Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE



You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

06/12/2019 à 14:41 - Les messages envoyés dans cette discussion et les appels sont désormais protégés avec le chiffrement de bout en bout. Appuyez pour plus d'informations.
18/05/2020 à 13:43 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨
*BADAK'ALA*
👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨

*Labarin gaske*


*NA*

_SAMIRA HAROUNA_

*Litattafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._

*SADAUKARWA GA*

👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦


*Labarin nan ya faru a gaske, sai dai a wurare daban daban, amma na canza garuruwa da sunaye, domin tak'aitawa kar gidajen suyi yawa yasa zan had'a labarin a gida d'aya.*

*Nagode da gudummuwarku gareki*


_Bismillahir rahamanir rahim_

_1_


Kamar saukar aradu tsohuwar nan ta d'aga hannu ta gaure matashin saurayin dake gabanta da mari, cikin d'aga murya da b'acin rai ta nuna shi da yatsa tana fad'in "Wallahi ko zaka mutu ba zan tab'a bari ka auri karuwar nan ba, *Junaid* ko ubanka dana haifa bai isa nace ga yanda za ayi ba yace a'a bare kuma kai daya haifa, in zaka auri wacce na zab'a maka ka aura, in kuma ba haka ba to ka sani zaka mutu a matsayin wanda bai b'ata aure ba har abada."

A hankali ya d'ago daga sunkuyar da kan da yayi tare da d'auke hannunshi akan kumcinshi ya kalleta, kyakyawa ne sosai wanda ya had'a komai da komai, abun mamaki kuma shine wasu matasan guda biyu dake tsaye daga bayanshi wanda suke matuk'ar kama, sai dai kaman wad'ancen matasan tafi k'azanta matuk'a da alama ma 'yan biyu ne, cikin ladabi yace "Hajia kiyi hak'uri idan abinda zan fad'a zai b'ata miki rai, amma a gaskiya ina son *Maryama* kuma ita nake so na aura, Hajia munyi iya k'ok'arin mu wajen yi miki biyayya, mun bar abinda muke so saboda ke, na zama malamin makaranta ba dan raina na son haka ba, amma a gaskiya yanzu abune da zaiyi wahala, dan magana ce ta aure, rayuwa ce da ake saka rai idan har anyi to sai mutuwa ce zata raba, kenan taya zamu yarda mu auri wanda ranmu baya so? A gaskiya ni dai ba zan iya ba, kuma iyayena sun amince na aure ta haka ma Alhaji ya amince."

Wuyan rigarshi ta finciko ta tilasta mishi kallon fuskarta tace "Junaid ni kake kallo kake fad'awa wannan maganar, to ka sani ni ce shugabar gidan nan sai abinda nake so akeyi, daga kai har uban naka zan iya tsine muku albarka idan kuka ce wannan yarinyar zaku shigo min da ita a cikin gidan."

Sakin rigarshi tayi har saida yayi baya amma ya tsaya cak yana kallonta, gyara tsayuwarshi yayi yace "Shikenan, tunda haka kika ce ni zan bar gidan nan naje can na auri wacce raina yake so, kuma wallahi..."

Bai k'arasa ba mahaifiyarshi *Zeinabu* ta d'auke shi da wani sabon marin tana fad'in "Kayi mana shiru anan."

Sake dafe kunci yayi yana kallonta da mamaki, ita ma kallonshi tayi duk da tana goyon bayan wacce yake so ya aura, amma dole tayi haka saboda k'arshe abin kanta zai koma, da yatsa ta nuna mishi k'ofar fita tace "B'ace min da gani, kuma kar na sake jin motsinka a gidan nan idan bani na neme ka ba."

Ya juya zai fita wata kyakyawar tsohuwa wacce fuskarta ke d'auke da tsaga wacce ake caccakawa sai tayi bak'i ga kumatu da kuma gefen bakinta, cike da dattako tace "Kai Junaid, zo nan, ba kamata yayi ya fita ba, mafita ya kamata a samu a game da matsalarshi, ba wai mu barshi haka ba."

