta amsa tayi sai dai ba ita ta kashe yaron ba take majistry tace wuce daita gidan yari a tsareta har zuwa sanda za'a gama bincike suhaima na kallo aka tasa keyar zulaihat cikin blackmariya aka wuce daita cike da tsantsar nadama .....

Jiki a sanyaye suhaima ta dawo gida kamar an mata mutuwa ta Kira number hajiya rahma amman shiru,haka tayita neman number har ranar data cika sati daya a gidan layinta bai shiga ba ta tattara ta wuce gida inda ta hadu da wani sabon tashin hankalin mah'ruf tagani zaune a parlou'nta mutuwar tsaye tayi hankalinta yayi mugu mugun tashi saboda bai ce mata komai ba ya fice daga ɓangaren ta biyosa tana bashi hakuri da kawo masa uzurinta yayimata banza ya cigaba da tafiya bata sake ganinsa ba sai washegari gabad'aya mah'ruf ya sauya mata sauyin da ta rasa gano dalilinsa yanzu ma zaune take a d'akinsa shiru ya ratsa dakin yadda batayi magana ba haka shima bai yi mata magana ba har ya gama shirya jikinsa tunanin ne kala daban daban ke yawo acikin zuciyarta ,har ga Allah tana jin tsoron wannan shirun nasa ba dan komai ba sai dan bata san abinda zai haifar ba ,tasan shi tasan halinsa tasan daya san halin da take ciki makircinta zai fito mata a mutum dinsa sak sannan ya had'ata da horo mai tsanani ....

Tana zaune ya hawo saman gado yayi kwanciyarsa ta matso a hankali ta kai hannuta jikinsa shiru yayi na second biyu sannan ya ware idanunshi akanta haɗe da cire hannunta ,ya koma ya zauna ya jingina bayansa da abun gado tare da d'aura kafarshi daya kan ɗaya yana cigaba da kallonta a hankali sautin Muryarta ta soma fitowa "habibi idan wani laifin nayi maka yasa ka canza min kayiwa Allah da Manzonsa kayi hakuri wallahi duk abinda zan maka mai ɗauke da laifi bisa kuskuren ne,muddin ina sane bazan taɓa yi abinda nasan zan bata maka rai ba ,yau kimanin wata guda kenan da ka kaurace min ka daina gayatata zuwa shifidarka na tambayeka kaki faɗa min laifina ,ka taimaka ka faɗa min abinda na maka saboda kiyayewa ?

Murmushi mah'ruf yayi irin wanda ke bala'in yi masa kyau a duk sanda yayi ,sannan yana yin irin wannan murmushin ne a lokacin da yake daf da muzgunawa mutun "suhaima yakamata zuwa wannan lokacin kinsan abinda kika aikata min .......

Shiru tayi na yan mintina tana kallonsa "tabbas nasan nayi maka laifi amman bansan wani iri laifi na aikata maka ba ina bukatar sani hannunsa ya kai qirjinsa yana shafawa a hankali a hankali "wel karki damu zuwa yanzu ya kamata kinsan laifinki ya sauko daga kan gado ya fita daga dakin ko cikakken minti talatin bai ba taji motsin shigowar mutane ta mike jikinta na rawa ta dawo parlou'n ummita aunty hajiya umma hajiya mama sai kanin mahaifinta daya shigo daga baya tare dasu Abba abun yayi matukar bata mamaki ta shiga kallonsu gabanta na faduwa gaisuwar munafurcin datasa basu ko ita bata samu damar yi ba tana kallon mah'ruf ya sake fita ya dawo hannunsa rike da usb ya karasa jikin ya jona "suhaima tunda ya fita ya shigo qirjinta ke wani irin bugawa har sanda ya gama haɗa komai hotunan ita da yanuwanta suka bayyana suna dikar rawa da bushewa da mahaukaciyar dariya ..
yace "a sha kallo lafiya suhaima .. ..

ya koma jingina bayansa da bangon dakin tare rungume hannuwansa duka a saman qirjinsa a matukar gigice ta waigo tana kallonsa "ki cigaba da kallon film nasan zai miki dadi sosai kamar yadda nima yayi min dadi very interested film ko ba haka ba ?yayi magana yana dage mata girarsa daya tayi saurin girgiza masa kai jikinta na wani irin rawa tamkar wacce aka jona jikinta da shocking gabad'aya mutanen dake zaune agurin babu wanda jikinsa bai mutu ba tsabar firgita ..