Mahaifin Junaid d'in wanda suma na gani su biyu duk kamarsu d'aya, kuma abin sha'awar ba zaka ce sun haifi kamar wannan zargadan zargadan matasan ba saboda yanda suke tsaye da kyau zaune da kyau, saidai mahaifin Junaid d'in jikinshi yafi murd'ewa kasancewarshi *soja* a cikin sojojin ma *colonel* ne, kamar baya son magana saboda yanda yayi maganar yace "Ku barshi ya tafi kawai tunda saiya mana rashin kunya ne zamu yarda da k'udirinshi." *colonel Hussein Suley Hassan Gaga* kenan wanda ko wajen aiki akafi kiranshi da Hassan Gaga.

Mai kama dashi ne sak mai sunan *Hassan* wanda shine babba yace "A'a d'an uwa ba ayi haka ba, ya kamata a tattauna a tsanake dan duk yanzu kowa zuciyarshi tafasa take."

A harzuk'e kyakyawar tsohuwar nan wacce kallo d'aya zaka mata kasan asalin buzuwa ce tace "Babu wani tattaunawa da za ayi game da maganar nan, na gama magana dan haka babu buk'atar sake taso da ita, ba zai tab'a auro karuwa ya kawomin a cikin zuri'a ba."

Tana fad'in haka ta wuce zuwa inda zai sadata da nata d'akin baccin kasancewarsu a babban falon gidan, sai lokacin kad'ai wani santalelen tsoho dake zaune yana kallon kowa ya bita da kallo da wani murmushi a fuskarshi, uwayen ma duk barin wurin sukayi rai a jagule, tsohon kad'ai ya rage sai matasan nan guda hud'u, Junaid ne ya juya zai fita tsohon yace "Junaid, kaje ka ci gaba da k'ok'arin samun yardar Maryama, zaka aureta, wannan alk'awari na ne gareka, kaji ko?"

Da murmushi a fuskarshi yace "Nagode Alhaji, Allah ya saka da alkairi."

Juyawa yayi ya kalli yan uwanshi, cikin farin ciki biyu suka rumgume shi sai d'aya da yace "Ko ba komai zakayi bacci cikin farin ciki, nima Allah yasa ta amince da zab'i na."

Murmushi sukayi sosai sai Junaid d'aya rad'a mishi a kunne "Ai kai ahalinta ce kake so, zata amince da gudu ma, idan bata amince ba ka mata bore irin nawa."

Dariya suka sake sakawa sai d'aya daga ciki daya juya ya kalli wanda ke zaune yana latsa wayarshi alamar shi duk matsalolin nan ko a kwalar rigarshi, girgiza kai mai matuk'ar kama da shi yayi yace "Yanzu yaya *Ammar* kai ko ka tayashi farin ciki ma."

Tabbas saurayin da gani kasan akwai shan k'amshi da d'acin rai da kuma miskilanci, dan ido kawai ya zuba mishi ya kalleshi take kuma ya d'auke ya ci gaba da abinda yake, d'aya saurayin ne yace "Kunga barshi da halinshi, watak'ila allurar sojojin ce ta motsa."

Yana fad'a sai kawai suka kwashe da dariya harda Alhaji dake shirin tashi, wannan kuma abun shi ya tunzura Ammar ya ji kamar ya rufe su da duka, tunda iskanci ne suke mishi, sunfi kowa sanin baya da buri a duniya daya wuce ya ganshi a matsayin soja mai kare k'asar shi, amma tsohuwar can ta bakinshi ta hanashi cika burinshi, ta tilasta mishi zama likita abinda sam baya birgeshi ma a tsarinshi, amma sun samu abin tsokanarshi da shi dan sunga yana mutuwar son zama sojan har yanzu, hararan daya musu da jajayen idonshi yasa su shiru sai *Amar* wanda shine tagwaicin haihuwarshi yace "Kunga mu bar gidan nan dan ran sojawa ya fara b'acewa, yanzu ne allurar zata motsa a huce kanmu."