"Na dade ina tunanin abubuwan dake faruwa a cikin gidan nan ,na rasa wanda zai bani amsa tunanina da tambayoyina akan abinda ke faruwa kwasam kwakwalwata ta yanke wannan hukuncin na haɗa Camera a gidan nan wanda shine silar bayyana komai na fahimci daga inda matsalar take daga baya kunnuwana suka ji komai daga bakinki ke da yan'uwanki.

"Wannan shine babban sheida agabanki gashin kina kallon komai a zahirinsa har aikin da wacan muguwar yayartaki tasa hafiz almustapha , suhaima kin bani mamaki nayi bakinciki aurenki da rayuwar da muka gudanar tare, bansan irin matar da nake aure ba kenan sai da komai ya gama cakudewa , nasan makira mai kafurar zuciya nake aure batare dana sani ba "meye laifina da na cancanci haka daga gareki suhaima ?"Idan ummita ta kasance kishiya gareki ni fa me nayi miki me ya'yana suka miki da kika dinga binsu daya bayan daya kina kashewa ?

"Kin sa nayi zargi matata ta sunah batare da ta aikata abinda nake tunani ba ,kinsa na bata wa iyayena rai duk a sanadin zargin ummita da zuciyata tayitayi ,kin munafurci kin nuna min kina qaunata kina tare dani kina tausayawa ummita halin da take ciki ba kya son na rabu daita a she duk yaudara ce da makirci .... ?

" Wulakacinki da yaudararki da cin amanarki bai tsaya iya haka ba har sai da kika dauko wani kato kika kawo shi har cikin gidana kika masa kyawawan tarba akan shimfid'ar aurenmu suhaima ? zakiyi mamakin yadda nasani ko ? "karki yi mamaki Allah ya ga cewar da zuciya daya nake tare dake shiyasa asirin mus'ab ya tono cikin sauki yayi tuban wahala saboda ya aikata irin abinda ya aikata dake asirinsa ya tono a gurin bincike ya lissafo har dake "na ɗauka taimakona kike ashe cutar dani kike, me yasa kika aureni tunda kinsa zuciyarki ba tsarkakkiya bace banda cuta da makirci da yaudara babu komai a cikinta? da yake dakikiyar zuciyarki da kwakwaluwar data iya makirci da yaudara gareki shine kika tsaya kina tambayar laifinki gareni ..

"A yau zamana dake ya kare a matsayinmu na ma'aurta suhaima rabuwarmu shi zai sa ki koyi darasin da zuciyarki bata taɓa kawo miki ba,daman na barki ne har sai zuwa wani lokaci saboda ina son hada wasu mahimman bayani sai gashi kin iske subai'a har gida kin zayyano mata mugun kulkinki akan mama ya faɗa kan hajiya inna dan haka babu ni bake na sa "me mama tayi miki matar da ta daukeki tamkar diyar cikinta matar duk abinda aka fada akanki bata yarda har kullum burinta ta kyautata miki saboda kin rasa tunaninki kin rasa masu fada miki gaskiya kika saka mata da wannan kinsa irin shirin da take yi akanki tun ban aureki ba take karfafa min gwiwa akanki

Rarrafowa tayi gabansa fuskarta Shabe Shabe da ruwan hawaye "kayiwa Allah habibi karka datse tsakaninmu wallahi sharrin sheidan ne da girman soyayyar da nake maka yasa na aikata haka ,hakika na yaudari kaina , mayaudariyar zuciyata ta cuceni gashi zata kai ni ta baro , ka yafe min ka zabi horo mai tsanani ka min amman ban da datse auren dake tsakaninmu wallahi ina sonka ta kare maganar tana kuka ...