Nan ma wata dariyar suka saka wacce tasa shi tashi da hanzari ya bi bayansu, ai da gudu dukansu suka fita kamar yara k'anana, rige-rigen fita sukeyi a bakin k'ofa hakan yasa yayi nasarar rik'o rigar *Jibril* wanda yake jika ne ga k'anwar kakansu *Husseina*, duk da kasancewar Jibril namiji saida idonshi sukayi ja kamar zaiyi kuka saboda wata matsa daya mishi a ciki ya had'a da fatar jikinshi, k'ara ya saki ya kalli su Amar da har sun kai k'ofar gida cikin muryar wahala yace "Kai dan ubanku ku zo ku taimaka min, ba tare mukayi tsokanar ba."

Dariya Amar harda yin zaune k'ofar gidan yana rik'e ciki saboda ya ga k'eta, Ammar kam sosai yake sake matse mishi fata yana fad'in "Gobe ka sake min iskanci?"

"A'a wallahi, daga yau gaisuwa ce tsakaninmu da kai, kayi hak'uri dan Allah yaya Ammar."

Jinjina kai Ammar yayi yace "Oho, kenan yanzu ka tuna da nine yayanka ko? D'an iska kawai gobe ka k'ara." Ya fad'a yana tura shi, Junaid na ganin haka ya haura ta kan Amar dake zaune yana dariya ya fita a gidan, dukansu baya suka rufa mishi shi kuma Ammar ya juyo ya dawo ciki.

➡️➡️➡️➡️➡️➡️➡️

Alhaji na tashi daga nan d'akin baccin tsohuwar nan ya shiga, zaune ya sameta cikin tsananin damuwa, sam bata san ya shigo ba har saida yace " Duk wannan damuwar akan maganar auren ce?"

Da sauri ta kalleshi, tana ganinshi ta ja k'aramin tsaki ta sake kawar da kanta, shi kam ko a jikinshi dan ya ga fiye da haka ya kuma yi hak'urin fiye da haka, dan haka ya d'ora da " *Zeeya'atu*, tsawon shekaru hamsin da bakwai da aurenmu, na saka miki ido kina juya yaran nan yanda kike so, dayawa daga cikinsu suna rayuwa babu farin ciki saboda kin tauyesu ta wani fannin, hatta aikin da sukeyi duk ke ce kika zab'a musu shi haka ma matan da suka zama uwayen yayansu, akwai wanda kina kallonshi zaki san baya farin ciki da zab'in naki , amma saboda biyayya sun hak'ura suna yi, to ya kamata ki sani zmanin yayan da kika haifa da zamanin yayan da suka haifa ma'ana jikokinki ba d'aya bane, yanzu ba'a tirsasa yaro yayi abinda baya so, nasan kin fara fahimtar hakan daga yanda Junaid ya miki magana yanzun nan, da wannan nake shawartarki da ki janye wannan kud'irin na cewa ba zai auri yarinyar nan ba, dan na mishi alk'awarin zai aureta kuma babu abinda zai hana hakan."

Har ya juya zai fita ta mik'e tace "Wallahi baka isa ba, indai ina numfashi a doron duniyar nan Junaid ba zai tab'a auren yarinyar dake yawon ta zubar ba, ba dai a dangina ba, sannan da kake maganar babu mai farin ciki a ciki amma ai suna zaune lafiya."

Juyowa yayi yace "Babu wanda yasan abinda ke b'oye cikin duhu, ki zuba ido zakiga auren Junaid da Maryama, tunda Allah bai haramta mishi ba mu ba zamu hana mishi ba, indai har zatayi tuban gaske to wannan ba matsala bane."

Cike da rainin wayo tace "Idan ya aureta ya shigo da ita cikin gidan nan harta haifa mishi 'ya'ya, ya'yan wa zamu kirasu? Kana so ace ai uwarsu tsohuwar karuwa ce suma kamar yanda Jibril ya kasance jika ga tsohuwar karuwa?"

Da k'arfi ya juyo ya k'ura mata ido, zuciyarshi ce ke bugawa da k'arfi yana ji kamar ya mata bugun mutuwa, saidai kuma abinda baiyi da k'uruciya ba shiyasa ba zai iya yi yanzu ba, haka ma baya so yayi magana ta hanyar bankad'o sirrin da yake ta rik'o a ranshi tsawon wannan shekarun, murmushi ya mata yace "Hum! Tabbas ba k'arya kika fad'a ba, ki sani nata karuwancin ne ya fito fili, na wasu kuma bai fito ba watak'ila talala ubangiji ya musu su gama gurza rashin mutumcinsu."