"Bazan yafe miki abinda kika min batu na cigaba da zaman aure dake gaskiya babu, zamanmu ya kare tsakaninmu, dan bazan sake zama aure dake baYa bar inda take durkushe a gabansa zuwa tsakiyar dakin ya juya mata baya yana mai jin bakinciki mara misaltuwa da sauri ta share hawayenta ta rarrafo zuwa garesa zata rike masa kafa ya juyo a fusace ya shureta yana watsa mata wani mugun kallo "na sakeki bana bukatar sake ganin fuskarki "dan Allah ka daina fadar waɗan maganganu masu kama da almara ,bakinka ya daina furta wannan kalmar habibi zuciyata zata buga tsura mata ido yayi yana kallonta gabad'aya ta gigice ta rud'e ta fita haiyacinta "menene kike wa hawaye bayan kinsan wannan ranar tana zuwa duk wanda yake aikata sharri irin wanda kuke yi keda yan'uwanki wannan ranar na zuwa ko ba dade ko ba jima ?
"Na sani habibi nasan ban kyauta maka ba na cutar da kai da ummita amman kayi hakuri karka sakeni "kinsan Allah idan na sake zama dake uwata da ubana zina sukayi suka haifeni ai sani baki yi ba tun wata daya daya gabata takardar sakinki ke ajiye ya karasa ya tura hannu cikin aljihunsa ya ciro farar envelope "kinganshi wannan shine sakamakonki ya je fama "sai abi wani sarkin kuma yau kawai na baki ki tattara duk abinda kika san naki ki bar min gidana jikinta na rawa ta karasa gurin mama dan a tunaninta itace zata tausaya mata "ma........
Saukar mari taji ta d'ago a gigice tana kallonta domin tabbatar da itace ta mareta ko kuwa wata ce daban, saukar wani marin yasa ta tabbatar da itace, ta durkushe a kasa tana cigaba da kallonta "suhaima me ummita tayi miki a rayuwarki da kika tsaneta irin haka har kika dinga rabata da ya'yanta ? babu abinda tayi miki me yasa kike son dauketa d'aga duniya ?
mah'ruf ya furzar da iska yana watsa mata wani kallo mama ta riko hannunta ta soma janta ta nufi kofar waje daita ",kiyi hakuri ki yafe min mama na tuba bazan sake ba dan Allah kiyi hakuri karki juya min baya mama ta tsaya tana dubanta hankalinta a tashe ",oh ƙina son na yafe miki ? Ina yawon yafiya ga duk abinda za'a min na yafe miki tun ba yau ba saboda duk abinda ake faɗa akanki babu wanda na yarda a kullum ina addu'a ya zamo karya ne gareki tare da yi miki addu'a batare da saninki ba, wannan ba adalci ba ne na miki a matsayinki na kishiyar diyar cikina ? "Kin sha hada makirci dan ki kuntatawa ummita sai na yafe miki idan ta faɗa min nace karya take miki nasan halinki bazai aikata ba komai kikewa ummita bana nunawa ko nuna damuwa saboda ban rikeki a matsayin kishiyar diyata ba fitar cikina na daukeki ina sonki suhaima ina sonki kamar diyar cikina me yasa kika yi haka ? Sai dai ina tabbatar miki a wannan karon babu abinda zan iya miki bayan duk abubuwan da kikayi ina miki addu'a da fatan shiriya gareki da ikon Allah kuma sai kin bar rayuwar mah'ruf da ummita ta sake kai hannuta ta rike "mama mama dan Allah ki yi haquri, ki sake bani dama ta dinga tafiya daita "dan Allah mama ki tsaya ki saurareni Abba umma dady aunty dan Allah ku sa baki "duk wanda zai sa baki bazan sauraresa ba bare cikinsu babu mai farinciki da kasancewarki cikin rayuwar mah'ruf sun fi kowa son tafiyarki "dan Allah mama nasan nayi kuskuren dan Allah karki rabani da gidan mah'ruf ku yafe min abinda nayi wallahi nasan abinda nayi bai dace ba nasan nayi kuskuren Amman ku yafe min karki koreni dan Allah, dan Allah mah'ruf kayi hakuri "babu wannan a tsakaninmu da kanshi ya fixgota daga hannu mama ya jata har gurin motar mahaifinta ya bude gidan baya ya tura ciki ya tsareta da idanunshi "idan kikayi ganganci fito wa wallahi da kakafunki da gangar jikinki da komai naki sai ya dawo bashi da amfani ni ne me aure kuma nace bana yi ya maida murfin kofar ya rufe yana huci ya juyo a daidai lokacin da mahaifinta ya fito yana daga kafafuna da kyar yana goge hawaye ya shiga motar ya tayar mah'ruf na tsaye suka bar gidan ..