Yana fad'a ya sa kai ya fita dan fad'an su ba k'arewa yake ba, shiru tayi tare da tunanin me yake nufi da abinda ya fad'a, ta jima a haka tana wannan tunanin kafin ta d'auki gabjejiyar wayarta ta dannawa Amar kira, dan daga kallon kayan dake jikinta da yanayin shigarta da kwalliyar fuskarta zaka san tsohuwar wayayya ce ta gidan gaba, yana d'auka cikin sanyin murya tace "Jikalle kana ina? Ka fita?"

Cikin gatsali yace "Me kike so kuma yanzu? Ni bana gida."

Murmushi tayi har saida yaji sautinsa tace "Jikalle kuma guduna kake yanzu? Me ya sa kake haka?"

Cike da k'aguwa yace "Kinga Hajia, ni na fad'a miki bana gida, sai anjima."

Kashe wayar yayi ita kuma ta aje gefe tana kallon wayar tace "Allah yasa ba wajen wata shed'aniya kaje ba, amma idan ma da wani abu zan gano koma menene."

➡️➡️➡️➡️➡️➡️➡️

Jibril ma yana fita bai jima ba ya dawo gida, fitowa yayi daga motarshi mai shegen kyau da tsada, cikin falon ya tunkara ya bi ta inda zai sadashi da d'akin baccin kakarshi, saman bene ya kalla inda hayaniyar yara ke tashi sunata wasa da guje guje, yana kusa da kaiwa ya tsaya cak saboda tuna wani abu daya riga ya zamar masa jiki, a hankali ya rintse idonshi yana kallon fuskar a hoton k'wak'walwarshi tare da tuna wasu maganganu da suke gigita tunaninshi, duk da idonshi rufe suke amma saida hawaye suke zubo mishi saboda tuna wasu maganganu na k'arshe da macen take cewa " *Idan fa ciki ya shiga jikina sakamakon hakan? Ya kake so nayi? Wai kai baka da imani ne?*"

Da sauri ya bud'a ido ya goge hawayenshi ya d'aga kai ya kalli sama yace "Allah ka kareta a duk inda take, Allah kasa bata samu ciki ba a dalilin wauta da mahaukaciyar sha'awata ta k'uruciya."

K'asa yayi da kanshi tare da fad'i a zuciyarshi "Ameen." Cikin sanyin jiki ya k'arasa k'ofar d'akin yayi sallama, amsa sallamar akayi daga cikin d'akin kuma harda muryar mahaifiyarshi, shiga yayi ya samu wuri ya zauna kusa da kakarshi yana fad'in "Mama sanunku, hira kuke ke da yar tsohuwa?"

Dukanshi Husseina tayi tace "Ubanka ne tsohon, ni matsa can ka bani wuri."

K'ara lafewa yayi a jikinta yace "Ina zan matsa ni da na zo miki da muhimmiyar magana."

Mahaifiyarshi mai sunan *Soueba* ce tace "A k'alla ka d'auki sama da wata d'aya kana fad'a min zamuyi magana amma ka kasa nutsuwa ka fad'a min."

Sosa kanshi yayi yace "Mama yau dai zan fad'a muku tunda na samu k'arfin gwiwa daga abinda Junaid yayi yau."

Zaro ido tayi tace "Kai duba ka kiyaye ni wallahi, kai ma rashin kunyar zakawa mutane? To babu ruwa na ni dai, Mama ku zama shaidata."

Murmushi Husseina tayi tace "To ki barshi ya fad'a mana muji me yake tafe da shi, fad'i ina jinka."

Kallonsu yayi dukansu yana murmushi kafin yace "Ni fa dama ina so na fad'a muku ne nima na samu matar aure."

Dogon tsaki Soueba tayi tace "Aikin banza, dama wannan maganar ce zaka fad'a."

Husseina ma dariya tayi tace "Wannan wacece haka zata kwashe min wannan rigimamman mijin?"

Nan ma k'asa yayi da kai cikin kunya ya kalli kakarshi ya jawo kanta yace "Zo na fad'a miki a kunne."

Cikin kunne ya rad'a mata ita kuma ta bud'e baki tace "Iyeee, to kai ai duk gida ne, ah gaskiya nayi farin ciki da jin hakan."

Soueba ta kalla tace "Kinji fa ke, tuwo na mai na za ayi, dan yace dai *Amna* (kamar k'anwa take gareshi saboda mahaifinta da mahaifinshi yayan wa ne da k'anwa, ma'ana ita jikar alhaji ce daya haifi ubanta, shi kuma jikan Husseina ne wacce suke ciki d'aya da alhajin) yake so."

Tashi yayi ya fita wai shi kunya yake ji, ita kanta Soueba taji dad'i daya kasance Amna ce yake so ba 'yar uwar haihuwarta ba *Hamna*, duk da ciki d'aya suka rayu kuma uwa d'aya ta haifesu, amma Hamna idonta a tsaye suke ga wayewa da kuma k'awaye masu ido bud'e, mahaifiyarsu *Hadiza* bata gidan yanzu shiyasa ba wani saka musu ido ake ba sosai, har ma gwara Ammar da basa shiri da ita shine ke ci mata uwa idan tayi ba daidai ba, dan akwaita da shegen yawo kullum ita ce a tafiye gidan sabuwar k'awa, musamman da mahaifinsu ya siya musu moto, ga yawan biki na k'awaye da sauran shagulgula, dan kowane wata akwai wacce zatayi bikin k'arin shekara ko kuma murnar samun wata jarabawa a makaranta, Hamna bata saka kayan kati sai atamfa, amma wani d'inkin da zaka gani a jikinta na atamfa har gwara riga yar kantin, domin kuwa bata saka kaya inba ji tayi sun kama jikinta ba sosai, bata saka zane sai siket ko doguwar riga, haka Hamna bata fita wajen biki ko wani shagali ba tare da tayi k'arin gashi na kanti ba, ko tayi kitso ko ta saka shi hakanan, indai ba sallah take ba ko zata tafi islamiyya to baka ganinta da hijab duk inda take ko zataje, yanzu haka sun shiga ajin lycée shekara biyu data wuce, rawar kanta da rashin kunyarta yasa basa shiri ko kad'an da Ammar, tana da rashin kunya da fitsara da mayar da martani, shi kuma baya d'auka hakan yasa yake mata dukan mutuwa inya samu dama, dan in mahaifiyarsu ko mahaifinsu na nan basa bari su ke d'aure mata gindi, domin kuwa a hannunsu suka tashi tun suna k'anana sosai, hatta filin sada zumunta na ahalin *Gaga* da aka bud'e akafar sadarwa ta WhatsApp Ammar fita yayi saboda Hamna kawai, saboda ko hira ake muryarta ce tafi ta kowa fitowa, ga tsokanar mutane wanda ya girmeta da wanda ta girma, ga yawon turo hotuna na sallama daban na barka da rana daban na barka da dare daban, shiyasa ranshi ya b'ace ya fita saboda haushinta yake ji sosai, duk abubuwan nan da Hamna ta had'a sab'aninsu ne ke ga Amna, dan ita ko magana ma bata cika son yi ba, ba tada kwarmniya ko kad'an, dan inma Hamna ta tsokaneta sai dai tayi banza da ita, to fa da wannan ne yasa ko murmushin Ammar baka gani a gidan, ga haushin hana shi aikin da yake so, ga takaicin rashin kunyar da Hamna ke mishi in tana cikin mutane.

➡️➡️➡️➡️➡️➡️➡️

Junaid na barin nan wajen masoyiyarshi ya nufa inda yasan zai iya ganinta, tun daga wajen masallacin ustaz Sani d'an jatau yake baza ido amma shiru harya k'arasa bakin *pacific*, wani lungu ya shiga da motar dan yasan suna zama nan ita da k'awar ta, amma rashin sa'a bai samu ganin ko d'aya daga ciki ba, kiran wayar k'awarta yayi dan Maryama bata d'aukan kiranshi tana ganin kamar yana takura mata, a lokacin sun fito daga cikin d'akinsu tana rufewa da d'an kwad'o kiran ya shigo, k'awar mai sunan *Iklima* ce ta kalleta tace "Mutuminki ne fa Mari, me zan ce mishi idan na d'auka?"