Har suka karasa gida kuka suhaima take ta shiga dakin hajiyarsu tana rusa kuka ta faɗa jikinta a gigice ta rungumeta tana tambayarta abinda ya faru "ya sake ni ya sakeni mah'ruf ya karashe sauran igiyoyin aurensa dake kaina "wani irin qara mahaifiyarsu ta saki mai razanarwa tashiga zuba sambatu tana duban tayis ,kanin mahaifinta ya shigo dakin yana dubansu  "Kinga irinta ko suhaima duk abinda Allah bai baka ba babu wanda ya isa ya baka , kin haɗu da yan'uwanki kin kuntatawa yar mutane yau wa gari ya waya ? "Allah ya sani  danuwana yayi iyakar kokarinsa akanku amman kunki kun biyewa mahaifiyarku zulaihat tana gidan prison ke mijinki ya sakeki ,ita rahma har yanzu ba'a san inda taje ba ga iyayenku a kwance , ya karasa maganar yana zubar da hawaye ya juya zuwa dakin mahaifinsu , suhaima kuka kawai take tana kiran na cuci kaina haka mahaifiyarta na zuba sambatu da jan gashin kanta tamkar mahaukaciya,
Kwana sukayi suna kuka yayinda jikin mahaifinta yayi tsanani saboda jimami da tashin hankali ana kiran sallahar asuba mota ta soma sauke kayan suhaima bisa umarnin mah'ruf babu abinda ya bari wanda dangaceta aikuwa kukanta ya tsananta babu wanda take son gani alokacin kamar hajiya rahma ..
Washegari da misalin karfe goma na safiyar juma'a mahaifinta
yace ga garinku aiko hankalin suhaima ya sake tashi ta dinga kuka tana burgima saboda babu mataimaki , Alhaji Umar ta soma  kira da yan'uwansa  da bashir kafin kace me  Alh Umar ya kira number's din abokansa sannan ya kira number hajiya rahma da kusan sati kenan yana kira bai shiga, yan'uwa mahaifibsu ne suka tsaya aka shirya mahaifin su zuwa gidansa na gaskiya wajen zaman makoki ma surutu ake akan halinsu da mahaifiyarsu "duniya kenan bawan Allah babu yadda bai so ya kara aure ta hanashi gashi ya bar mata duniya gabad'aya  sai da aka kulle mahaifinyarsu a daki saboda haukan data dinga yi .

acikin kwana biyu suhaima ta shiga tashin hankali bayan kwana uku ta shirya zuwa isheri sai dai wayam ta nemi gidan boka kasa ko sama ta rasa babu shi babu alamunsa sai fill da ciyayi,dinga zagaye gurin tana magana "nan ne mana nan muka zo ga titi can muna sauka sai kwanar, haka tayi ta yawo a isheri sai kusan yammata ta dawo a jikace ta kasa bacci ta kasa wanka saboda rashin kwanciyar hankalin , wasa wasa sai da hajiya rahma ta share wata daya da sati daya bata dawo gida ba, wanda zuwa lokacin rayuwa tayiwa suhaima tsanani jikin hajiyarsu yaki dadi ban da hadiyar zuciya babu abinda take can kuwa gurin boka yana nan kamar yadda yake bokan ne ya rufe idanun suhaima dama wanda zai zo daga bangaren hajiya rahma, juyata yake son ransa ya maidaita kamar matarsa, ya mantar daita komai mijinta da ya'yanta da y'an'uwanta kwata kwata bata tunanin gidan babu kowa agabanta sai boka ..

Hankalin ummita ya kwanta sosai sai dai yanayin jikinta yaki dawowa normal tana dai daurewa ne kawai acikin satin rashin lafiya ya sata gaba sosai bata iya hassalawa kanta komai ko parloun kasa bata iya saukowa balle ace ta shiga kitchen mama ce duk ke yin komai na gidan ,bata dade ba ta fahimci ciki gareta tayi murna sosai mahruf bai lura ba sai a wani dare daya makale lallai sai ya kwana agurinta , ta kwana tana amai ta galabaita sosai aiko gari na wayewa ya d'auketa sai asibiti doctor husain ya karbeta yana bata kulawa batare da bata lokaci ba ya gano ciki gareta na wata uku da kwanaki ,tun da mah'ruf yaji batun ciki da kwanankinsa yayi shiru yana duban likita kafin daga baya yace " doctor nifa duka wata biyu nake tunanin ciki bayan zubewar wannan ciki yanzu kuma naji kace ciki wata uku da wani abu ,ka dai duba da kyau ko dai wata biyu ne ?
"Gaskiya idan abinda result ya nuna mana ne wata uku kenan da kwanaki ,ya juyo yana kallon ummita wacce tayi tsuru tsuru tana kallonsa zuciyarta na dokawa ,a hankali yace tashi muje gida ta girgiza masa kai tana duban doctor husain.

ta soma magana qirjinta na mahaukacin bugawa "doctor husain tun bayan da nayi misscarage ban sake yin wani period ba har zuwa wannan lokacin kuma ni tunda nake ban taɓa wata muamula da wani mutun ba bayan mijina to ko dai "kodai me tashi muje   gida  ? Ta girgiza masa kai
Dakin ya dauki shiru baka jin motsin komai sai na saukar
numfashinsu jikinta na rawa tace " doctor kayi shiru ..

mah'ruf ya riko tsintsiyar hannunta cikin zafin nama ta juyo a matukar tsorace haɗe da sanya kwayar idanunta take jikinta ya sake daukar rawa "Doctor dan girman Allah kayi masa bayani ,ina gudun samun matsala dashi banason abinda zai shafi aurena da mijina domin shi din duniyata ne ina matukar kaunarsa tana gama magana ta zamo ta durkusa a gaban mahruf "yayana kuma mijina ka kwantar da hankalinka wallahi wannan cikin naka bansa me Allah yake nufi da hakan ba bazan taɓa cin amanar aurenka dake kaina ba saboda ina sonka tana gama magana sai hawaye sharrrrrrr ya shiga gangarowa .

sautin muryarsa ne ya ratsa kunnuwanta " ki natsu wallahi babu komai a halin yanzu qauna mun kai matakin da ko wani irin yanayi muka tsinci kanmu ciki zamu sadaukarwa junanmu fariciki tare da boye sirrinmu babu abinda zai sake nisanta tsakaninmu, sannan babu abinda zai raba aurenmu har yanzu ina jin sonki acikin zuciyata, ni kaɗai nasan me nake ji akanki wasu zafafan hawaye ne suka shiga turereniyar gangaro mata tasa bayan hannunta ta share tana jin wani sanyi from know where ya lullu'be sansar jikinta , kallonsu doctor Husain yayi cike da tausayawa sannan ya buɗe baki ya soma magana a tsanake "mah'ruf ta kanka zan soma maganata tunda kaine gaba da ummita, wannan al'amari daya faru ba wani sabon abu bane ,alhamdullahi da Allah yasa zuciyarka bata kawo zargi atsakaninka da matarka ba, dan abinda ya faru daita ya sha faruwa sai dai idan bai faru akanka ba bazaka san da zamansa ba .