Masha Allah, tabbas Maryama mai kyau ce ta gidan gaba, ga ta doguwa sosai da d'an kumari, gashi fatarta jawur da ita duk da tana shafa mai amma kasan ita ma akwai asalin farinta, akan luma-luma kumatunta kuma wasu tsage ne suka k'awata fuskar har guda bibbiyu, a take tace "Kawai ki fad'a masa bama tare dake, kar ma ki fad'a masa na fita."

Zata d'auka kiran ya tsinke kuma sai baiyi gaggawar maidowa ba, hanyar gidansu ya nufo wanda ke bayan masallacin daya bari a farko, yana sake kira kuma Iklima ta d'auka tace "Barka da dare."

"Barka Hajia Iklima, ya kike?" Cikin sakin fuska ta amsa da "Lafiya lau, ya yau?"

Saida ya sauke ajiyar zuciya yace "Yau da dama, ina mutuniyar take? Nasan kema kinsan bata d'aukar kirana."

Kallon Maryama tayi suna kan hanyar fitowa daga gida, kewayen wata mata Maryama ta lek'a ta same su zaune a d'an filin wurin suna kallon telbijin, matar ce ta kallesu tace "Mari fita zakiyi ne?"

"Eh maman *Husna*, ina *Huda* take ne?"

Da sauri wata yarinya da ba zata wuce shekaru biyar zuwa shida ba ta mik'e tsaye ta tunkarota, tana suwa ta rik'e hannunta tace "Mamma, yau ma fita zakiyi?"

Da murmushi ta shafa fuskarta tace "Fita zanyi Huda, amma yau ba zan jima ba zan dawo kinji."

Marairaicewa tayi ta k'ara matse hannunta tace "Mamma kullum haka kike cewa ba zaki jima ba, me ya sa ba zakiyi zamanki a gida ba?"

Ba annuri a fuskarta tace "Saboda saina fita muke samu mu ci abinci." Hannu tasa a jakarta ta fito da dala ashirin (ba zasu gaza naira ashirin ba), bata tayi tace "Gashi kije Aminu ki siyo madara kisha, idan kinji bacci kije lungunmu ki kwanta nayi shinfid'a."

Juyawa tayi zata fita taji ta rik'e hannunta, tana juyowa yarinyar tace "Mamma meyasa ke saida dare kike nemo mana abinci? Ki dinga zuwa da rana mana tunda baki komai a wannan lokacin."

A hankali ta zage hannunta daga na yarinyar ta sake juyawa, kamar saukar ruwan sama ta tsinci muryar Huda na cewa "Mamma kenan da gaske ke 'yar iska ce?"

Tsayawa tayi amma bata iya juyowa ba saboda hawayen da take, Iklima na ganin haka ta fice ta barta, da sauri ta taka ta barta nan ta fita, amma saboda wayo da kuma k'uruciya sai yarinyar ta fito da gudu har k'ofar gida tana kuka cikin d'aga murya tace "Ashe dama ban da uba, ni shegiya ce, to ni dai bana son neman abincin naki hakanan, daga yau ba zan sake cin abincinki ba idan kin kawo, kije kawai karma ki..."

Marin da Maryama ta d'auke ta dashi yasa yarinyar fad'uwa k'asa, wani daga cikin masu zama a k'ofar gidan ne ya kama Huda ya d'auke ta yana rarrashi.

Iklima dake amsa wayar Junaid shi kuma a daidai lokacin ya k'araso k'ofar gidan, cikin rashin sani tace "Mari ai tun rana rabona da ita dana barota gida, izuwa yanzu kuma nasan ta yada zango a wani wurin."

Daga inda yake ya hango fitowarta sai Maryama dake bayanta, daga cikin wayar yayi murmushi yace "...


*Allah ka mana kyakyawan k'arshe.*👏
18/05/2020 à 13:46 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨
*BADAK'ALA*
👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨

*Labarin Gaske*

*NA*

_SAMIRA HAROUNA_

*Litattafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._

*SADAUKARWA GA*

👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦


_Bismillahir rahamanir rahim_


Please Login or Register in order to submit comment