Yaja numfashi ya sauke yana dubansu sannan ya cigaba da magana " kwana a can ta kwanta akan ƙaramin gadon marasa lafiya yayi scan sannan yace " wannan cikin na jikin matarka ina ganin tagwaye ne daya ya fita ya bar daya , daman kuma babu yadda Allah baya alamarinsa ,ikon Allah yafi gaban komai Allah ya inganta muku wanna mah'ruf ya soma mikewa tsaye yana mikar da ummita "mun gode kwarai doctor jikin ummita babu kwari ta mike tare jin bugun zuciya da firgici tana jin tsoron suje gida ya birkice mata "ina tabbarwa kaina ko abinda ummita zata haifa ba nawa bane , na amsa kuma da zuciya daya bare babu wani shakka ko zargi acikin zuciyata akan cikin jikinta dan nasan halin matata bazata taɓa aikata wani abun asha ba , ya zagayo daita bayan kujerar da suka tashi ya matso daita gabansa ya daura habarsa akan kafad'arta suna fuskantar doctor husain "Ina da tabbas akan matata da kyakkywan zato akanta domin tana cikin siffan matan da Allah ya ambata sunansu acikin alquarni mai girma wani sanyayyen ajiyar zuciya ta sauke, tana hadiye wani miyaun daya tsaya mata a makoshi,juyowa tayi gabadaya ta shige jikinsa tana kukan farinciki , mah'ruf hannunwansa duka yasa ya rungumeta ajikinshi , shiru doctor yayi yana kallonsu rungume da juna,a hankali zuciyarta ke sake bud'ewa da sake kar'barsa a matsayin wani jigo gareta da rayuwarta gbdy ,wani irin sonshi ne ke d'awainiyya da gangar jikinta sosai ta narke ajikinshi tana fidda numfashi gabadaya ta rud'e bata ganin komai sai shi da soyayyarsa dake d'awainiyya daita ta manna kanta a qirjinsa tana sauke numfashi .

Zareta yayi kadan ajikinshi ya talla'bo fuskarta ya tsura mata idanunshi yana kallon kwayar idanunta da hawayen dake cigaba da tsiyoyawa daga cikin idanunta , cike da matsanamcin shaukinta ya shiga girgiza mata kai yana matso da fuskarshi ya soma lasar hawayenta da harshensa , Gabadaya shi kanshi ya manta da inda suke saboda kaunar dake fixgarshi ,zai iya yin komai akanta ,wasu sabin hawayen farinciki suka sake zubo mata , jikinsa na kyarma ya sake matso da fuskarshi daf da nata har suna jin hucin numfashin juna da bugun zuciyarsu, rungumota yayi sosai "Please qauna ki daina kuka nan haka ki tausaya min bazan iya jurar ganin hawayenki ba , kin taka matsayin da zan iya miki komai domin ina sonki so mai tsanani sannan na yarda dake dari bisa dari , a halin yanzu bani da burin daya wuce ganin babynmu a duniya cikin koshin lafiya wani irin bugawa zuciyarta yayi da matsanancin karfi saboda tuno yadda take rasa cikinta , take jikinta ya ɗauki rawa "ina jin tsoro kar na sake rasa shi....
Da sauri ya da'ura ɗan yatsansa akan lip's d'inta "shiiiiiiiiiii babu abinda zai samu wannan ciki da izinin Allah zan yi kokarin naga na karesa da dukkanin karfina, ni dai ki kwantar min da hankalinki ta yadda babynmu zai fito cikin koshin lafiya ,murmushin jin dadi doctor husain yayi "tabbas waɗan nan masoya sun burgeshi matuka kuma sun shiga ransa , tsaftacciyar soyayyarsu ta shiga ranshi sosai ta shige jikinsa tana shaƙar kamshin turarensa ..

Tsawon lokaci suka ɗauka suna manne da juna basu san sanda doctor husain ya fita
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On WANNAN CE QADDARARMU
avatar
amina-4

11 months ago

Reply

Interesting novel

avatar
amina-4

11 months ago

Reply

Interesting novel

Please Login or Register in order to submit comment